ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump

by CGTN Hausa
2 years ago
Trump

A ranar 14 ga wata bisa agogon wurin, gwamnatin Amurka ta sanar da kara kakaba haraji a kan wasu kayayyaki daga kasar Sin da kudinsu ya kai dalar Amurka kimanin biliyan 18, kafin daga bisani shugaban kasar ta Amurka Joe Biden ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “dazun nan na sanar da kakaba jerin sabbin haraji a kan kayayyakin da ake shigar da su daga kasar Sin, kaso 15% a kan karafa da Saholami da kaso 100% a kan motoci masu amfani da lantarki, sai kuma kaso 50% a kan farantan samar da lantarki ta hasken rana. Kasar Sin na da niyyar jagorantar sana’o’i masu alaka, ni kuma ina da niyyar tabbatar da fifikon Amurka a fannonin.” 

Abin dariya shi ne, a ranar 12 ga watan Yunin shekarar 2019, shugaba Biden din da kan sa ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “Trump ba shi da masaniya, yana ganin kasar Sin za ta biya harajin da ya buga, amma kowane dalibi da ya fara karanta ilmin tattalin arziki zai iya tabbatar da cewa, jama’ar kasar Amurka ne suke biya. Ko mai karbar kudin kaya a kantin sayar da kayayyakin masarufi na “Target” ya san me ke faruwa, sun fi Trump sanin tattalin arziki.”

  • Matakin Amurka Na Kara Buga Harajin Kwastam Kan Hajojin Sin Babban Kurkure Ne
  • Xi Ya Yi Kira Da A Karfafa Azamar Yayatawa Da Kare Babbar Ganuwar Kasar Sin

Shin ko Mr. Biden shi ma ya rasa ilminsa na tattalin arziki bayan da ya hau kujerar shugaban kasar Amurka? A’a, ba haka ba ne, yana da cikakkiyar masaniya a kan me harajin da ya kakaba zai haifar ga kamfanonin kasar da ma al’ummarta. Bisa kididdigar da kamfanin Moody ya yi, masu sayayya na kasar Amurka suna biyan kaso 92% na harajin da gwamnatin kasarsu ta sanya wa kayayyakin kasar Sin, abin da ya sa duk wani magidancin kasar ke biyan karin dala 1300 a kowace shekara. Wani sharhin da jaridar Wallstreet Journal ta fitar a ranar 14, ya yi nuni da cewa, matakin da gwamnatin Amurka ta dauka tabbas zai gurgunta tsarin samar da kayayyaki ga kamfanonin kasar Amurka, wanda hakan zai kara kudin da masu sayayya da ma kamfanoni na kasar suke biya.

ADVERTISEMENT

Amma me ya faru ga shugaba Biden har ya sauya matsayinsa a kan batun haraji a kan kayayyakin kasar Sin. Lallai bana ne za a gudanar da babban zabe a kasar Amurka, amma tattalin arzikin kasar na fama da matsalolin da suka hada da hauhawar farashin kaya, da babban gibin kudi da sauransu, don haka ma gwamnatin kasar kamar yadda ta saba yi, take kokarin karkata hankalin al’ummarta ga kasashen ketare. Yadda gwamnatin Biden ta dauki wannan mataki a daidai wannan lokaci, manufa ce ta siyasa, ta bayyana tsattsauran matsayinta a kan kasar Sin, don neman samun karin kuri’u a wasu jihohi marasa tabbaci.

A ganin Clark Packard, masani a cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka, sabon matakin haraji da gwamnatin Biden ta dauka, ya sake dora burin siyasa da yake neman cimmawa a kan muradun kasar baki daya. A zahiri dai, idan an kwatanta da abin da yake neman cimmawa ta fannin siyasa, moriyar kasa da ta jama’a sam ba su da daraja, ballantana ma batun ingancin tsarin samar da kayayyaki na duniya, da farfadowar tattalin arzikin duniya, da‘yancin ciniki, da ma kokarin da kasa da kasa ke yi na tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Duk da haka, daukar matakan da ba su dace ba na dakile kamfanonin wasu kasashe, ba kawai zai lalata moriyar kamfanoni da masu sayayya na kasar ba ne, har ma zai lalata bunkasuwar masana’antu masu nasaba na kasar ita kan ta. Yadda ‘yan siyasar kasar suke iya kokarin cin babban zabe, amma suna zubar da kimar kasar a idon duniya, kuma zai haifar musu da karin matsaloli a cikin gida. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Trump
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

MASU ALAKA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
Daga Birnin Sin

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus
Daga Birnin Sin

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos
Daga Birnin Sin

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Next Post
Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.