• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Sheikh Dahiru Bauchi Ya Gargadi Tinubu Kan Shirin Yakar Nijar

by Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
Sheikh Dahiru Bauchi Ya Gargadi  Tinubu Kan Shirin Yakar Nijar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yayin da wa’adin da kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afrika (ECOWAS), ta bai wa gwamnatin mulkin soja a Jamhuriyar Nijar, ya cika, fitaccen malamin Addinin Musulunci, Sheikh Dahiru Usman Bauchi, ya yi kira ga shugaba Bola Ahmed Tinubu da kada ya shiga yaki da kasar da ke makwabtaka da Nijeriya.

Shahararren malamin, wanda shi ne shugaban darikar Tijjaniya a Nijeriya, ya kuma bukaci majalisar dokokin kasar nan da kada ta amince da bukatar da shugaban kasar ya gabatar mata kan yakar Nijar.

  • AU, UN Da ECOWAS Sun Garzaya Nijar Don Tattaunawa Da Sojin Juyin Mulki
  • Kwatsam Ta Zayyana Ƙa’idoji Kafin Fara Shigo Da Kayayyaki Daga Iyakoki

A cewar dattijon malamin, maimakon su shiga yaki da kasar, kamata ya yi shugaba Tinubu da sauran shugabannin ECOWAS su tattauna da gwamnatin mulkin sojan Nijar da ta hambarar da shugaba Mohammed Bazoum.

Sheikh Bauchi ya bayyana haka ne a Bauchi a lokacin da yake zantawa da ‘yan jarida, inda ya kara da cewa Nijeriya da Jamhuriyar Nijar na da dadaddiyar alakar da ke bukatar kara karfafa ta.

“’Yan Nijeriya da Nijar sun dade a tare. Don haka akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tsunduma cikin harkokin diflomasiyya da nufin karfafa kyakkyawar alakar bunkasar tattalin arziki da ci gaban kasashen Afirka ta Yamma,” in ji shi.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

A cewar Shehin malamin, ya yi gargadin cewa, “yana da kyau a samar da wani kuduri na aminci don kaucewa zubar da jinin wadanda ba su ji ba ba su gani ba. ”

Daga nan sai ya bukaci sauran shugabannin Afirka ta Yamma da sauran masu ruwa da tsaki da su rungumi tattaunawa ta diflomasiya.

“Muna kira ga Shugaba Tinubu; Muna kuma kira ga Majalisar Dokoki ta kasa da dukkan shugabannin ECOWAS da masu ruwa da tsaki da kada su shiga da Nijar.

“Wannan kudirin ne na ceto rayukan wadanda ba su ji ba ba su gani ba, da kuma ceto mutane daga shiga cikin kuncin rayuwa,” in ji Sheikh Dahiru Bauchi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ECOWASJuyin MulkiNijarSheikh Dahiru BauchiTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

AU, UN Da ECOWAS Sun Garzaya Nijar Don Tattaunawa Da Sojin Juyin Mulki

Next Post

Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

Related

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

12 minutes ago
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

3 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

14 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

20 hours ago
Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?
Labarai

Shirin Ahmed Isa Na Brekete Family: Maslaha Ko Matsala?

21 hours ago
Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

22 hours ago
Next Post
Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

Faransa Ta Sharara Wa Morocco Ci 4-0 Ta Tsallaka Zuwa Kwata Fainal

LABARAI MASU NASABA

An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.