• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daidaiton Ƙasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Ƙasashen Duniya

by CMG Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Daidaiton Ƙasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Ƙasashen Duniya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

“Ya kamata a ƙara rungumar zaman lafiya da kwanciyar hankali a yayin da duniya ta tsunduma cikin rikice-rikice da rashin zaman lafiya,” waɗannan kalaman firaministan ƙasar Sin Li Qiang ne yayin da yake jawabi a wajen buɗe taron shekara-shekara na sabbin jagorori karo na 14, wanda aka fi sani da Davos na lokacin zafi, da ya gudana a ranakun 27 zuwa 29 na Yuni a Tianjin, ƙasar Sin. 

Taron da ya samu mahalarta kusan 1,500 daga fannoni daban daban kama daga ‘yan kasuwa, hukumomin gwamnatoci, ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa, da kuma malaman jami’o’I daga ƙasashen duniya kusan 100, kalaman Li saƙo ne zuwa ga al’ummar duniya da ke fuskantar rashin zaman lafiya da rikice-rikicen siyasa da bambance-bambancen aƙida suka haifar. Dunƙulewar kasuwancin duniya na fuskantar barazanar takunkumi na bai-ɗaya daga wasu ƙasashen yamma. Kana, yunƙurin samun haɗin gwiwar kimiyya ya samu cikas ta hanyar siyasa. Haka kuma yunƙurin yin musayar al’adu ya samu cikas ta rashin yarda, matsin lamba da rikice-rikicen siyasa.

  • Amfanin Juna Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

An amince da ƙasar Sin a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da suka fi cin gajiyar dunƙulewar duniya. Wannan gaskiya ne, tun bayan da aka yi gyare-gyare da bude ƙofa ga waje, ƙasar Sin ta samu nasarorin da ba a taba ganin irinta ba a harkokin mulki. Ta kawar da matsanancin talauci ta hanyar fitar da mutane kusan miliyan 800 daga kangin talauci. A tsakanin shekarar 2013 zuwa 2021, alkaluman bankin duniya sun nuna cewa, ƙasar Sin ta ba da gudummawar da ya kai kashi 38.6 cikin ɗari ga tattalin arzikin duniya. Haka kuma a lokacin da duniya ke cikin annobar COVID-19 da kuma bayan cutar, ƙasar Sin ta kasance jigon ci gaba mai ƙarfi yayin da sauran manyan ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziki ke fafutukar samar da ingantaccen ci gaban GDP.

Tattalin arzikin ƙasar Sin yana da matuƙar fa’ida. A yayin da tattalin arzikin duniya yake ƙaruwa da kashi 2.8 cikin ɗari a shekarar 2023. “Tattalin arzikin Sin ta kai kusan ninki biyu, a ƙalla fiye da kashi 4 cikin ɗari. Don haka, har yanzu tattalin arzikin ƙasar Sin na samun bunƙasuwa cikin sauri fiye da yawancin tattalin arzikin ƙasashen duniya.”

Ci gaba da zurfafa kasancewar kamfanonin ƙetare a kasuwannin kasar Sin, da zuba jari, shi ma ya kasance kyakkyawan aminci da cikakken kwarin gwiwar da ƙasashen duniya ke da shi game da bunƙasuwar tattalin arzikin ƙasar Sin.

Labarai Masu Nasaba

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Mummunar fahimtar da wasu kafafen yaɗa labarai na yammacin Turai ke yi ma tattalin arzikin ƙasar Sin ba zai yi tasiri ga yunƙurin dunƙulewar duniya waje guda da gano hanyoyin samun ci gaba da farfadowar tattalin arziki ba.

Ƙasar Sin ta kasance wata muhimmiyar madogara ga ci gaban tattalin arzikin duniya a cikin shekaru goma da suka gabata. Ƙasashen duniya dole su yi haɗin gwiwa tare da keta hazo don ciyar da tattalin arzikin duniya gaba.

Wannan dalili ne ya sanya yin adawa da ƙasar Sin tamkar ɓata lokaci ne. Kalmomi kamar “a guji” ko “a yi nesa” da ƙasar Sin sun zama sanannu a siyasar yammacin duniya, da aka yi amfani da su don ƙasashen yammacin duniya su ƙyamaci ƙasar Sin. Sai dai da’awarsu ba ta yi tasiri ba saboda ai “bindin raƙumi ya yi nesa da ƙasa”.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Amfanin Juna Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

Next Post

Bangaren Sin Ya Taya Saliyo Murnar Gudanar Da Babban Zabe Cikin Kwanciyar Hankali Da Lumana 

Related

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe
Daga Birnin Sin

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

14 hours ago
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

14 hours ago
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata
Daga Birnin Sin

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

16 hours ago
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4
Daga Birnin Sin

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

19 hours ago
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

21 hours ago
Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki
Daga Birnin Sin

Namibia Za Ta Karfafa Hulda Da Sin Yayin Baje Kolin Cinikayya Da Tattalin Arziki

22 hours ago
Next Post
Bangaren Sin Ya Taya Saliyo Murnar Gudanar Da Babban Zabe Cikin Kwanciyar Hankali Da Lumana 

Bangaren Sin Ya Taya Saliyo Murnar Gudanar Da Babban Zabe Cikin Kwanciyar Hankali Da Lumana 

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.