ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul’aziz Bisa Sharadi Uku

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Dakta Idris

Kotun Majistire mai lamba ta daya da ke Bauchi ta amince da bukatar bayar da belin Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi bisa sharadin guda uku.

 

Idan za a tuna dai, ‘yansandan sun gurfanar da Malamin ne a gaban kotun bisa zarginsa da tada zaune tsaye da ka iya barazana ga zaman lafiyan jama’a. Kuma hakan ya biyo bayan korafin da kungiyar Fitiyanul Islam ta shigar ne a kansa.

ADVERTISEMENT
  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tasa Ƙeyar Dr. Idris Kan Zargin Kalaman Batanci Ga Manzon Allah

Da ya ke yanke hukunci kan bukatar belin, Mai Shari’a Abdulfata Baba Shakoni, ya ce, ya amince da bukatar belin malamin bisa sharadi guda uku, na farko zai kawo Hakimi, na biyu Babban Sakatare da ke aiki a karkashin Gwamnatin jihar Bauchi da kuma wani Malami da ke kwayan Bauchi.

 

LABARAI MASU NASABA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Kazalika, ofishin Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a ta jihar Bauchi sun bukaci kotun da ta amince musu su amshi ragamar karar daga hannun ‘yansanda domin cigaba da Shari’ar.

 

Daga bisani kotun ta amince da wannan bukatar.

 

Da ya ke karin haske kan hukuncin, daya daga cikin lauyoyin da suke kare malamin, Barista Sadik Abubakar Ilelah, ya nuna farin cikinsu bisa samun belin malamin tare da cewa insha Allahu za su cika sharudan da Alkalin ya gindaya.

 

Da yake bayani kan amsar ragamar karar da suka yi, daya daga cikin lauyoyin a ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, Aliyu Ibn Idris, ya ce, “Shi Antoni Janar na jiya ko na tarayya yana da dama da dalili ba dalili ya shiga cikin kara.”

 

“Antoni Janar ya shigo ya karbi Kes ba sabon abu ba ne. Iyakaci abun da za a duba shigowar tamu za ta haifar da adalci ko ba za ta haifar da adalci ba. Insha Allahu za mu yi iyaka abun da za mu yi a wanzan da adalci a kai,” Inji shi.

 

Sannan, ma’aikatan shari’an ta bukaci ‘yanda da su ba su kundin Shari’ar da sauran abubuwan da suka hada wajen shigar da cajin domin nazarin akwai bukatar canzawa ko a’a.

 

Daga bisani dai Alkalin ya dage shari’ar zuwa ranar 24 ga watan nan da muke ciki domin cigaba da shari’a.

 

Wakilinmu ya labarto cewa an sake komawa da malamin zuwa gidan yari har zuwa lokacin da za su cika sharadin belin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci
Manyan Labarai

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya
Manyan Labarai

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4
Manyan Labarai

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
Next Post
Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

LABARAI MASU NASABA

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

Abin Da Ya Sa NPA Ta Yi Hadaka Da ‘Snake Island Port’ -Dakta Dantsoho

November 14, 2025
Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

Shugaban NPA Ya Bukaci A Yi Hadaka Domin Cin Gajiyar Albarkatun Fannin Sufurin Afirka

November 14, 2025
Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

Bayan Barazanar Amurka: Sultan Ya Nemi Hadin Kan ‘Yan Nijeriya Wajen Yaki Da Ta’addanci

November 14, 2025
Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

Jan Aikin Da Ke Gaban Manyan Hafsoshin Tsaron Nijeriya

November 14, 2025
Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.