• English
  • Business News
Sunday, July 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
10 months ago
in Labarai
0
Dakta Gadan-ƙaya Ya Bada Haƙuri Kan Zargin Auren Jinsi Da Ya Yi A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Fitaccen malamin addinin musulunci da ke jihar Kano, Dakta Abdallah Gadon-Ƙaya ya yi amai ya lashe kan zargin da ya yi na cewa, wasu gungun masu auren jinsi da luwaɗi da maɗigo sun taru a jihar Bauchi domin sheƙe ayarsu a kwanakin baya.

 

Malamin ya fito ɓalo-ɓalo ya janye kalamansa tare da bai wa al’umma musamman musulmai haƙuri bisa furucin nasa.

  • Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato
  • Ambaliyar Ruwa Ta Katse Hanyar Maiduguri Zuwa Damboa

Gadon-Kaya ya ce, bisa zurfafa bincike da gwamnatin jihar Bauchi da hukumomin tsaro suka yi, an tabbatar da cewa labarin da ya bayar ƙarya ce sam babu wani auren jinsi da aka taru daga jihohi domin yinsa a jihar Bauchi.

 

Labarai Masu Nasaba

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Idan za a tuna dai malamin ya taɓa shelanta wa duniya cewa, wani mutumi ya kirasa ya tabbatar masa da cewa, ana auren jinsi da luwaɗi da maɗigo a wani otel da ke jihar Bauchi. Malamin har ya ce yana da hujja da sunan otel ɗin kuma zai iya bayarwa idan aka nema.

 

Sai dai bayan da gwamnatin jihar Bauchi ta hannun hukumar Shari’a da ta nemi malamin domin ya zo ya gabatar mata da hujjojin nasa da kuma inda abun ya faru sai ya janye kalaman nasa.

 

Kan hakan ne malamin ya fito cikin wani faifayin bidiyo mai tsawon mintuna fiye da biyar ya na bai wa gwamnan jihar Bauchi, Bala Muhammad da jami’an gwamnatin da hukumomin tsaro haƙuri bisa bayanin da ya fitar da ya tada hankalin jama’a da daman gaske.

 

Ya ce: “A satukan da suka gabata, akwai bayanin da na yi a kan labari da wani bawan Allah ya ba ni a kan faruwar wani taron auren jinsi a jihar Bauchi. Na ce ya kirani ya bani bayani cewa ga abun da ke faruwa cewa a yi wa’azi a faɗakar kuma a yi bincike.

 

“To, mun yi wannan maganar kuma maganar ta yaɗu kuma muka ce a bincika hukuma ta ɗauki mataki. Hukuma ta bincika, jami’an tsaro sun bincika babu wannan auren jinsin kuma ba a yi shi ba a jihar Bauchi.”

 

Ya ce suna godiya wa Allah bisan rashin faruwar hakan,  domin a cewarsa, hakan ma alkairi ne domin ba a samu faruwar ɓarnar ba.

 

Ya jinjina wa irin ƙoƙarin da jami’an tsaro da gwamnatin jihar Bauchi suka yi wajen bincikawa sosai har suka tabbatar da babu faruwar wannan labarin kwata-kwata.

 

Ya nuna cewa, a sakamakon kalaman nasa, rayukan dubban mutane sun ɓaci musamman wadanda suke kishin musulunci a ko’ina suke.

 

“Don haka, muna amfani da wannan damar tun da bincike ya tabbatar da ba a yi wannan abun ba, muna bada haƙuri ga duk wanda wannan abun ya shafe shi tun daga kan mai girma gwamna a matsayinsa na uba kuma jagora a wannan jihar da sauran muƙarrabansa da na kusa da shi, da jami’an tsaro da dukkan sauran al’umma baki daya.

 

“Mu yi haƙuri dukkanmu. Saboda ita da’awar haka ta gada wani lokacin za a iya faɗan wani abun wani lokacin ya zama haka ne wani lokacin ya zama ba haka ba ne, to daman ba fata muke abun ya faru ba. Allah ya bai wa kowa haƙuri baki ɗayanmu, Allah ya sa muma mu dace.

 

“Allah shi ne shaida ba mun yi wannan abun saboda cin zarafi ko ɓata wani ko kuma cin mutuncin wani, kwata-kwata babu wannan a tare da mu. Wallahi kishin jihar ce. Ni ɗan Bauchi ne, halastaccen ɗan Bauchi. Zan iya bayar da duk abun da na mallaka da rayuwata don na kare wannan jihar tawa na taimaki addini na taimaki da’awa.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Auren Jinsi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kwangilar Biliyan 30: PDP Ta Bukaci EFCC Ta Binciki Gwamnatin Sakkwato

Next Post

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Related

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace
Labarai

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

2 minutes ago
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 
Wasanni

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

9 hours ago
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta
Labarai

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

12 hours ago
Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson
Siyasa

Duk Da Ni Ɗan Adawa Ne Buhari Ya Hana A Murɗe Min Zaɓe — Dickson

14 hours ago
An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja
Manyan Labarai

An Kama Mutane 4 Da Ake Zargi Da Haƙar Ma’adanai Ba Bisa Ƙa’ida Ba A Neja

15 hours ago
‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki
Labarai

‘Yancin Gashin Kai: Ma’aikatan Kananan Hukumomi Sun Yi Barazanar Shiga Yajin Aiki

17 hours ago
Next Post
Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

Gwamnan Kano Ya Rushe Kantomomin Kananan Hukumomin Jihar Kano 44

LABARAI MASU NASABA

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

VON Zai Fara Watsa Shirye-Shirye Da Harshen Sinanci — Ndace

July 27, 2025
Yadda Ake Faten Acca

Yadda Ake Faten Acca

July 27, 2025
Hanyoyin Gyaran Gashi

Hanyoyin Gyaran Gashi

July 27, 2025
Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

Nijeriya Ta Lashe Gasar Kofin Nahiyar Afirika Ta Mata 

July 26, 2025
Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

Musuluntar Wata Ce Ya Ja Hankalina Shiga Fim – Sailuba Dadin Kowa

July 26, 2025
Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

Masanin Kimiyyar Na’ura Mai Kwakwalwa Robert Tarjan Ya Jinjinawa Dabarun Sin Na Ingiza Ilimin Kimiyya

July 26, 2025
Kasar Sin Na Tir Da Harin Isra’ila Kan Makarantu A Gaza Tare Da Kira Da A Dakatar Da Bude Wuta

Isra’ila Na Sanya Alamar Rusau A Dubban Gidajen Fararen Hula A Gaza

July 26, 2025
Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

Firaministan Sin Ya Halarci Taron Kasa Da Kasa Game Da Jagorancin AI

July 26, 2025
Auren jinsi

Natijojin Auren Dattijo Ga Budurwa

July 26, 2025
An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

An Yi Bikin Karbar Fitilar Gasar Wasannin Kasa Da Kasa Ta Shekarar 2025 A Chengdu

July 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.