• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Rungumar Sabuwar Dabarar Kiwo A Kano

by Abubakar Abba
12 months ago
Kaji

Wasu daga cikin masu kiwon Kajin gidan gona a Jihar Kano, sun fito da wata sabuwar dabara ta hada kai da wasu kananan masu kiwon Kajin gidan gona a jihar.

Masu kiwon, musamman wadanda ke kyankyashe ‘ya’yan Kajin kai tsaye da kuma wadanda ba kai tsaye suke kyankyashewa ba, na sayar da ‘yan tsakin da aka kyankayshe musu kwana daya da kyankyasa, wanda daga baya kuma bayan mako biyu ko uku, sai su koma wurin masu kananan kiwon da suka sayarwa, su sake sayen ‘yan tsakin, kafin su kammala girma.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Guda daga cikin masu kiwon Kajin a jihar, Malam Shehu Caji; ya sanar da cewa, rungumar wannnan sabuwar dabara ta zama dole, musamman don ganin sana’ar tasu ta ci gaba da dorewa.

A cewarsa, mun rungumi wannan sabuwar dabara ce; domin duba yadda ake ci gaba da samun hauhawar farashin abincin Kaji a fadin wannan kasa.

Shehu ya kara da cewa, a yanzu buhun abincinsu da ake fara ciyar da su mai nauyin kilo 25; ya kai Naira 20,700, sabanin Naira 10,000 da ake sayar da shi a shekarar da wuce.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

Ya ci gaba da cewa, rungumar wannan dabara; ko shakka babu ta zama dole, domin a hankali fannin yana kara mutuwa ne, inda ya sanar da cewa, akasarin kwararrun da suke a cikin sana’ar na da yakin cewa, tuni fannin ya riga ya mutu, wanda hakan ya sanya suka dakatar da sana’ar baki-daya.

A cewarsa, mai kiwon zai sayi ‘yan tsakin da aka kyankyashe a kwana daya, sai ya ci gaba da kiwata su har zuwa daga mako biyu zuwa uku, sai kuma ya sake mayar da su inda aka sayo su, sai su kuma su sake saye daga wurinka, ma’ana; kamar kana jujjuya saye da sayar da su ne.

Ya sanar da cewa, wannna dabara ita ce yanzu ake amfani da ita wannan fanni na kiwon Kajin gidan gona; wadda kuma ta na ci gaba da tafiyar da fannin, amma ga wanda ya rungume ta.

Kazalika, rahotannin sun bayyana cewa; akasarin manoma yanzu, sun rungumi wannan babbar dabara.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Sharhi Kan Noman Agwaluma A Nijeriya

October 18, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Ɓarayi 13 Tare Da Ƙwato Shanu 27 A Kaduna
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Jihar Taraba Ta Ayyana Yi Wa Kasuwannin Sayar Da Dabbobi 9 Garanbawul

October 18, 2025
Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI
Noma Da Kiwo

Dalilin Bankin AfDB Na Yin Hadaka Da WFP Da IFPRI

October 18, 2025
Next Post
Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Bukatar Kawo Karshen Mace-mace A Hanyoyinmu

LABARAI MASU NASABA

gaza

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

Duk Da Barazanar Tattalin Arzikin Duniya, Kasar Sin Ta Sanya Tabbaci Da Kwanciyar Hankali A Duniyarmu Mai Cike Da Ruɗani

October 28, 2025
Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

Ina Fatan Buga Kofin Duniya Na 2026 — Messi

October 28, 2025
Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
Kaji

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.