• English
  • Business News
Saturday, September 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Talauci Zuwa Wadata: Kasar Sin Na Son Taimakawa Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
11 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Daga Talauci Zuwa Wadata: Kasar Sin Na Son Taimakawa Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A ranar 25 ga Fabrairun 2021 ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin ta samu cikakkiyar nasarar kawar da fatara. Yayin da aka fitar da mazauna karkara miliyan 98.99 na karshe daga kangin talauci. Wannan gagarumar nasara ba wai kawai ta taimaka wajen cimma muradun karni na Majalisar Dinkin Duniya ba, har ma da baiwa kasar damar cimma burin farko na ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya na “kawo karshen talauci a duk fadin kasar”, shekaru 10 kafin lokacin da aka tsara.

 

A shekarar 2021, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta kafa cibiyoyin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka na yin musayar fasahohin aikin gona na zamani, domin inganta zamanantar da aikin gona a nahiyar Afirka. Bayan shekaru uku, wato a wannan shekara ta 2024, shugaba Xi ya kara bayyana cewa, za a aiwatar da ayyukan hadin gwiwa guda 10 a cikin shekaru uku masu zuwa, wadanda suka shafi fannoni daban-daban da suka hada da ilmantar da juna tsakanin al’ummomi, da ci gaban cinikayya, da hadin gwiwar sassan masana’antu, da dai sauransu. Bugu da kari, an karfafa gwiwar cibiyoyi da kamfanoni na kasar Sin da su raya kauyukan gwaji game da ci gaban aikin gona da kawar da fatara a Afirka, tare da tallafawa shirin “Kamfanoni dari a kauyuka dubu” da hadin gwiwar kamfanonin kasar Sin a Afirka suka kaddamar don gudanar da ayyukan kyautata zamantakewar kamfanoni.

  • WHO Za Ta Kwashe Mata Da Kananan Yaran Gaza 1,000, Zuwa Turai Don Kula Da Lafiyarsu
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Ingiza Bude Kofa A Matsayin Koli Domin Cimma Nasarar Sauye Sauye Da Samar Da Ci Gaba

A karkashin shirin rage fatara da bunkasa aikin gona kuwa, kasar Sin ta kaddamar da ayyukan kawar da fatara da kuma ayyukan noma guda 47, wadanda ke ba da taimakon fasaha ga Malawi, Burundi da Cote d’Ivoire. Tare da kusan ma’aikatan noma 9,000 da kwararru a fannin noma 500 da aka aika zuwa Afirka, shirin ya amfanar da kananan manoman Afirka sama da miliyan daya, wanda ya taimaka wa nahiyar wajen samun fasahohin noma na zamani.

 

Labarai Masu Nasaba

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

A ranar 17 ga Oktoban shekarar 2024 ne aka yi bikin ranar yaki da fatara ta kasar Sin karo na 10, wacce ta zo daidai da ranar kawar da talauci na duniya karo na 32. Tare da samun goyon bayan sama da kashi daya bisa uku na al’ummar duniya da Sin da Afirka ke wakilta, da jajircewa daga gwamnatocinsu, hadin gwiwar Sin da Afirka kan kawar da fatara zai yi tasiri sosai a kokarin da ake yi na kawar da talauci a duniya. (Mohammed Yahaya)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

WHO Za Ta Kwashe Mata Da Kananan Yaran Gaza 1,000, Zuwa Turai Don Kula Da Lafiyarsu

Next Post

EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

Related

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

10 hours ago
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI
Daga Birnin Sin

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

11 hours ago
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon
Daga Birnin Sin

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

12 hours ago
Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Farin Cikin Ganin Kamfanoni Suna Gudanar Da Shawarwarin Kasuwanci Da Kyau Bisa Ka’idojin Kasuwa

13 hours ago
Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Yi Alkawarin Bayar Da Sabuwar Gudummawa Dangane Da Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya

14 hours ago
Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang
Daga Birnin Sin

Membobin Tawagar Koli Ta Sin Sun Ziyarci Jami’ai Da Gidajen Al’umma A Yankunan Jihar Xinjiang

15 hours ago
Next Post
EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

September 27, 2025
Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

September 27, 2025
Yadda Na Kawo Karshen Yajin Aikin ASUU Cikin Kwana Daya – Jonathan

Lalacewar Tsarin Zabe Babbar Barazana Ce Ga Dorewar Dimokuradiyyar Afirka — Jonathan

September 27, 2025
Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka

September 26, 2025
2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

2027: Abubuwan Da Jam’iyyun Siyasar Nijeriya Ke Tsammanin Samu Daga Sabon Shugaban INEC

September 26, 2025
Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

Jerin Tattaunawa Ta Musamman Da CMG Ya Gudanar Sun Maida Hankali Kan GGI

September 26, 2025
’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

’Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi A Kaduna, Sun Ƙwato Bindiga Da Wayoyi

September 26, 2025
Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

September 26, 2025
A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

A Karo Na Hudu ’Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Sun Yi Nasarar Kammala Ayyukansu A Wajen Kumbon

September 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.