• English
  • Business News
Thursday, September 18, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump

by CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 14 ga wata bisa agogon wurin, gwamnatin Amurka ta sanar da kara kakaba haraji a kan wasu kayayyaki daga kasar Sin da kudinsu ya kai dalar Amurka kimanin biliyan 18, kafin daga bisani shugaban kasar ta Amurka Joe Biden ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “dazun nan na sanar da kakaba jerin sabbin haraji a kan kayayyakin da ake shigar da su daga kasar Sin, kaso 15% a kan karafa da Saholami da kaso 100% a kan motoci masu amfani da lantarki, sai kuma kaso 50% a kan farantan samar da lantarki ta hasken rana. Kasar Sin na da niyyar jagorantar sana’o’i masu alaka, ni kuma ina da niyyar tabbatar da fifikon Amurka a fannonin.” 

Abin dariya shi ne, a ranar 12 ga watan Yunin shekarar 2019, shugaba Biden din da kan sa ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “Trump ba shi da masaniya, yana ganin kasar Sin za ta biya harajin da ya buga, amma kowane dalibi da ya fara karanta ilmin tattalin arziki zai iya tabbatar da cewa, jama’ar kasar Amurka ne suke biya. Ko mai karbar kudin kaya a kantin sayar da kayayyakin masarufi na “Target” ya san me ke faruwa, sun fi Trump sanin tattalin arziki.”

  • Matakin Amurka Na Kara Buga Harajin Kwastam Kan Hajojin Sin Babban Kurkure Ne
  • Xi Ya Yi Kira Da A Karfafa Azamar Yayatawa Da Kare Babbar Ganuwar Kasar Sin

Shin ko Mr. Biden shi ma ya rasa ilminsa na tattalin arziki bayan da ya hau kujerar shugaban kasar Amurka? A’a, ba haka ba ne, yana da cikakkiyar masaniya a kan me harajin da ya kakaba zai haifar ga kamfanonin kasar da ma al’ummarta. Bisa kididdigar da kamfanin Moody ya yi, masu sayayya na kasar Amurka suna biyan kaso 92% na harajin da gwamnatin kasarsu ta sanya wa kayayyakin kasar Sin, abin da ya sa duk wani magidancin kasar ke biyan karin dala 1300 a kowace shekara. Wani sharhin da jaridar Wallstreet Journal ta fitar a ranar 14, ya yi nuni da cewa, matakin da gwamnatin Amurka ta dauka tabbas zai gurgunta tsarin samar da kayayyaki ga kamfanonin kasar Amurka, wanda hakan zai kara kudin da masu sayayya da ma kamfanoni na kasar suke biya.

Amma me ya faru ga shugaba Biden har ya sauya matsayinsa a kan batun haraji a kan kayayyakin kasar Sin. Lallai bana ne za a gudanar da babban zabe a kasar Amurka, amma tattalin arzikin kasar na fama da matsalolin da suka hada da hauhawar farashin kaya, da babban gibin kudi da sauransu, don haka ma gwamnatin kasar kamar yadda ta saba yi, take kokarin karkata hankalin al’ummarta ga kasashen ketare. Yadda gwamnatin Biden ta dauki wannan mataki a daidai wannan lokaci, manufa ce ta siyasa, ta bayyana tsattsauran matsayinta a kan kasar Sin, don neman samun karin kuri’u a wasu jihohi marasa tabbaci.

A ganin Clark Packard, masani a cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka, sabon matakin haraji da gwamnatin Biden ta dauka, ya sake dora burin siyasa da yake neman cimmawa a kan muradun kasar baki daya. A zahiri dai, idan an kwatanta da abin da yake neman cimmawa ta fannin siyasa, moriyar kasa da ta jama’a sam ba su da daraja, ballantana ma batun ingancin tsarin samar da kayayyaki na duniya, da farfadowar tattalin arzikin duniya, da‘yancin ciniki, da ma kokarin da kasa da kasa ke yi na tinkarar sauyin yanayi.

Labarai Masu Nasaba

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Duk da haka, daukar matakan da ba su dace ba na dakile kamfanonin wasu kasashe, ba kawai zai lalata moriyar kamfanoni da masu sayayya na kasar ba ne, har ma zai lalata bunkasuwar masana’antu masu nasaba na kasar ita kan ta. Yadda ‘yan siyasar kasar suke iya kokarin cin babban zabe, amma suna zubar da kimar kasar a idon duniya, kuma zai haifar musu da karin matsaloli a cikin gida. (Mai Zane:Mustapha Bulama)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaCi gaban tattalin arzikin SinHajojin sin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Shari’ar Ganduje Ta Ɗauki Zafi, An Sauya Alƙali

Next Post

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

Related

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka
Daga Birnin Sin

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

9 minutes ago
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya
Daga Birnin Sin

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

1 hour ago
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14
Daga Birnin Sin

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

2 hours ago
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing
Daga Birnin Sin

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

3 hours ago
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar
Daga Birnin Sin

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

5 hours ago
Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 
Daga Birnin Sin

Ya Kamata A Kiyaye Nasarorin Da Aka Cimma A Shawarwarin Sin Da Amurka 

23 hours ago
Next Post
Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

Likitocin Sin Dake Aikin Agajin Kiwon Lafiya A Nijar Sun Gudanar Da Tiyatar ALT A Karon Farko A Yammacin Afirka

September 18, 2025
Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

Fim Mai Taken 731 Na Tunatar Da Jama’a Muhimmancin Kiyaye Zaman Lafiya

September 18, 2025
Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

Kotun Sojin Nijeriya Ta Yanke Hukuncin Kisa Kan Wani Soja Da Ya Kashe Ɗan Adaidaita

September 18, 2025
Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

Sashen Raya Kimiyya Da Fasaha Na Sin Ya Kai Babban Matsayi Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 14

September 18, 2025
Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

Jose Mourinho Ya Zama Sabon Kocin Benfica

September 18, 2025
An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

An Bude Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan Karo Na 12 A Birnin Beijing

September 18, 2025
NNPP

Gwamna Yusuf Ya Nuna Jin Daɗinsa Kan Yadda Kano Ta Zarce Legas, Oyo A Sakamakon NECO Na 2025

September 18, 2025
Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

Shugaban Guinea-Bissau Ya Goyi Bayan Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Da Sin Ta Gabatar

September 18, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Sojoji Sun Tarwatsa Wata Haramtacciyar Masana’antar Ƙera Makamai A Filato

September 18, 2025
Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

Ci Gaban Tattalin Arzikin Sin Na Taimaka Ga Bunkasa Al’adunta Da Mu’amalar Al’adu Tsakaninta Da Kasashen Duniya

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.