• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Buhari Ya Cire Tallafin Mai Da Tinubu Bai Zama Shugaban Kasa Ba —Garba Shehu

byKhalid Idris Doya
2 years ago
Tallafin Mai

Garba Shehu, kakakin tsohon Shugaban Kasa, Muhammadu Buhari, ya ce da Buhari ya sanya hannu kan dokar cire tallafin mai da yanzu shugaba Bola Ahmed Tinubu bai zama shugaban kasa ba.

Shehu, ya wallafa hakan ne a shafinsa na Twitter, inda ya bayyana dalilin da suka sanya Buhari bai sanya hannu kan dokar ba, da kuma yadda cire tallafin da Tinubu ya yi tun farkon hawansa mulki.

  • Amarya Da Kanwar Mijinta Sun Kubuta Daga Hannun Wadanda Suka Sace Su
  • Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

Lamarin ya sanya wasu na tambayar me ya sa Buhari bai cire tallafin ba shekarun da ya kwashe a mulki.

Garba Shehu ya ce tabbas da APC ta fadi a zaben 2023 da Buhari ya cire tallafin man.

Ya ce, ya amince zai yi bayanin ne domin jama’a na tambaya kan cire tallafin da neman bayanin kan mene ne ya hana Buhari sanya hannun tare da muhawarar da suka biyo bayan sausa fasalin kudi.

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Ya ce kamata ya yi jam’iyya ta fito ta ba da amsa kan tambayoyin amma tilas dai ya sanya su fito su ce wani abu.

“Tabbas gwamnatin Tinubu da Shettima ta yi abun a yaba na cire tallafin mai. Mun yi imanin janye tallafin mai ba don shugaban kasa ne kawai ko don muradin kansa ba. Lamari ne da ya shafi al’ummar kasa.”

Ya ce batun janye tallafin mai da sauya takardun kudi lamari ne da suka janyo muhawara amma sai gwamnatin Buhari ta jingine batun janye tallafin mai zuwa lokacin da ya dace domin lamura su tafi daidai.

Ya kara da cewa lokacin da abubuwa suka yunkuro a lokacin zaben 2023 da gwamnatin Buhari ta dage kan cire tallafin mai da ‘yan kasa sun yi hannun riga da APC ta hanyar da za su kaurace wa zabar jam’iyyar.

“Amma sai muka yi la’akari da siyasarmu. Sai gwamnatin Buhari ta jingine batun cire tallafin mai domin jam’iyyar APC ta samunasara a zabe. Kuma hakan ya taimaka har aka samu nasara.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki
Labarai

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu
Labarai

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
‘Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sintiri, Sun Yi Wa Mata Fyade A Katsina

'Yan Bindiga Sun Kashe Dan Sintiri, Sun Yi Wa Mata Fyade A Katsina

LABARAI MASU NASABA

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version