• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 14 ga wata bisa agogon wurin, gwamnatin Amurka ta sanar da kara kakaba haraji a kan wasu kayayyaki daga kasar Sin da kudinsu ya kai dalar Amurka kimanin biliyan 18, kafin daga bisani shugaban kasar ta Amurka Joe Biden ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “dazun nan na sanar da kakaba jerin sabbin haraji a kan kayayyakin da ake shigar da su daga kasar Sin, kaso 15% a kan karafa da Saholami da kaso 100% a kan motoci masu amfani da lantarki, sai kuma kaso 50% a kan farantan samar da lantarki ta hasken rana. Kasar Sin na da niyyar jagorantar sana’o’i masu alaka, ni kuma ina da niyyar tabbatar da fifikon Amurka a fannonin.” 

Abin dariya shi ne, a ranar 12 ga watan Yunin shekarar 2019, shugaba Biden din da kan sa ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “Trump ba shi da masaniya, yana ganin kasar Sin za ta biya harajin da ya buga, amma kowane dalibi da ya fara karanta ilmin tattalin arziki zai iya tabbatar da cewa, jama’ar kasar Amurka ne suke biya. Ko mai karbar kudin kaya a kantin sayar da kayayyakin masarufi na “Target” ya san me ke faruwa, sun fi Trump sanin tattalin arziki.”

  • Matakin Amurka Na Kara Buga Harajin Kwastam Kan Hajojin Sin Babban Kurkure Ne
  • Xi Ya Yi Kira Da A Karfafa Azamar Yayatawa Da Kare Babbar Ganuwar Kasar Sin

Shin ko Mr. Biden shi ma ya rasa ilminsa na tattalin arziki bayan da ya hau kujerar shugaban kasar Amurka? A’a, ba haka ba ne, yana da cikakkiyar masaniya a kan me harajin da ya kakaba zai haifar ga kamfanonin kasar da ma al’ummarta. Bisa kididdigar da kamfanin Moody ya yi, masu sayayya na kasar Amurka suna biyan kaso 92% na harajin da gwamnatin kasarsu ta sanya wa kayayyakin kasar Sin, abin da ya sa duk wani magidancin kasar ke biyan karin dala 1300 a kowace shekara. Wani sharhin da jaridar Wallstreet Journal ta fitar a ranar 14, ya yi nuni da cewa, matakin da gwamnatin Amurka ta dauka tabbas zai gurgunta tsarin samar da kayayyaki ga kamfanonin kasar Amurka, wanda hakan zai kara kudin da masu sayayya da ma kamfanoni na kasar suke biya.

Amma me ya faru ga shugaba Biden har ya sauya matsayinsa a kan batun haraji a kan kayayyakin kasar Sin. Lallai bana ne za a gudanar da babban zabe a kasar Amurka, amma tattalin arzikin kasar na fama da matsalolin da suka hada da hauhawar farashin kaya, da babban gibin kudi da sauransu, don haka ma gwamnatin kasar kamar yadda ta saba yi, take kokarin karkata hankalin al’ummarta ga kasashen ketare. Yadda gwamnatin Biden ta dauki wannan mataki a daidai wannan lokaci, manufa ce ta siyasa, ta bayyana tsattsauran matsayinta a kan kasar Sin, don neman samun karin kuri’u a wasu jihohi marasa tabbaci.

A ganin Clark Packard, masani a cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka, sabon matakin haraji da gwamnatin Biden ta dauka, ya sake dora burin siyasa da yake neman cimmawa a kan muradun kasar baki daya. A zahiri dai, idan an kwatanta da abin da yake neman cimmawa ta fannin siyasa, moriyar kasa da ta jama’a sam ba su da daraja, ballantana ma batun ingancin tsarin samar da kayayyaki na duniya, da farfadowar tattalin arzikin duniya, da‘yancin ciniki, da ma kokarin da kasa da kasa ke yi na tinkarar sauyin yanayi.

Labarai Masu Nasaba

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Duk da haka, daukar matakan da ba su dace ba na dakile kamfanonin wasu kasashe, ba kawai zai lalata moriyar kamfanoni da masu sayayya na kasar ba ne, har ma zai lalata bunkasuwar masana’antu masu nasaba na kasar ita kan ta. Yadda ‘yan siyasar kasar suke iya kokarin cin babban zabe, amma suna zubar da kimar kasar a idon duniya, kuma zai haifar musu da karin matsaloli a cikin gida. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCi gaban tattalin arzikin SinHajojin sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shari’ar Ganduje Ta Ɗauki Zafi, An Sauya Alƙali

Next Post

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

Related

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu
Daga Birnin Sin

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

2 hours ago
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO
Daga Birnin Sin

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

3 hours ago
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles
Daga Birnin Sin

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

4 hours ago
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba
Daga Birnin Sin

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

5 hours ago
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

6 hours ago
Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama
Daga Birnin Sin

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

1 day ago
Next Post
Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.