• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
12 months ago
in Labarai
0
Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen malamin addinin musulunci da ke jihar Kano, Dakta Abdallah Gadon-Ƙaya ya yi amai ya lashe kan zargin da ya yi na cewa, wasu gungun masu auren jinsi da luwaɗi da maɗigo sun taru a jihar Bauchi domin sheƙe ayarsu a kwanakin baya.

 

Malamin ya fito ɓalo-ɓalo ya janye kalamansa tare da bai wa al’umma musamman musulmai haƙuri bisa furucin nasa.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Gadon-Kaya ya ce, bisa zurfafa bincike da gwamnatin jihar Bauchi da hukumomin tsaro suka yi, an tabbatar da cewa labarin da ya bayar ƙarya ce sam babu wani auren jinsi da aka taru daga jihohi domin yinsa a jihar Bauchi.

 

Labarai Masu Nasaba

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Idan za a tuna dai malamin ya taɓa shelanta wa duniya cewa, wani mutumi ya kirasa ya tabbatar masa da cewa, ana auren jinsi da luwaɗi da maɗigo a wani otel da ke jihar Bauchi. Malamin har ya ce yana da hujja da sunan otel ɗin kuma zai iya bayarwa idan aka nema.

 

Sai dai bayan da gwamnatin jihar Bauchi ta hannun hukumar Shari’a da ta nemi malamin domin ya zo ya gabatar mata da hujjojin nasa da kuma inda abun ya faru sai ya janye kalaman nasa.

 

Kan hakan ne malamin ya fito cikin wani faifayin bidiyo mai tsawon mintuna fiye da biyar ya na bai wa gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad da jami’an gwamnatin da hukumomin tsaro haƙuri bisa bayanin da ya fitar da ya tada hankalin jama’a da daman gaske.

 

Ya ce: “A satukan da suka gabata, akwai bayanin da na yi a kan labari da wani bawan Allah ya ba ni a kan faruwar wani taron auren jinsi a jihar Bauchi. Na ce ya kirani ya bani bayani cewa ga abun da ke faruwa cewa a yi wa’azi a faɗakar kuma a yi bincike.

 

“To, mun yi wannan maganar kuma maganar ta yaɗu kuma muka ce a bincika hukuma ta ɗauki mataki. Hukuma ta bincika, jami’an tsaro sun bincika babu wannan auren jinsin kuma ba a yi shi ba a jihar Bauchi.”

 

Ya ce suna godiya wa Allah bisan rashin faruwar hakan,  domin a cewarsa, hakan ma alkairi ne domin ba a samu faruwar ɓarnar ba.

 

Ya jinjina wa irin ƙoƙarin da jami’an tsaro da gwamnatin jihar Bauchi suka yi wajen bincikawa sosai har suka tabbatar da babu faruwar wannan labarin kwata-kwata.

 

Ya nuna cewa, a sakamakon kalaman nasa, rayukan dubban mutane sun ɓaci musamman wadanda suke kishin musulunci a ko’ina suke.

 

“Don haka, muna amfani da wannan damar tun da bincike ya tabbatar da ba a yi wannan abun ba, muna bada haƙuri ga duk wanda wannan abun ya shafe shi tun daga kan mai girma gwamna a matsayinsa na uba kuma jagora a wannan jihar da sauran muƙarrabansa da na kusa da shi, da jami’an tsaro da dukkan sauran al’umma baki daya.

 

“Mu yi haƙuri dukkanmu. Saboda ita da’awar haka ta gada wani lokacin za a iya faɗan wani abun wani lokacin ya zama haka ne wani lokacin ya zama ba haka ba ne, to daman ba fata muke abun ya faru ba. Allah ya bai wa kowa haƙuri baki ɗayanmu, Allah ya sa muma mu dace.

 

“Allah shi ne shaida ba mun yi wannan abun saboda cin zarafi ko ɓata wani ko kuma cin mutuncin wani, kwata-kwata babu wannan a tare da mu. Wallahi kishin jihar ce. Ni ɗan Bauchi ne, halastaccen ɗan Bauchi. Zan iya bayar da duk abun da na mallaka da rayuwata don na kare wannan jihar tawa na taimaki addini na taimaki da’awa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren Jinsi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

Next Post

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Related

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

50 minutes ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

1 hour ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

2 hours ago
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur
Manyan Labarai

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

2 hours ago
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya
Manyan Labarai

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

3 hours ago
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

5 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

LABARAI MASU NASABA

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

Ƙungiyar Ƙwadago Ta Ba Gwamnati Wa’adin Kwana 14 Ta Janye Sabon Harajin Man Fetur

September 12, 2025
Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

Likitoci Masu Neman Ƙwarewa Sun Fara Yajin Aikin Ƙasa A Nijeriya

September 12, 2025
Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.