• English
  • Business News
Tuesday, June 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Rungumar Sabuwar Dabarar Kiwo A Kano

by Abubakar Abba
8 months ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilan Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Rungumar Sabuwar Dabarar Kiwo A Kano
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wasu daga cikin masu kiwon Kajin gidan gona a Jihar Kano, sun fito da wata sabuwar dabara ta hada kai da wasu kananan masu kiwon Kajin gidan gona a jihar.

Masu kiwon, musamman wadanda ke kyankyashe ‘ya’yan Kajin kai tsaye da kuma wadanda ba kai tsaye suke kyankyashewa ba, na sayar da ‘yan tsakin da aka kyankayshe musu kwana daya da kyankyasa, wanda daga baya kuma bayan mako biyu ko uku, sai su koma wurin masu kananan kiwon da suka sayarwa, su sake sayen ‘yan tsakin, kafin su kammala girma.

  • EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa
  • Shugabannin Sin Da UAE Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 40 Da Kafuwar Huldar Diflomasiyya Tsakaninsu

Guda daga cikin masu kiwon Kajin a jihar, Malam Shehu Caji; ya sanar da cewa, rungumar wannnan sabuwar dabara ta zama dole, musamman don ganin sana’ar tasu ta ci gaba da dorewa.

A cewarsa, mun rungumi wannan sabuwar dabara ce; domin duba yadda ake ci gaba da samun hauhawar farashin abincin Kaji a fadin wannan kasa.

Shehu ya kara da cewa, a yanzu buhun abincinsu da ake fara ciyar da su mai nauyin kilo 25; ya kai Naira 20,700, sabanin Naira 10,000 da ake sayar da shi a shekarar da wuce.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

Ya ci gaba da cewa, rungumar wannan dabara; ko shakka babu ta zama dole, domin a hankali fannin yana kara mutuwa ne, inda ya sanar da cewa, akasarin kwararrun da suke a cikin sana’ar na da yakin cewa, tuni fannin ya riga ya mutu, wanda hakan ya sanya suka dakatar da sana’ar baki-daya.

A cewarsa, mai kiwon zai sayi ‘yan tsakin da aka kyankyashe a kwana daya, sai ya ci gaba da kiwata su har zuwa daga mako biyu zuwa uku, sai kuma ya sake mayar da su inda aka sayo su, sai su kuma su sake saye daga wurinka, ma’ana; kamar kana jujjuya saye da sayar da su ne.

Ya sanar da cewa, wannna dabara ita ce yanzu ake amfani da ita wannan fanni na kiwon Kajin gidan gona; wadda kuma ta na ci gaba da tafiyar da fannin, amma ga wanda ya rungume ta.

Kazalika, rahotannin sun bayyana cewa; akasarin manoma yanzu, sun rungumi wannan babbar dabara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KajikanoKiwo
ShareTweetSendShare
Previous Post

AGF Ya Umarci Sauya Kundin Shari’ar Masu Zanga-Zanga Zuwa Ofishinsa

Next Post

Bukatar Kawo Karshen Mace-mace A Hanyoyinmu

Related

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

2 days ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Hikimar Yunƙurin Sake Farfaɗo Da Noman Filanten A Jihar Nasarawa

2 days ago
Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 
Noma Da Kiwo

Jigawa Za Ta Samar Da Kashi 25 Na Shinkafar Da Nijeriya Ke Bukata – Hon Abdurahman 

3 days ago
Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 
Noma Da Kiwo

Kin Biyan Bashi Daga Wasu Manoma Zai Kawo Cikas Ga Noman Shinkafa A Bana – Ɗan Madamin Samaru 

4 days ago
Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA
Noma Da Kiwo

Kudaden Da Ake Karba A Kogin Hadejia Jama’are Daga Hannun Manoma, Ba Haraji Ba Ne – HJRBDA

2 weeks ago
Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025
Noma Da Kiwo

Wani Gidan Gona A Jihar Ogun Zai Fitar Da Tarwada Ta Kimanin Naira Biliyan Shida A 2025

2 weeks ago
Next Post
Rikita-rikitar Aikin Hanyar Abuja Zuwa Kaduna…

Bukatar Kawo Karshen Mace-mace A Hanyoyinmu

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

Gwamnatin Zamfara Ta Ƙaryata Rahoton Karɓo Lamuni Da Wata Jarida Ta Yaɗa

June 24, 2025
Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

Kasar Sin Na Fatan Isra’ila Da Iran Za Su Tsagaita Bude Wuta Nan Bada Jimawa Ba

June 24, 2025
Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

Majalisa Ta Yi Allah-wadai Da Kashe Wasu Matafiya ‘Yan Kaduna 13 A Jihar Filato

June 24, 2025
Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

Al’ummun Afrika Da Sin Ba Za Su Taba Mantawa Da Gudunmuwar Tawagar Jami’an Lafiya Ta Sin Ba

June 24, 2025
Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

Barau Ya Nisanta Kansa Daga Kiraye-kirayen Ya Zama Mataimakin Tinubu A Zaben 2027

June 24, 2025
Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

Shugabannin PDP Sun Ziyarci INEC Kan Neman Sanin Ka’idojinta

June 24, 2025
Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

Sin Da Kasashen Musulmi Za Su Kara Zurfafa Dangantakarsu

June 24, 2025
Sabbin Ministoci

Majalisar Dattawa Ta Kara Tsawaita Aiwatar Da Ayyukan Kasafin Kudi Na 2024 Da Wata 6

June 24, 2025
Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

Nuna Karfin Tuwo Ba Zai Kawo Zaman Lafiya Ga Yankin Gabas Ta Tsakiya Ba

June 24, 2025
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

June 24, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.