• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?

by CGTN Hausa
1 year ago
in Ra'ayi Riga
0
Dala Biliyan 95! Shin Da Gaske Kasar Amurka Tana Da Karamci?
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kasar Amurka Joe Biden ya sa hannu a kan wani shirin dokar samar da gudummawa ga kasashen ketare da ya kunshi dala biliyan 95, bayan da majalisun dokokin kasar suka zartas da shi. An ce, daga cikinsa, za a ware gudummawar da ta kai biliyan 60.8 ga Ukraine da ma biliyan 26 ga Isra’ila, baya ga dala biliyan 8 da za a samar ga yankin Asiya da tekun Pasifik da sunan wai tabbatar da“tsaron yankin Indo-Pasifik”. Daga nan kuma, shirin dokar ya fara aiki a hukumance. Bayan da ya sa hannu a dokar, shugaba Biden ya bayyana cewa, za a fara jigilar makamai da kudinsu ya kai dala biliyan daya zuwa Ukraine cikin wasu sa’o’i kadan. 

Da yake amsa tambayoyin manema labarai game da zartas da shirin dokar da aka yi, shugaban majalisar wakilai ta kasar Amurka, Mike Johnson ya bayyana cewa, “Babu kwanciyar hankali a duniyarmu, wadda tamkar ma’ajiyar albarusai ce, don haka muka yi kokari, kuma ina ganin tarihi zai ba da amsa.” To, amma ko da gaske ne abin haka yake kamar yadda ‘yan siyasar Amurka irinsu Mr. Mike Johnson suka fada?

  • Kasar Sin Ta Shirya Harba Na’urar Binciken Wata Ta Chang’e-6 
  • Shugabannin Sin Da Tanzaniya Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 60 Da Kafuwar Huldar Diplomasiyyar Kasashen Su

Babu shakka, duniyarmu na fama da tashe-tashen hankali. Rikici na ci gaba a tsakanin Rasha da Ukraine sama da shekaru biyu bayan barkewarsa, ga kuma tabarbarewar rikici a tsakanin Palasdinu da Isra’ila, wanda har ya haifar da mummunan tasiri ga sauran kasashen shiyyar. Yake-yake sun haifar da munanan hasarorin rayuka da kuma matsalolin jin kai. A kan ce, babu wanda ya ci nasara a fagen yaki. Amma bayan fagen yaki, akwai kasar da ke cin kazamar riba. Bisa kididdigar da aka samar, an ce, gudummawar da Amurka ta samar wa Ukraine ta kai dala biliyan 43.7 tun bayan barkewar rikicin a shekarar 2022, sai kuma a watan Nuwamban bara, majalisun dokokin Amurka sun amince da samar da gudummawar soja da ta kai dala biliyan 14.3 ga Isra’ila. Amma a hakika, duk da cewa gudummawa ce ga kasashen ketare, amma akasarin kudaden sun shiga aljihun masu sayar da makamai na kasar ta Amurka ne. A wannan karo ma, daga cikin dala biliyan 60.8 da ta samar wa Ukraine, akwai dala biliyan 27.6 da aka ware musamman domin sayen makamai da tsarin kandagarkin makamai daga Amurka, kwatankwacin dala biliyan 9 ne kawai da aka ware wajen samar da gudummawar jin kai da farfado da tattalin arziki a kasar Ukraine.

Abin lura kuma shi ne, shirin dokar ta kuma tsara samar da dala biliyan 8.12 don “tinkarar matakan da babban yankin kasar Sin za ta dauka a yankin Indo-Pasifik”. Daga cikinsu kuwa, an ware dala biliyan 1.9 don samar da kayayyakin tsaro da ma hidimomi ga yankin Taiwan da ma sauran kawayen kasar Amurka da ke yankin. Babu shakka, hakan ya saba wa sanarwoyi guda uku da kasashen Sin da Amurka suka bayar cikin hadin gwiwa, kuma katsalanda ce a cikin harkokin gidan kasar Sin, wanda kuma ya isar da sakon da bai dace ba ga mahukuntan yankin Taiwan tare da tona mana asirin Amurka game da mugun burin da take son cimmawa a yankin Asiya da tekun Pasifik. Lallai Amurka ta yi ta kalubalantar kasar Sin a kan batun Taiwan da tekun kudancin kasar Sin, don tsananta sabani a yankin, ta yadda mahukuntan yankin Taiwan da ma sauran “kawayenta” na yankin za su ba ta hadin kai wajen cimma burinta.

Amurka na daukar kanta a matsayin kasar da ta fi samar da gudummawa ga kasashen ketare. Amma a hakika, kullum tana samar da gudummawa ce don habaka cimma moriyarta da kiyaye babakeren da ta kafa a duniya, wadda ta haifar da mummunan tasiri ga zaman lafiya da ci gaba a duniya.

Labarai Masu Nasaba

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

Kamar yadda Mr.Mike Johnson ya fada, “Babu kwanciyar hankali a duniya, wadda tamkar ma’ajiyar albarusai ce.” Sai dai abin da Amurka ke yi na cinna wuta ga albarusan. Gudummawar nan ta dala biliyan 95, ta sake shaida wa duniya ainihin abin da ke kunshe a cikin gudummawar da Amurka ke samarwa duniya.(Mai Zane:Mustapha Bulama)

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Attajiri Abdul Samad Rabiu Zai Karbi Ribar Dala Miliyan 79.4 Daga Kamfaninsa Na Abinci

Next Post

Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

Related

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba
Ra'ayi Riga

Tarihi: Mugunta Ba Za Ta Iya Lashe Adalci Ba

4 days ago
Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe
Ra'ayi Riga

Ci Gaban Sojojin Sin Yana Hidimar Manufar Zaman Lafiya A Ko Da Yaushe

1 week ago
Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa
Ra'ayi Riga

Kowa Ya Ci Zomo Ya Ci Gudu: Shekaru 80 Da Nasarar Sinawa A Kan Zalunci Da Danniyar Japanawa

1 week ago
Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 
Ra'ayi Riga

Kasar Sin Za Ta Ci Gaba Da Ba Da Gudummawarta Wajen Kiyaye Zaman Lafiya Da Ci Gaban Duniya 

1 week ago
Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya
Ra'ayi Riga

Sin: Bin Tafarki Na Gaskiya

1 week ago
Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya
Ra'ayi Riga

Kyakkyawan Fata Kan Nasarar Yaki Da Akidar Mulkin Danniya A Duniya

1 week ago
Next Post
Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

Unai Emery Zai Ci Gaba Da Zama A Aston Villa

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

Gwamnatin Tarayya Za Ta Inganta Muhimman Abubuwan More Rayuwa Don Ci Gaban Ƙasa

September 13, 2025
Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

Ambaliyar Ruwa Ta Yi Sanadiyyar Mutuwar Mutum Uku A Zariya

September 13, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido Ba

September 13, 2025
Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

Tsawon Hanyoyin Jiragen Kasa A Biranen Sin Ya Zama Na Farko A Duniya

September 12, 2025
Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

Tawagogin Sin Da Amurka Za Su Tattauna A Spaniya

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

Kamfanonin Kasashen Waje Za Su Ci Gaba Da Habaka Harkokinsu A Sin

September 12, 2025
Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.