ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Talauci Zuwa Wadata: Kasar Sin Na Son Taimakawa Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
1 year ago
Afirka

A ranar 25 ga Fabrairun 2021 ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin ta samu cikakkiyar nasarar kawar da fatara. Yayin da aka fitar da mazauna karkara miliyan 98.99 na karshe daga kangin talauci. Wannan gagarumar nasara ba wai kawai ta taimaka wajen cimma muradun karni na Majalisar Dinkin Duniya ba, har ma da baiwa kasar damar cimma burin farko na ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya na “kawo karshen talauci a duk fadin kasar”, shekaru 10 kafin lokacin da aka tsara.

 

A shekarar 2021, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta kafa cibiyoyin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka na yin musayar fasahohin aikin gona na zamani, domin inganta zamanantar da aikin gona a nahiyar Afirka. Bayan shekaru uku, wato a wannan shekara ta 2024, shugaba Xi ya kara bayyana cewa, za a aiwatar da ayyukan hadin gwiwa guda 10 a cikin shekaru uku masu zuwa, wadanda suka shafi fannoni daban-daban da suka hada da ilmantar da juna tsakanin al’ummomi, da ci gaban cinikayya, da hadin gwiwar sassan masana’antu, da dai sauransu. Bugu da kari, an karfafa gwiwar cibiyoyi da kamfanoni na kasar Sin da su raya kauyukan gwaji game da ci gaban aikin gona da kawar da fatara a Afirka, tare da tallafawa shirin “Kamfanoni dari a kauyuka dubu” da hadin gwiwar kamfanonin kasar Sin a Afirka suka kaddamar don gudanar da ayyukan kyautata zamantakewar kamfanoni.

ADVERTISEMENT
  • WHO Za Ta Kwashe Mata Da Kananan Yaran Gaza 1,000, Zuwa Turai Don Kula Da Lafiyarsu
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Ingiza Bude Kofa A Matsayin Koli Domin Cimma Nasarar Sauye Sauye Da Samar Da Ci Gaba

A karkashin shirin rage fatara da bunkasa aikin gona kuwa, kasar Sin ta kaddamar da ayyukan kawar da fatara da kuma ayyukan noma guda 47, wadanda ke ba da taimakon fasaha ga Malawi, Burundi da Cote d’Ivoire. Tare da kusan ma’aikatan noma 9,000 da kwararru a fannin noma 500 da aka aika zuwa Afirka, shirin ya amfanar da kananan manoman Afirka sama da miliyan daya, wanda ya taimaka wa nahiyar wajen samun fasahohin noma na zamani.

 

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

A ranar 17 ga Oktoban shekarar 2024 ne aka yi bikin ranar yaki da fatara ta kasar Sin karo na 10, wacce ta zo daidai da ranar kawar da talauci na duniya karo na 32. Tare da samun goyon bayan sama da kashi daya bisa uku na al’ummar duniya da Sin da Afirka ke wakilta, da jajircewa daga gwamnatocinsu, hadin gwiwar Sin da Afirka kan kawar da fatara zai yi tasiri sosai a kokarin da ake yi na kawar da talauci a duniya. (Mohammed Yahaya)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku
Daga Birnin Sin

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta
Daga Birnin Sin

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing
Daga Birnin Sin

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Next Post
EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

Ƴan Bindiga Sun Sace Mutane 14 A Wani Sabon Hari A Zamfara

November 16, 2025
Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

Babban Jirgin Ruwan Yaki Samfurin 076 Na Sin Ya Kammala Gwajinsa Na Farko A Teku

November 16, 2025
Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

Sin Ta Gargadi Philippines A Kan Ci Gaba Da Tayar Da Zaune Tsaye A Tekun Kudancinta

November 16, 2025
An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

An Yi Taron Karatun Sinanci Na Duniya Na 2025 A Beijing

November 16, 2025
Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

Ana Mai Da Hankali Kan Dabarun Kasar Sin A Fannin Tinkarar Sauyin Yanayin Duniya A Taron COP30

November 16, 2025
Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

Wata Ƙungiya Ta Fara Bin Digdigin Takardun Karatun Matawalle

November 16, 2025
DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.