ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Amfanin Juna Shi Ne Tushen Hadin Gwiwar Afirka Da Sin

by CMG Hausa
3 years ago
Sin

Kowa na cewa yanayin tattalin arzikin duniya ba shi da kyau yanzu, amma idan ka halarci taron baje kolin tattalin arziki da ciniki na Sin da Afirka, da ya gudana a birnin Changsha na kasar Sin a kwanakin baya, to, za ka ce kamar maganar ba ta yi daidai ba.

Saboda duk wani mutum da ya halarci taron ya ji mamakin yadda yanayin bikin ke da armashi, inda ake samun cunkuson mutane matuka. Alkaluman da aka gabatar bayan rufe taron baje kolin a jiya sun nuna cewa, cikin wa’adin taron na kwanaki 4, an nuna nau’ikan kayayyaki kimanin 1600 na wasu kasashe 29 dake nahiyar Afirka, inda aka samu mutane fiye da dubu 100 da suka halarci taron baje kolin, tare da kulla yarjeniyoyi 120, wadanda darajarsu ta kai dalar Amurka biliyan 10.3.

  • Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba A Fannin Raya Jiragen Masu Matukar Saurin Tafiya 

Abun da ya fi burge ni a wajen taron baje kolin na wannan karo, shi ne yadda aka nuna dimbin kayayyakin amfanin gonan kasashen Afirka, irinsu kifaye na kasar Madagascar, da man zaitun na kasar Aljeriya, da tattasai na kasar Malawi, da dai sauransu. Kana wani nau’in ganyen shayi mai launin jar galura na kasar Kenya ya samu karbuwa sosai, saboda yadda yake kunshe da sinadarai masu gina jiki. Inda aka sayar da ganyen na ton 2, a cikin ranar farko da aka gudanar da bikin.

ADVERTISEMENT

Ban da amfanin gona, an samu damar nuna wasu kayayyaki masu daraja kirar kasashen Afirka, irinsu tufafi, da lemu iri-iri, da kayan kwalliya na shafe-shafe, da dai sauransu, don neman shigar da su cikin kasuwannin kasar Sin. Cikinsu har da jakunkuna da tufafi masu kyan gani da wani saurayi dan kasar Zambia mai suna Kabaso ya kirkiro, wadanda suke da salon musamman na Afirka. A cewarsa, ya halarci taron baje kolin ne don yin bincike kan yanayin kasuwannin Sin, don neman sayar da kayayyakinsa ga karin jama’ar kasar.

Cikin abubuwan da aka nuna a wajen taron baje kolin, har da dandali na ciniki. Inda wani shafin yanar gizo mai taken Kilimall yake taimakawa sayar da kayayyakin Sin zuwa kasashen Afirka, gami da shigar da kayayyakin kirar kasashen Afirka cikin kasar Sin. Zuwa yanzu shafin nan ya sayar da kayayyaki na kimanin nau’ika miliyan 1 ga mutane fiye da miliyan 10, inda ta samar da guraben aikin yi fiye da 5000 a kasar Kenya kacal.

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Sa’an nan ban da bikin baje koli, an gudanar da wasu bukukuwa kimanin 40 a gefen taron, tare da samar da sakamako mai gamsarwa. Misali, a wajen taron dandalin tattaunawar kasar Sin da kasashen Afirka ta fuskar kiwon lafiya da yin amfani da ganye wajen kare lafiyar jiki, bangarorin Sin da Afirka sun yi alkawarin daidaita ka’idojinsu na tantance ingancin kayayyaki a kwastam don magance yaduwar cutuka, ta yadda za a iya shigar da kayayyaki amfanin gonan kasashen Afirka cikin kasuwannin Sin cikin karin sauki. Kana a wajen wani taro na karfafa ciniki a fannin kayayyakin masana’antu, wani yankin masana’antu na lardin Hunan na kasar Sin ya kulla yarjejeniya tare da hukumar fitar da kayayyaki ta kasar Kodibwa, inda suka samar da shirin hadin gwiwa don raya masana’antu.

Sai dai, abin tambaya shi ne, me ya sa ake iya gudanar da bukukuwan masu alaka da hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin tattalin arziki da ciniki cikin wani yanayi mai armashi, duk da wani yanayin tabarbarewa da tattalin arzikin duniya ke ciki? A ganina, zan iya yin amfani da maganar wani jami’in asusun Bill & Melinda Gates na kasar Amurka, mai suna Obai Khalifa, da ya fada wa ‘yan jarida a gefen taron baje koli na wannan karo, wajen amsa tambayar. A cewarsa, ya amince da yadda kasar Sin take kula da kasashen Afirka, inda ba ta kallon kasashen a matsayin nauyin da aka danka mata. Maimakon haka, kasar Sin ta dauki kasashen Afirka a matsayin abokan hulda, wadanda ake iya zuba musu jari don samun damar ci gaban tattalin arziki. Kana abubuwan da ya gani a wajen bikin baje kolin na wannan karo sun sa shi fahimtar huldar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, iri na amfanin juna.

Bayan da kayayyakin kasashen Afirka suka shiga cikin kasuwannin kasar Sin, masu samar da su dake kasashen Afirka za su samu karin kudin shiga, yayin da Sinawa za su samu damar more wadannan kayayyaki. Kana a lokacin da kamfanonin kasar Sin ke gudanar da wasu ayyuka a kasashen Afirka, lamarin zai ciyar da tattalin arzikin kasashen Afirka gaba, gami da haifarwa kamfanonin da riba. Dalilin yadda ake tsayawa kan manufar daidai-wa-daida da amfanin juna, ya sa hadin gwiwar Sin da Afirka a fannin tattalin arziki da ciniki ke dinga samun ci gaba, inda ake ba da gudummuwa ga kokarin kawar da wani yanayi na rashin tabbas a duniyarmu.

Sin
CMG Hausa
+ postsBio
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugabannin Kasashen Duniya Sun Yi Wa Sin Fatan Alheri A Sabuwar Shekara
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    San Francisco sabon mafarin hadin gwiwar Sin da Amurka ne
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Xi Ya Halarci Kwaya-Kwaryan Taron Shugabannin Mambobin APEC
  • CMG Hausa
    https://hausa.leadership.ng/author/cmg-hausa/
    Shugaban Kasar Sin Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Jagororin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

MASU ALAKA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya
Daga Birnin Sin

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026
Daga Birnin Sin

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”
Daga Birnin Sin

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Next Post
Daidaiton Ƙasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Ƙasashen Duniya

Daidaiton Ƙasar Sin Na Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Ci Gaban Ƙasashen Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.