ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Za Mu Kawar Da Matsalar Tsaro A Nijeriya -Nuhu Ribadu

by Sadiq
3 years ago
Tsaro

Sabon mai bai wa shugaba Tinubu shawara kan harkokin tsaro kuma tsohon shugaban hukumar EFCC Nuhu Ribadu, ya kama aiki ranar Litinin, inda ya yi alkawarin samar da zaman lafiya a Nijeriya.

Nuhu Ribadu, wanda ya gaji Manjo-Janar Babagana Monguno bayan ayyana shi da shugaba Tinubu ya yi a ranar 19 ga watan Yuni ya sha alwashin kawo karshen matsalar tsaro tare da samar da daidaito a Nijeriya.

  • Amarya Da Kanwar Mijinta Sun Kubuta Daga Hannun Wadanda Suka Sace Su
  • Dan Sanda Ya Shiga Hannu Kan Yunkurin Kashe Abokin Aikinsa A Kaduna

Wannan al’amari na zuwa a daidai lokacin da babban hafsan tsaron Nijeriya Manjo-Janar Christopher Musa ya tabbatar da cewa rundunar tsaron Nijeriya karkashin ikonsa za ta yi iya kokarinta na tattabar da maido da zaman lafiya a kasar nan.

ADVERTISEMENT

Musa ya yi wadanan kalaman ne, a daidai sa’ilin da ma’aikatar tsaron kasar nan ta ke kokarin assasa wani ofishi da kuma ma’aikatar masana’antu na sojoji.

Ribadu, ya ce akwai gagarumin aiki a gaban gwamnatin Tinubu wajen tabbatar da kasancewar Nijeriya kasa daya da kuma daidaita al’amura a kasar.

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Mai ba da shawara kan lamurran tsaron kasar ya ce “wannan aikin ne da za’a yi wa ‘yan Nijeriya kuma manufarmu ita ce mu ci gaba da aikin da aka riga aka soma.”

“Za mu daidaita al’amuran kasar nan, za mu tsare kasar mu, kuma za mu samar da zaman lafiya a Nijeriya domin muna da yakinin cewa lokaci ya yi da kasarmu za ta ci moriyar zaman lafiya da dawo da doka da oda kamar yadda ya ke a sauran kasashen duniya” in ji shi.

Ya kara da cewa “tabbatar da ci gaba da dorewar a matsayin kasa wani abu ne da za mu ci gaba da aiki a kai. Za mu duba muga ayyukan da aka yi a baya sannan sai mu dora a kai. Domin cimma wannan manufa, za mu bukaci hadin kan ‘yan Nijeriya domin samun damar gudanar da ayukan mu kamar yadda ya kamata”.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

Mahajjata Sama Da Miliyan 2 Ne Za Su Yi Aikin Hajjin Bana

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.