ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daidaiton Ƙasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Ƙasashen Duniya

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

“Ya kamata a ƙara rungumar zaman lafiya da kwanciyar hankali a yayin da duniya ta tsunduma cikin rikice-rikice da rashin zaman lafiya,” waɗannan kalaman firaministan ƙasar Sin Li Qiang ne yayin da yake jawabi a wajen buɗe taron shekara-shekara na sabbin jagorori karo na 14, wanda aka fi sani da Davos na lokacin zafi, da ya gudana a ranakun 27 zuwa 29 na Yuni a Tianjin, ƙasar Sin. 

Taron da ya samu mahalarta kusan 1,500 daga fannoni daban daban kama daga ‘yan kasuwa, hukumomin gwamnatoci, ƙungiyoyin ƙasa da ƙasa, da kuma malaman jami’o’I daga ƙasashen duniya kusan 100, kalaman Li saƙo ne zuwa ga al’ummar duniya da ke fuskantar rashin zaman lafiya da rikice-rikicen siyasa da bambance-bambancen aƙida suka haifar. Dunƙulewar kasuwancin duniya na fuskantar barazanar takunkumi na bai-ɗaya daga wasu ƙasashen yamma. Kana, yunƙurin samun haɗin gwiwar kimiyya ya samu cikas ta hanyar siyasa. Haka kuma yunƙurin yin musayar al’adu ya samu cikas ta rashin yarda, matsin lamba da rikice-rikicen siyasa.

  • Amfanin Juna Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

An amince da ƙasar Sin a matsayin ɗaya daga cikin ƙasashen da suka fi cin gajiyar dunƙulewar duniya. Wannan gaskiya ne, tun bayan da aka yi gyare-gyare da bude ƙofa ga waje, ƙasar Sin ta samu nasarorin da ba a taba ganin irinta ba a harkokin mulki. Ta kawar da matsanancin talauci ta hanyar fitar da mutane kusan miliyan 800 daga kangin talauci. A tsakanin shekarar 2013 zuwa 2021, alkaluman bankin duniya sun nuna cewa, ƙasar Sin ta ba da gudummawar da ya kai kashi 38.6 cikin ɗari ga tattalin arzikin duniya. Haka kuma a lokacin da duniya ke cikin annobar COVID-19 da kuma bayan cutar, ƙasar Sin ta kasance jigon ci gaba mai ƙarfi yayin da sauran manyan ƙasashe masu ƙarfin tattalin arziki ke fafutukar samar da ingantaccen ci gaban GDP.

ADVERTISEMENT

Tattalin arzikin ƙasar Sin yana da matuƙar fa’ida. A yayin da tattalin arzikin duniya yake ƙaruwa da kashi 2.8 cikin ɗari a shekarar 2023. “Tattalin arzikin Sin ta kai kusan ninki biyu, a ƙalla fiye da kashi 4 cikin ɗari. Don haka, har yanzu tattalin arzikin ƙasar Sin na samun bunƙasuwa cikin sauri fiye da yawancin tattalin arzikin ƙasashen duniya.”

Ci gaba da zurfafa kasancewar kamfanonin ƙetare a kasuwannin kasar Sin, da zuba jari, shi ma ya kasance kyakkyawan aminci da cikakken kwarin gwiwar da ƙasashen duniya ke da shi game da bunƙasuwar tattalin arzikin ƙasar Sin.

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

Mummunar fahimtar da wasu kafafen yaɗa labarai na yammacin Turai ke yi ma tattalin arzikin ƙasar Sin ba zai yi tasiri ga yunƙurin dunƙulewar duniya waje guda da gano hanyoyin samun ci gaba da farfadowar tattalin arziki ba.

Ƙasar Sin ta kasance wata muhimmiyar madogara ga ci gaban tattalin arzikin duniya a cikin shekaru goma da suka gabata. Ƙasashen duniya dole su yi haɗin gwiwa tare da keta hazo don ciyar da tattalin arzikin duniya gaba.

Wannan dalili ne ya sanya yin adawa da ƙasar Sin tamkar ɓata lokaci ne. Kalmomi kamar “a guji” ko “a yi nesa” da ƙasar Sin sun zama sanannu a siyasar yammacin duniya, da aka yi amfani da su don ƙasashen yammacin duniya su ƙyamaci ƙasar Sin. Sai dai da’awarsu ba ta yi tasiri ba saboda ai “bindin raƙumi ya yi nesa da ƙasa”.

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar
Daga Birnin Sin

Manufar Soke Haraji Ga Kasashen Afirka Ta Sin Ta Samar Da Sabbin Damammaki Ga Nahiyar

June 12, 2026
Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”
Daga Birnin Sin

Zhang Guoqing Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Na “Hadin Kai Don Bunkasa Tattalin Arzikin Duniya”

June 12, 2026
Next Post
Bangaren Sin Ya Taya Saliyo Murnar Gudanar Da Babban Zabe Cikin Kwanciyar Hankali Da Lumana 

Bangaren Sin Ya Taya Saliyo Murnar Gudanar Da Babban Zabe Cikin Kwanciyar Hankali Da Lumana 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.