ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, November 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Da Sauran Rina A Kaba A Kokarin Masu Ruwa Da Tsakin Jam’iyyar PDP Na Shawo Kan Wike

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Wike

A kokarin lalibowa da nemo mafita ta karshe kan rikicin da ke faruwa a cikin jam’iyyar PDP, mambobin Majalisar amintattu na jam’iyyar sun gana da gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike, a gidan gwamnati da ke Fatakwal a ranar Talata.

Da yake magana bayan kammala ganawar sirri da suka yi tare da gwamnan, mai rikon mukamin Shugaban Majalisar amintattu na jam’iyyar kuma tsohon Shugaban Majalisar Dattawa, Adolphus Wabara, ya ce, ganawar ta gudana cikin kwankiyar hankali amma dai ba kammalata ba tukunna, inda ya ayyana ta a matsayin ‘Inkunkulusib’.

  • Kwamitin Amintattu Na PDP Ya Gana Da Wike Kan Rikicin Jam’iyyar

Wabara ya ce: “Mun kwashe sama da awanni hudu muna tattaunawa da hazikin gwamna na jihar Ribas. Mun shafe sama da awa hudu amma ba a kammala ganawar ba.

ADVERTISEMENT

“Kun san tabbatar da zaman lafiya na iya daukan lokaci. Amma, Ina tunanin mun kusa cimma gaci. Mun na da kwarin guiwa. Mun ji bangaren gwamnan. Za mu koma Abuja mu hado duk abubuwan da muka tattaro.

“Ganawarmu ta yi armashi, amma wani abu guda da nake son kowa ya sani shine wannan ahlin za ta ci gaba da zama gida daya a lema daya wato PDP, kuma da izinin Allah za mu kai ga kammalawa cikin nasara. Tare da hadin kai shi (Wike) da sauran dukkanin Gwamnoni za mu kai mataki na gaba.”

LABARAI MASU NASABA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

Ya nuna kwarin guiwarsa na cewa nan kusa kadan za su shawo kan matsalolin tare da tabbatar da cewa PDP ta Kara zama a karkashin lema daya domin tunkarar abubuwan da suke gabanta.

Ya kara da cewa a daidai lokacin da gangamin yakin neman zaben na shugaba kasa ya kankama, jam’iyyar za ta tabbatar dukkanin abubuwan da suka kamata suna layin da ya dace domin kai jam’iyyar ga nasara.

Da yake ganawa da ‘yan jarida, gwamnan Jihar Ribas, Nyesom Ezenwo Wike, ya ce, abu mai matukar muhimmanci shine PDP tana dinke wuri guda.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP
Siyasa

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja
Labarai

Majalisar Wakilai Ta Yi Tir Da Harin Da Aka Kai Wa Tawagar Ɗan Majalisar Neja

November 7, 2025
Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha
Siyasa

Dalilin Da Ya Sa Sanatoci Ba Su Goyi Bayana Ba Lokacin Da Aka Dakatar Da Ni – Natasha

November 4, 2025
Next Post
‘Yan Takarar PDP Sun Maka Ayu, Anyanwu Da Wasu A Komar EFCC Kan Zargin Badakalar Kudade

'Yan Takarar PDP Sun Maka Ayu, Anyanwu Da Wasu A Komar EFCC Kan Zargin Badakalar Kudade

LABARAI MASU NASABA

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025
An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

An Kafa Cibiyar Kiwon Lafiya Ta Hadin Gwiwa Ta Farko Tsakanin Sin Da Afirka A Guinea

November 13, 2025
Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

Jiga Jigan APC Sun Ziyarci Majalisar Wakilai Bayan Sauya Sheƙar Ƴan NNPP 2

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.