ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, June 24, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
EFCC

Domin hana duk wani tirjiya daga gwamnonin jihohi, hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC) za ta fara bibiyan kudaden da ake tura wa kananan hukumomin kai tsaye nan da watan Nuwamba 2024.

Shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi na kasa, Hakeem Ambali ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta musamman da ya yi da manema labarai a ranar Lahadi da ta gabata.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Layuka A Gidajen Mai Za Su Ragu Idan ‘Yan Kasuwa Suka Fara Sayan Mai A Wajenmu – Dangote

Hakan ya kasance kamar yadda hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati ta tabbatar da aniyarta na sa ido sosai tare da bin diddigin yadda shugabannin kananan hukumomi ke kashe kudaden shiga daga asusun da gwamnatin tarayya ke warewa duk wata.

ADVERTISEMENT

Wannan sabon ci gaba ya nuna wani gagarumin sauyi na aiwatar da ikon mallakar kananan hukumomi kamar yadda kotun koli ta ba da umarni da kuma gabanin wa’adin ranar 31 ga Oktoba da aka sanya wa jihohi su gudanar da zaben shugabannin kananan hukumomi.

A watan Mayu ne gwamnatin tarayya ta shigar da kara a gaban kotun koli ta hannun babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi, inda ta shigar da kara domin kalubalantar ikon gwamnonin na karba da kuma hana kudaden da gwamnatin tarayya ke yi wa kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

Karar ta nemi hana gwamnonin jihohi rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da kafa kwamitocin riko.

Babban lauyan gwamnatin tarayya ya yi nuni da cewa kundin tsarin mulkin kasar nan ya ba da umarnin gudanar da zaben kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya.

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci da ke tabbatar da cin gashin kai na harkokin kudi na kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

Sai dai an samu jinkirin fara aiwatar da tsarin sakamakon dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi na tsawon watanni uku saboda damuwar da ta taso dangane da tasirinta na biyan albashi da kuma yadda za a iya gudanar da tsarin.

Har ila yau, a ranar 20 ga watan Agusta, gwamnatin tarayya ta kafa hadakar kwamitin ma’aikatu mai mambobi 10 don aiwatar da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomi.

Mambobin kwamitin sun hada da ministan kudi, Wale Edun; babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi SAN; ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Bagudu; Akanta-Janar na tarayya; Oluwatoyin Madein da gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Olayemi Cardoso.

Sauran sun hada da sakatare janar na ma’aikatar kudi ta tarayya, Misis Lydia Jafiya, shugaban hukumar kula da rarraba asusun gwamnatin tarayya, Mohammed Shehu, da wakilan gwamnonin jihohi da na kananan hukumomi.

Babban aikin kwamitin dai shi ne, tabbatar da ganin an bai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin cin gashin kansu, tare da ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata ba tare da tsangwama daga gwamnatocin jihohi ba.

Kwamitin wanda sakataren gwamnatin tarayya, George Akume ya jagoranta, ya kammala tare da mika aikinsa a ranar 13 ga watan Oktoba.

A ranar Talatar da ta gabata ne wani bincike da jaridar The PUNCH ta gudanar ya nuna cewa akalla kananan hukumomi 164 a jihohi takwas ne har yanzu ba su gudanar da zabe ba, kuma akwai yiwuwar gwamnatin tarayya ta kwace kason kamar yadda kotun koli ta zartar.

A halin yanzu dai, shugaban hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce hukumarsa za ta sanya ido a kan yadda ake gudanar da kasafin kudin daukacin kananan hukumomin kasar nan.

Olukoyede, a wata hira da aka buga a mujallar hukumar, wanda wakilinmu ya samu kwafinsa a ranar Lahadi, ya bayyana cewa hukumar EFCC za ta sanya ido kan yadda ake gudanar da kasafin kudin na dukkan kananan hukumomin kasar nan.

Ya koka da yadda gwamnatocin jihohi ke yin tasiri a kan albarkatun kananan hukumomin.

Shugaban EFCC ya ce hukumar ta fadada ayyukanta a fadin kasar nan. Ya kuma sha alwashin cewa duk wani jami’in karamar hukumar da ya karkatar da kudade za a kama shi kuma a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.

Shi ma shugaban kungiyar kananan hukumomi a Nijeriya, Aminu Kaita, ya tabbatar da cewa har yanzu ana ci gaba da rabon kason kudaden kananan hukumomin daga asusun tarayya.

Kaita ya shaida cewa, “Muna aiki tukuro. Rana ta karshe shi ne Oktoba, kuma bai wuce ba tukuna. Don haka muna aiki a kan hakan.”

EFCC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa

June 12, 2026
Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

June 12, 2026
Next Post
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

An Kashe Mutum 2, 8 Sun Jikkata Yayin Rikici A Bauchi

June 24, 2026
Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

Tsohon Shugaban APC Na Kebbi Ya Rasu A Hannun ’Yan Bindiga

June 24, 2026
Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

Ya Kamata Sin Da Birtaniya Su Yi Aiki Tare Don Ci Gaba Da Inganta Dangantakarsu

June 23, 2026
Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

Firaministan Sin Ya Jaddada Muhimmancin Kara Azamar Bunkasa Kirar Kayayyakin Aikin Masana’antu Na Zamani

June 23, 2026
Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

Gombe Ta Zabge Farashin Taki Da Kashi 50 Cikin 100

June 23, 2026
Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

Wang Yi Ya Gana Da Babban Sakataren Majalisar Tsaron Masar Da Ministan Fadar Gwamnatin Afirka Ta Kudu A Indiya

June 23, 2026
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

’Yansanda Sun Kama Mutane 57 Da Ake Zargi Da Ayyukan Ta’addanci A Adamawa

June 23, 2026
Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

Li Qiang Ya Gana Da Firaministan Kasar Guinea

June 23, 2026
Maniyyatan Nijeriya

Hajjin 2026: NAHCON Ta Kammala Jigilar Alhazan Nijeriya Daga Saudiyya

June 23, 2026
Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

Kamfanin Sin Ya Kammala Babban Aikin Samar Da Ruwa A Babban Birnin Nijeriya

June 23, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.