• English
  • Business News
Tuesday, July 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Abokin Daka Akan Sha Gari

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Da Abokin Daka Akan Sha Gari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kamar yadda muke ji yau da kullum daga bakin masana, cewa babu wata kasa a duniyar nan da za ta samu cikakken ci gaba, ba tare da bunkasa yankunanta na karkara ba, muna iya ganin shaidu na zahiri don gane da hakan a nan kasar Sin.

Mahukuntan kasar Sin sun jima da fahimtar muhimmancin kawar da kangin talauci da raya karkara, a matsayin babban jigon gina kasa, tare da tabbatar da ba a bar wani bangare na alummar Sinawa a baya ba.

Kaza lika da yake yankunan karkara na taka muhimmiyar rawa wajen gina kasa, ta hanyar samar da nauo’in cimaka, kama daga hatsi, da kayan lambu da ’yayan itatuwa, gudummawar sassan na karkara na kan gaba wajen tabbatar da samar da isasshen abinci ga daukacin yankunan kasar, hakan ya sa har kullum, gwamnatin Sin ke kara azama wajen ganin yankunan karkara sun kara azamar fita daga talauci, da samun kyakkyawar rayuwa.

Bahaushe kan ce Da ruwan ciki a kan ja na rijiya, har kullum mahukuntan Sin na dagewa wajen ganin yankunan karkarar kasar sun samu dukkanin tallafin da suke bukata na raya sanao’i, da inganta damammakin samar da ilimi, lafiya da sauran ababen more rayuwa.

Wannan ne ma ya sa duk da yawan ayyukan dake gaban shugaban kasar Xi Jinping, wanda kuma shi ne babban sakataren kolin JKS, ya kan ware lokuta musamman domin ziyartar yankunan karkarar kasar Sin, ya gana da jamaar yankunan, ya ji koken su, da yanayin rayuwar su, da irin ci gaban da suka samu karkashin manufofin wanzar da ci gaba.

Labarai Masu Nasaba

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Wani abun birgewa game da manufar gwamnatin Sin mai ci shi ne yadda take karfafa gwiwar yankunan karkara, wajen tashi tsaye domin dogaro da kai. Cikin kalaman shugaba Xi Jinping ya taba bayyana cewa Idan har burin mu shi ne kallon na sama da mu, muna neman a taimaka mana, muna korafin rashin samun dama kamar saura, ta yaya za mu iya samun karfin gwiwar yakar fatara?”
Ziyarar da shugaba Xi Jinping ya kai kauyen Yongfeng na lardin Sichuan a cikin makon nan, ta shaida wannan muhimmiyar manufa, domin kuwa yayin da yake rangadi a kauyen na Yongfeng, ya nazarci yadda ake kara azamar kyautata samar da kayan noma na zamani, da matakan bunkasa samar da hatsi a yankin, da ayyukan raya karkara, da matakan dakile yaduwar annobar COVID-19.

Wannan ziyara ta shugaba Xi, ta dada shaida burin mahukuntan Sin, na yin tafiyar samar da ci gaba tare da dukkanin yankunan kasar, ta yadda kowa zai ci gajiya daga alfanun manufofin kawar da talauci, da wanzar da ci gaba, da gina alumma mai makomar bai daya ga kowa, kamar dai yadda a kan ce Da abokin daka a kan sha gari. (Saminu Hassan)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Kumbon Shenzhou-14 Ya Kara Samar Da Ci Gaban ’Yan Adam Baki Daya

Next Post

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata

Related

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

9 hours ago
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki
Daga Birnin Sin

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

10 hours ago
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko
Daga Birnin Sin

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

11 hours ago
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan
Daga Birnin Sin

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

11 hours ago
Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan
Daga Birnin Sin

Sin Na Bikin Cika Shekaru 88 Da Dukkan Al’ummar Kasar Ta Fara Yakin Kin Jinin Harin Sojojin Japan

12 hours ago
Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin: Kasarsa Ta Kimtsa Tsaf Wajen Inganta Aikin BRI Da Bunkasa Kasuwanci Da Zuba Jari Tare Da Habasha

13 hours ago
Next Post
Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata

Cinikin Waje Na Kasar Sin Ya Bunkasa Yadda Ya Kamata

LABARAI MASU NASABA

Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa

Nijeriya Ba Ta Da Sha’awar Yin Gwajin Makamin Nukiliya — Shettima

July 8, 2025
Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

Da Ɗumi-Ɗumi: Osimhen Ya Amince Da Komawa Galatasaray Na Dindindin

July 7, 2025
Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

Sin Za Ta Ci Gaba Da Karfafa Hadin Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Tinkarar Sauyin Yanayi

July 7, 2025
Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

Ƙungiyar Al’ummar Igbo Ta Ohanaeze Ndigbo Ta Ce Tinubu Ya Fi Ƙarfin ‘Yan Jam’iyyar Haɗaka Ta ADC

July 7, 2025
Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

Sin Za Ta Gina Wuraren Cajin Ababen Hawa Masu Ingantaccen Lantarki

July 7, 2025
NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

NiMet Ta Yi Hasashen Cikin Watan Yulin 2025 Za A Tabka Ambaliyar Ruwan Sama A Jihohin Nijeriya 19

July 7, 2025
Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

Sin Ta Kafa Kungiyar Masana Masu Binciken Sararin Samaniya Mai Zurfi Ta Farko

July 7, 2025
Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

Xi Ya Ajiye Furanni Ga Wadanda Suka Mutu Yayin Yakin Bijirewa Harin Japan

July 7, 2025
Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

Asibiti Mai Zaman Kansa A Kano Zai Fara Aikin Manyan Tiyatu Tare Da Rage Kuɗi Kaso 50%

July 7, 2025
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista

July 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.