ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, June 14, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Adawar Siyasa A Jihar Sakkwato Da Sauran Lamurra

by Leadership Hausa
2 years ago

Hakika lamarin jagorancin jama’a a lokacin mulkin dimokuradiyya yana tafiya ne da adawa. Sai dai kuma idan za a yi adawar, ya dace a yi mai ma’ana wadda hankali ke dauka, domin adawa a tafarkin ilimi ita ce gishirin siyasa.

Lallai an yi adawa a lokacin gwamnatin, Alhaji Attahiru Dalhatu Bafarawa ta APP/ANPP (1999-2003), inda a lokacin, su Hon. Abubakar Shehu Tambuwal da Hon. Arzika Tureta (marigayi) suke a sahun gaba wajen yin adawa a karkashin tutar jam’iyyar PDP (wadda ke rike da gwamnatin tsakiya). Sai dai a lokacin babu kafafen sadarwa na soshiyal midiya irin yanzu. Hasali ma kila ko da akwai su, ba za a yi adawa ta wuce-wuri da cin mutuncin juna irin ta yanzu.

  • Ƙaramin Ministan Tsaro Da Manyan Shugabannin Soji Sun Isa Sokoto Domin Fatattakar ‘Yan Bindiga
  • Ambaliyar Ruwa Ta Lalata Gidaje 14,940 A Sokoto

Abin da aka al’adanta ne cewa wanda ake yi ma adawa idan ya tsima a fagen siyasa, wani sa’ilin ya kan iya janye abokan adawarsa su dawo bangarensa. Hakan ya faru a lokacin gwamnatin Bafarawa, inda ya yi nasarar janye Alhaji Abubakar Shehu Tambuwal ya dawo jam’iyyarsa. Hakan ma ta faru a lokacin Gwamna Aliyu Magatakarda Wamakko, inda ya janye Usman Sulaiman (Dan-Madamin Isa) daga wancan bangaren na Bafarawa zuwa nasa. Ko a haka da ake yanzu, wa ya san gobe ban da Allah (SWA)? Hausawa kan ce Sarki goma zamani goma.

ADVERTISEMENT

Abin da wani shugaba kan iya jurewa na adawa, wani ba zai dauka ba. Kuma inda wani ya yi rawa aka yi mai kari, wani idan ya yi, kashi zai sha. A bayyane take cewa a nan jiharmu ta Sakkwato, ana wuce gona da iri wajen amfani da soshiyal midiya wajen yin adawa wadda take da sigar cin zarafi da shiga rigar mutuncin juna har da na iyali. Kuma fa an lura da cewa kowane bangare ya sami dama, yi yake, amma ga abin da ya bayyana a halin yanzu, dayan bangaren na masu adawa ya fi zakewa.

An tabbatar da cewa a tarihin siyasar Sakkwato, ba a yi gwamna mai juriyar sukar adawa ba kamar Barista Aminu Waziri Tambuwal, wanda ya sauka jiya-jiya. Me ya sa a Sakkwato ba a koyi da salon adawar siyasa ta makwabtan jihohinmu na yankin kudu? A tasu salon adawar siyasa, iya sarrafa harshen Turanci da tajwidinsa ko akasin haka ba su ne abin suka ba ga shugaba, sai dai salon jagoranci da wanzar da ayyukka da ke da tasiri ga jama’a, ko bin diddigin ajandar da dan takara ya bayyana a lokacin neman kuri’un jama’a, da sauransu.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

A wani bangaren kuma, za a iya cewa, sai bango ya tsage, kadangare ke samun kafar shiga. Gwamnatinmu ta Sakkwato na bukatar kimtsa gidanta musamman a tawagar kafar sadarwa (media team), sabanin gwamnatocin da suka gabata na Bafarawa da Wamakko da Tambuwal inda kowace daga cikinsu na da gwargwadon kwararrun masana masu aiki kafada da kafada a tawagar masu rubuta jawabi (speech writing team) da ababen da suka shafi fitar da bayanai (Press release) da aka tantance sosai don kauce wa tuntuben alkalami da sako mai harshen damo da sauransu.

