• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Abokin Daka Akan Sha Gari

by CMG Hausa
3 years ago
Gari

Kamar yadda muke ji yau da kullum daga bakin masana, cewa babu wata kasa a duniyar nan da za ta samu cikakken ci gaba, ba tare da bunkasa yankunanta na karkara ba, muna iya ganin shaidu na zahiri don gane da hakan a nan kasar Sin.

Mahukuntan kasar Sin sun jima da fahimtar muhimmancin kawar da kangin talauci da raya karkara, a matsayin babban jigon gina kasa, tare da tabbatar da ba a bar wani bangare na alummar Sinawa a baya ba.

Kaza lika da yake yankunan karkara na taka muhimmiyar rawa wajen gina kasa, ta hanyar samar da nauo’in cimaka, kama daga hatsi, da kayan lambu da ’yayan itatuwa, gudummawar sassan na karkara na kan gaba wajen tabbatar da samar da isasshen abinci ga daukacin yankunan kasar, hakan ya sa har kullum, gwamnatin Sin ke kara azama wajen ganin yankunan karkara sun kara azamar fita daga talauci, da samun kyakkyawar rayuwa.

Bahaushe kan ce Da ruwan ciki a kan ja na rijiya, har kullum mahukuntan Sin na dagewa wajen ganin yankunan karkarar kasar sun samu dukkanin tallafin da suke bukata na raya sanao’i, da inganta damammakin samar da ilimi, lafiya da sauran ababen more rayuwa.

Wannan ne ma ya sa duk da yawan ayyukan dake gaban shugaban kasar Xi Jinping, wanda kuma shi ne babban sakataren kolin JKS, ya kan ware lokuta musamman domin ziyartar yankunan karkarar kasar Sin, ya gana da jamaar yankunan, ya ji koken su, da yanayin rayuwar su, da irin ci gaban da suka samu karkashin manufofin wanzar da ci gaba.

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Wani abun birgewa game da manufar gwamnatin Sin mai ci shi ne yadda take karfafa gwiwar yankunan karkara, wajen tashi tsaye domin dogaro da kai. Cikin kalaman shugaba Xi Jinping ya taba bayyana cewa Idan har burin mu shi ne kallon na sama da mu, muna neman a taimaka mana, muna korafin rashin samun dama kamar saura, ta yaya za mu iya samun karfin gwiwar yakar fatara?”
Ziyarar da shugaba Xi Jinping ya kai kauyen Yongfeng na lardin Sichuan a cikin makon nan, ta shaida wannan muhimmiyar manufa, domin kuwa yayin da yake rangadi a kauyen na Yongfeng, ya nazarci yadda ake kara azamar kyautata samar da kayan noma na zamani, da matakan bunkasa samar da hatsi a yankin, da ayyukan raya karkara, da matakan dakile yaduwar annobar COVID-19.

Wannan ziyara ta shugaba Xi, ta dada shaida burin mahukuntan Sin, na yin tafiyar samar da ci gaba tare da dukkanin yankunan kasar, ta yadda kowa zai ci gajiya daga alfanun manufofin kawar da talauci, da wanzar da ci gaba, da gina alumma mai makomar bai daya ga kowa, kamar dai yadda a kan ce Da abokin daka a kan sha gari. (Saminu Hassan)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka
Daga Birnin Sin

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Next Post
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

Jami’an Tsaro Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar #FreeNnamdiKanuNow A Abuja

October 20, 2025
Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

Wani Mai Taɓin Hankali Ya Kashe Mutum 1, Ya Raunata 3 A Taraba

October 20, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kama Alburusai 400 A Delta

October 20, 2025
Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.