• English
  • Business News
Thursday, June 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
9 months ago
in Labarai
0
Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen malamin addinin musulunci da ke jihar Kano, Dakta Abdallah Gadon-Ƙaya ya yi amai ya lashe kan zargin da ya yi na cewa, wasu gungun masu auren jinsi da luwaɗi da maɗigo sun taru a jihar Bauchi domin sheƙe ayarsu a kwanakin baya.

 

Malamin ya fito ɓalo-ɓalo ya janye kalamansa tare da bai wa al’umma musamman musulmai haƙuri bisa furucin nasa.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Gadon-Kaya ya ce, bisa zurfafa bincike da gwamnatin jihar Bauchi da hukumomin tsaro suka yi, an tabbatar da cewa labarin da ya bayar ƙarya ce sam babu wani auren jinsi da aka taru daga jihohi domin yinsa a jihar Bauchi.

 

Labarai Masu Nasaba

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

Idan za a tuna dai malamin ya taɓa shelanta wa duniya cewa, wani mutumi ya kirasa ya tabbatar masa da cewa, ana auren jinsi da luwaɗi da maɗigo a wani otel da ke jihar Bauchi. Malamin har ya ce yana da hujja da sunan otel ɗin kuma zai iya bayarwa idan aka nema.

 

Sai dai bayan da gwamnatin jihar Bauchi ta hannun hukumar Shari’a da ta nemi malamin domin ya zo ya gabatar mata da hujjojin nasa da kuma inda abun ya faru sai ya janye kalaman nasa.

 

Kan hakan ne malamin ya fito cikin wani faifayin bidiyo mai tsawon mintuna fiye da biyar ya na bai wa gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad da jami’an gwamnatin da hukumomin tsaro haƙuri bisa bayanin da ya fitar da ya tada hankalin jama’a da daman gaske.

 

Ya ce: “A satukan da suka gabata, akwai bayanin da na yi a kan labari da wani bawan Allah ya ba ni a kan faruwar wani taron auren jinsi a jihar Bauchi. Na ce ya kirani ya bani bayani cewa ga abun da ke faruwa cewa a yi wa’azi a faɗakar kuma a yi bincike.

 

“To, mun yi wannan maganar kuma maganar ta yaɗu kuma muka ce a bincika hukuma ta ɗauki mataki. Hukuma ta bincika, jami’an tsaro sun bincika babu wannan auren jinsin kuma ba a yi shi ba a jihar Bauchi.”

 

Ya ce suna godiya wa Allah bisan rashin faruwar hakan,  domin a cewarsa, hakan ma alkairi ne domin ba a samu faruwar ɓarnar ba.

 

Ya jinjina wa irin ƙoƙarin da jami’an tsaro da gwamnatin jihar Bauchi suka yi wajen bincikawa sosai har suka tabbatar da babu faruwar wannan labarin kwata-kwata.

 

Ya nuna cewa, a sakamakon kalaman nasa, rayukan dubban mutane sun ɓaci musamman wadanda suke kishin musulunci a ko’ina suke.

 

“Don haka, muna amfani da wannan damar tun da bincike ya tabbatar da ba a yi wannan abun ba, muna bada haƙuri ga duk wanda wannan abun ya shafe shi tun daga kan mai girma gwamna a matsayinsa na uba kuma jagora a wannan jihar da sauran muƙarrabansa da na kusa da shi, da jami’an tsaro da dukkan sauran al’umma baki daya.

 

“Mu yi haƙuri dukkanmu. Saboda ita da’awar haka ta gada wani lokacin za a iya faɗan wani abun wani lokacin ya zama haka ne wani lokacin ya zama ba haka ba ne, to daman ba fata muke abun ya faru ba. Allah ya bai wa kowa haƙuri baki ɗayanmu, Allah ya sa muma mu dace.

 

“Allah shi ne shaida ba mun yi wannan abun saboda cin zarafi ko ɓata wani ko kuma cin mutuncin wani, kwata-kwata babu wannan a tare da mu. Wallahi kishin jihar ce. Ni ɗan Bauchi ne, halastaccen ɗan Bauchi. Zan iya bayar da duk abun da na mallaka da rayuwata don na kare wannan jihar tawa na taimaki addini na taimaki da’awa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren Jinsi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

Next Post

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Related

Kawayen amarya
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

2 hours ago
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna
Labarai

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

4 hours ago
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

6 hours ago
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC
Labarai

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

15 hours ago
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya
Labarai

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

15 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

16 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

LABARAI MASU NASABA

Kawayen amarya

Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Iko Da Jagorancin Ƙaramar Hukuma A Katsina

June 26, 2025
An Damke Basarake Da Wasu Mutum 10 Bisa Zargin Hada Baki Da ‘Yan Bindiga A Kudancin Kaduna

Musayar Wuta Tsakanin Sojoji Da ‘Yan Bindiga Ta Ci Rayuka Da Dama A Jihar Neja

June 26, 2025
Tinubu

Tinubu Zai Rattaba Hannu Kan Kudirorin Sauya Fasalin Haraji 4 A Yau Alhamis 

June 26, 2025
Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

Cristiano Ronaldo Na Shirin Tsawaita Kwantiraginsa A Kungiyar Al-Nassr

June 25, 2025
Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

Ni Ne Na Kai Kaina ga Hukumar EFCC, In Ji Tsohon Jami’in NNPC

June 25, 2025
Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

Shugabannin Sin Da Mozamqiue Sun Mikawa Juna Sakon Taya Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya

June 25, 2025
MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

MSS: Neman Sinawa ‘Yan Leken Asiri Da CIA Ta Yi Tamkar Wasan Ban Dariya Ne

June 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Kano Ta Ayyana Ranar Alhamis Hutu Domin Murnar Sabuwar Shekarar Musulunci

June 25, 2025
Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

Gwamnan Jigawa Ya Kaddamar Da Rumbun Sauki Don Sayar Wa Ma’aikata Kayayyakin Abinci A Farashi Mai Rahusa A Sakkwato

June 25, 2025
Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

Sin Ta Sha Alwashin Rarraba Fasahohinta Na Ainihi Da Dabarunta Na Kirkire-Kirkire Tare Da Sauran Sassan Kasa Da Kasa

June 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.