ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Karshe, Biden Ya Zamanto Irinsu Trump

by CGTN Hausa
2 years ago
Trump

A ranar 14 ga wata bisa agogon wurin, gwamnatin Amurka ta sanar da kara kakaba haraji a kan wasu kayayyaki daga kasar Sin da kudinsu ya kai dalar Amurka kimanin biliyan 18, kafin daga bisani shugaban kasar ta Amurka Joe Biden ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “dazun nan na sanar da kakaba jerin sabbin haraji a kan kayayyakin da ake shigar da su daga kasar Sin, kaso 15% a kan karafa da Saholami da kaso 100% a kan motoci masu amfani da lantarki, sai kuma kaso 50% a kan farantan samar da lantarki ta hasken rana. Kasar Sin na da niyyar jagorantar sana’o’i masu alaka, ni kuma ina da niyyar tabbatar da fifikon Amurka a fannonin.” 

Abin dariya shi ne, a ranar 12 ga watan Yunin shekarar 2019, shugaba Biden din da kan sa ya rubuta ta kafar sada zumunta cewa, “Trump ba shi da masaniya, yana ganin kasar Sin za ta biya harajin da ya buga, amma kowane dalibi da ya fara karanta ilmin tattalin arziki zai iya tabbatar da cewa, jama’ar kasar Amurka ne suke biya. Ko mai karbar kudin kaya a kantin sayar da kayayyakin masarufi na “Target” ya san me ke faruwa, sun fi Trump sanin tattalin arziki.”

  • Matakin Amurka Na Kara Buga Harajin Kwastam Kan Hajojin Sin Babban Kurkure Ne
  • Xi Ya Yi Kira Da A Karfafa Azamar Yayatawa Da Kare Babbar Ganuwar Kasar Sin

Shin ko Mr. Biden shi ma ya rasa ilminsa na tattalin arziki bayan da ya hau kujerar shugaban kasar Amurka? A’a, ba haka ba ne, yana da cikakkiyar masaniya a kan me harajin da ya kakaba zai haifar ga kamfanonin kasar da ma al’ummarta. Bisa kididdigar da kamfanin Moody ya yi, masu sayayya na kasar Amurka suna biyan kaso 92% na harajin da gwamnatin kasarsu ta sanya wa kayayyakin kasar Sin, abin da ya sa duk wani magidancin kasar ke biyan karin dala 1300 a kowace shekara. Wani sharhin da jaridar Wallstreet Journal ta fitar a ranar 14, ya yi nuni da cewa, matakin da gwamnatin Amurka ta dauka tabbas zai gurgunta tsarin samar da kayayyaki ga kamfanonin kasar Amurka, wanda hakan zai kara kudin da masu sayayya da ma kamfanoni na kasar suke biya.

ADVERTISEMENT

Amma me ya faru ga shugaba Biden har ya sauya matsayinsa a kan batun haraji a kan kayayyakin kasar Sin. Lallai bana ne za a gudanar da babban zabe a kasar Amurka, amma tattalin arzikin kasar na fama da matsalolin da suka hada da hauhawar farashin kaya, da babban gibin kudi da sauransu, don haka ma gwamnatin kasar kamar yadda ta saba yi, take kokarin karkata hankalin al’ummarta ga kasashen ketare. Yadda gwamnatin Biden ta dauki wannan mataki a daidai wannan lokaci, manufa ce ta siyasa, ta bayyana tsattsauran matsayinta a kan kasar Sin, don neman samun karin kuri’u a wasu jihohi marasa tabbaci.

A ganin Clark Packard, masani a cibiyar nazari ta Cato ta kasar Amurka, sabon matakin haraji da gwamnatin Biden ta dauka, ya sake dora burin siyasa da yake neman cimmawa a kan muradun kasar baki daya. A zahiri dai, idan an kwatanta da abin da yake neman cimmawa ta fannin siyasa, moriyar kasa da ta jama’a sam ba su da daraja, ballantana ma batun ingancin tsarin samar da kayayyaki na duniya, da farfadowar tattalin arzikin duniya, da‘yancin ciniki, da ma kokarin da kasa da kasa ke yi na tinkarar sauyin yanayi.

LABARAI MASU NASABA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Duk da haka, daukar matakan da ba su dace ba na dakile kamfanonin wasu kasashe, ba kawai zai lalata moriyar kamfanoni da masu sayayya na kasar ba ne, har ma zai lalata bunkasuwar masana’antu masu nasaba na kasar ita kan ta. Yadda ‘yan siyasar kasar suke iya kokarin cin babban zabe, amma suna zubar da kimar kasar a idon duniya, kuma zai haifar musu da karin matsaloli a cikin gida. (Mai Zane:Mustapha Bulama)

Trump
CGTN Hausa
+ postsBio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN: Fasahohin Zamani Sun Habaka Ayyuka Yayin Da Tsarin Cin Moriya Tare Ya Yi Fintinkau

MASU ALAKA

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu
Daga Birnin Sin

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
Next Post
Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

Karin Matakan Kariyar Cinikayya Na Amurka: “Kaikayi Zai Koma Kan Mashekiya”

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Gaza Wajen Magance Matsalar Tsaro A Nijeriya — Atiku

Atiku Ya Soki Tsare El-Rufai, Ya Ce Sharuɗan Belinsa Sun Yi Tsauri

June 24, 2026
Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

Trump Ne Zai Jagoranci Bayar Da Kofin Duniya A Wasan Ƙarshe – Infantino

June 24, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

’Yansanda Sun Kama Wani Mutum da Harsasai 174 A Nasarawa

June 24, 2026
Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

Sojoji Sun Kama Ɗan Fashi Da Makami A Taraba

June 24, 2026
An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.