ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Bayar Da Belin Dakta Idris Abdul’aziz Bisa Sharadi Uku

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Dakta Idris

Kotun Majistire mai lamba ta daya da ke Bauchi ta amince da bukatar bayar da belin Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi bisa sharadin guda uku.

 

Idan za a tuna dai, ‘yansandan sun gurfanar da Malamin ne a gaban kotun bisa zarginsa da tada zaune tsaye da ka iya barazana ga zaman lafiyan jama’a. Kuma hakan ya biyo bayan korafin da kungiyar Fitiyanul Islam ta shigar ne a kansa.

ADVERTISEMENT
  • Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tasa Ƙeyar Dr. Idris Kan Zargin Kalaman Batanci Ga Manzon Allah

Da ya ke yanke hukunci kan bukatar belin, Mai Shari’a Abdulfata Baba Shakoni, ya ce, ya amince da bukatar belin malamin bisa sharadi guda uku, na farko zai kawo Hakimi, na biyu Babban Sakatare da ke aiki a karkashin Gwamnatin jihar Bauchi da kuma wani Malami da ke kwayan Bauchi.

 

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

Kazalika, ofishin Antoni Janar kuma kwamishinan shari’a ta jihar Bauchi sun bukaci kotun da ta amince musu su amshi ragamar karar daga hannun ‘yansanda domin cigaba da Shari’ar.

 

Daga bisani kotun ta amince da wannan bukatar.

 

Da ya ke karin haske kan hukuncin, daya daga cikin lauyoyin da suke kare malamin, Barista Sadik Abubakar Ilelah, ya nuna farin cikinsu bisa samun belin malamin tare da cewa insha Allahu za su cika sharudan da Alkalin ya gindaya.

 

Da yake bayani kan amsar ragamar karar da suka yi, daya daga cikin lauyoyin a ma’aikatar shari’a ta jihar Bauchi, Aliyu Ibn Idris, ya ce, “Shi Antoni Janar na jiya ko na tarayya yana da dama da dalili ba dalili ya shiga cikin kara.”

 

“Antoni Janar ya shigo ya karbi Kes ba sabon abu ba ne. Iyakaci abun da za a duba shigowar tamu za ta haifar da adalci ko ba za ta haifar da adalci ba. Insha Allahu za mu yi iyaka abun da za mu yi a wanzan da adalci a kai,” Inji shi.

 

Sannan, ma’aikatan shari’an ta bukaci ‘yanda da su ba su kundin Shari’ar da sauran abubuwan da suka hada wajen shigar da cajin domin nazarin akwai bukatar canzawa ko a’a.

 

Daga bisani dai Alkalin ya dage shari’ar zuwa ranar 24 ga watan nan da muke ciki domin cigaba da shari’a.

 

Wakilinmu ya labarto cewa an sake komawa da malamin zuwa gidan yari har zuwa lokacin da za su cika sharadin belin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026
Labarai

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano
Kotu Da Ɗansanda

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026
Labarai

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Next Post
Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

Taimkon Juna Tushen Dangantakar Sin Da Afrika

LABARAI MASU NASABA

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

NAHCON Ta Ƙaddamar Da Kwamitin Da Zai Kula Da Shafin Nusuk Masar Na Hajjin 2026

November 14, 2025
NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

NSCDC Ta Cafke Mutum Biyu Bisa Zargin Satar NAPEP Da Safarar Miyagun Kwayoyi A Kano

November 14, 2025
Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

Gwamnan Gombe Ya Gabatar Da Naira Biliyan 535.69 A Matsayin Kasafin 2026

November 14, 2025
Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

Sin Za Ta Mayar Da Martani Idan Har Japan Ta Aiwatar Da Matakin Da Bai Dace Ba

November 14, 2025
Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

Tinubu Ya Zuba Naira Tiriliyan 1.5 Don Bunkasa Noma Da Kayan Aiki Na Zamani

November 14, 2025
Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

Jirgin Ruwan Dakon Jiragen Saman Yaki Na Sichuan Ya Fara Gwajin Sufuri A Karon Farko

November 14, 2025
Rashin Daukar Tsauraran Matakai Na Iya Durkusar Da Bangaren Noma – Shehu Galadima

Dalilin Asusun NADF Na Yin Hadaka Da Gwamnatin Jihar Jigawa

November 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

Xi Jinping Ya Gana Da Sarkin Thailand

November 14, 2025
BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

BUK Za Ta Kafa Cibiyar Horas da Aikin Jarida da Sabbin Kafofin Sadarwa Na Zamani

November 14, 2025
Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

Babban Taron Kawancen Sin Da Afirka Ya Nuna Hadin Gwiwa Kan Gudanar Da Tsarin Shugabancin Duniya Na Bai-Daya

November 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.