ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daga Talauci Zuwa Wadata: Kasar Sin Na Son Taimakawa Afirka

by CGTN Hausa and Sulaiman
2 years ago
Afirka

A ranar 25 ga Fabrairun 2021 ne shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin ta samu cikakkiyar nasarar kawar da fatara. Yayin da aka fitar da mazauna karkara miliyan 98.99 na karshe daga kangin talauci. Wannan gagarumar nasara ba wai kawai ta taimaka wajen cimma muradun karni na Majalisar Dinkin Duniya ba, har ma da baiwa kasar damar cimma burin farko na ci gaba mai dorewa na Majalisar Dinkin Duniya na “kawo karshen talauci a duk fadin kasar”, shekaru 10 kafin lokacin da aka tsara.

 

A shekarar 2021, shugaban kasar Sin Xi Jinping ya sanar da cewa, kasar Sin za ta kafa cibiyoyin hadin gwiwa tsakanin Sin da Afirka na yin musayar fasahohin aikin gona na zamani, domin inganta zamanantar da aikin gona a nahiyar Afirka. Bayan shekaru uku, wato a wannan shekara ta 2024, shugaba Xi ya kara bayyana cewa, za a aiwatar da ayyukan hadin gwiwa guda 10 a cikin shekaru uku masu zuwa, wadanda suka shafi fannoni daban-daban da suka hada da ilmantar da juna tsakanin al’ummomi, da ci gaban cinikayya, da hadin gwiwar sassan masana’antu, da dai sauransu. Bugu da kari, an karfafa gwiwar cibiyoyi da kamfanoni na kasar Sin da su raya kauyukan gwaji game da ci gaban aikin gona da kawar da fatara a Afirka, tare da tallafawa shirin “Kamfanoni dari a kauyuka dubu” da hadin gwiwar kamfanonin kasar Sin a Afirka suka kaddamar don gudanar da ayyukan kyautata zamantakewar kamfanoni.

ADVERTISEMENT
  • WHO Za Ta Kwashe Mata Da Kananan Yaran Gaza 1,000, Zuwa Turai Don Kula Da Lafiyarsu
  • Xi Ya Jaddada Bukatar Ingiza Bude Kofa A Matsayin Koli Domin Cimma Nasarar Sauye Sauye Da Samar Da Ci Gaba

A karkashin shirin rage fatara da bunkasa aikin gona kuwa, kasar Sin ta kaddamar da ayyukan kawar da fatara da kuma ayyukan noma guda 47, wadanda ke ba da taimakon fasaha ga Malawi, Burundi da Cote d’Ivoire. Tare da kusan ma’aikatan noma 9,000 da kwararru a fannin noma 500 da aka aika zuwa Afirka, shirin ya amfanar da kananan manoman Afirka sama da miliyan daya, wanda ya taimaka wa nahiyar wajen samun fasahohin noma na zamani.

 

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

A ranar 17 ga Oktoban shekarar 2024 ne aka yi bikin ranar yaki da fatara ta kasar Sin karo na 10, wacce ta zo daidai da ranar kawar da talauci na duniya karo na 32. Tare da samun goyon bayan sama da kashi daya bisa uku na al’ummar duniya da Sin da Afirka ke wakilta, da jajircewa daga gwamnatocinsu, hadin gwiwar Sin da Afirka kan kawar da fatara zai yi tasiri sosai a kokarin da ake yi na kawar da talauci a duniya. (Mohammed Yahaya)

Afirka
CGTN Hausa
+ posts Bio
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
  • CGTN Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cgtn-hausa/
    Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa
Afirka
Sulaiman
+ posts Bio
  • Sulaiman
    Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara
  • Sulaiman
    Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
  • Sulaiman
    Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
  • Sulaiman
    ‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

MASU ALAKA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5
Daga Birnin Sin

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana
Daga Birnin Sin

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi
Daga Birnin Sin

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Next Post
EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

EFCC Ta Sake Gabatar Da Zarge-zarge 14 Kan Tsohon Gwamnan Kwara

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.