Idan ko akwai ayarin kwararrun masanan, to kila ba a ba su cikakkiyar damar yin aiki tare ba don abin ya yi armashi domin kuwa hannu daya ba ya daukar jinka.

Idan kuma aka zo bangaren ganawa da uban tafiyar, watau gwamna, nan ma akwai bukatar gyara sosai. A inda aka fito, lokacin da gwamnatin nan na kan turbar adawa, ganawa da Tambuwal na daya daga cikin kalubalolin da ake sukarsa da su domin ko kwamishinoninsa ba su faye samun ganawa da shi ba a lokacin da suke so. Bincike ya tabbatar da cewa duk kanwar ja ce, domin babu bambancin jiya da yau, inda hasali ma, ko hadiman Gwamna Dakta Ahmad Aliyu mai ci yanzu, shakku suke wajen yi wa mutum iso ko neman damar ganawa da shi.

Sai kuwa idan shi gwamnan ne ke da bukata da ganinka. Haka abin yake ga mukarraban gwamnatin, domin kuwa kalilan daga ‘yan majalisar jihar ke da juriyar sauraren jama’arsu a ofis ko a gida kamar yadda ya dace. Wannan ya saba wa a kalla gwamnoni biyu da aka yi kafin Tambuwal da Ahmad. Domin kuwa ana iya ganawa da Bafarawa a ofis ko gida a wancan lokacin da yake gwamnan Jihar Sakkwato. Shi Aliyu Wamakko sha-kundum ne domin kusan kowa na iya ganawa da shi a ko ina ta kama sa’ilin da yake gwamna. Ashe kuwa kyawon da ya gaji ubansa.

Ai ba kowa ne zai ce sai ya gana da gwamna ba, sai wanda ke ganin matsayinsa ya kai. Wannan sanken ne ke kawo shakku ga manyan ‘yan bokonmu da sauran masana a Sakkwato da ke da zimmar zuwa don bayar da shawara ga gwamnan ko ‘yan majalisarsa. Akwai ma bayanan da ke nuna cewa galibin kwamishinonin gwamnatin Sakkwato ba su daukar waya ko da ta wanda suka sani ce. Da fatar za a gyara.

Daga Dakta Sajo Sanyinna, malami ne a jami’ar Usmanu Danfodiyo kuma tsohon shugaban kungiyar ‘yan jarida ta kasa reshen Jihar Sakkwato

Sakkwato
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Yadda Arsenal Ta Lashe Gasar Firimiya Bayan Shekara 22
  • Leadership Hausa
    Bukatar Kawo Karshen Akidar Kyamar Baki A Kasar Afirka Ta Kudu

MASU ALAKA

Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu
Manyan Labarai

Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu

June 14, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF
Rahotonni

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin
Rahotonni

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Next Post
Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

Gwamna Dauda Ya Ƙaddamar Da Aikin Sake Gina Asibitin Talata Mafara

LABARAI MASU NASABA

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

Gidajen Gala Ne Kadai Mafita Ga Masana’antar Kannywood – Falalu Dorayi

June 14, 2026
Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu

Gwamnati Ba Za Ta Saki ’Yan Ta’adda Ba Duk Da Kisan Tsohon Kakakin DHQ — Tinubu

June 14, 2026
Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

Yadda Ake Wainar Masara Da Miyar Yaji

June 14, 2026
Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

Hanyoyin Hada Humra Mai Kamshi

June 14, 2026
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su Lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu (1)

June 13, 2026
Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

Talauci Ya Sake Karuwa Da Kashi 63 Duk Da Sauye-sauyen Tattalin Arzikin Da Gwamnati Ta Yi – IMF

June 13, 2026
Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

Muhallin Halittu Da Aka Yi Gado A Kasar Sin Sun Samu Ci Gaba Ta Fuskar Ba Su Kariya

June 13, 2026
Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

Gwamnonin Arewa-maso-yamma Sun Kaddamar Da Shirin Rage Radadin Talauci A Yankin

June 13, 2026
Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

Sake Jan Damarar Soja Da Japan Ke Yi Karin Alama Ce Mai Hadari

June 14, 2026
NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

NANS Ta Kafa Kwamitin Ganin Yadda Ake Tafiyar Da Ayyukan TETFund

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.