ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
EFCC

Domin hana duk wani tirjiya daga gwamnonin jihohi, hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC) za ta fara bibiyan kudaden da ake tura wa kananan hukumomin kai tsaye nan da watan Nuwamba 2024.

Shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi na kasa, Hakeem Ambali ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta musamman da ya yi da manema labarai a ranar Lahadi da ta gabata.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Layuka A Gidajen Mai Za Su Ragu Idan ‘Yan Kasuwa Suka Fara Sayan Mai A Wajenmu – Dangote

Hakan ya kasance kamar yadda hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati ta tabbatar da aniyarta na sa ido sosai tare da bin diddigin yadda shugabannin kananan hukumomi ke kashe kudaden shiga daga asusun da gwamnatin tarayya ke warewa duk wata.

ADVERTISEMENT

Wannan sabon ci gaba ya nuna wani gagarumin sauyi na aiwatar da ikon mallakar kananan hukumomi kamar yadda kotun koli ta ba da umarni da kuma gabanin wa’adin ranar 31 ga Oktoba da aka sanya wa jihohi su gudanar da zaben shugabannin kananan hukumomi.

A watan Mayu ne gwamnatin tarayya ta shigar da kara a gaban kotun koli ta hannun babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi, inda ta shigar da kara domin kalubalantar ikon gwamnonin na karba da kuma hana kudaden da gwamnatin tarayya ke yi wa kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Karar ta nemi hana gwamnonin jihohi rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da kafa kwamitocin riko.

Babban lauyan gwamnatin tarayya ya yi nuni da cewa kundin tsarin mulkin kasar nan ya ba da umarnin gudanar da zaben kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya.

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci da ke tabbatar da cin gashin kai na harkokin kudi na kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

Sai dai an samu jinkirin fara aiwatar da tsarin sakamakon dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi na tsawon watanni uku saboda damuwar da ta taso dangane da tasirinta na biyan albashi da kuma yadda za a iya gudanar da tsarin.

Har ila yau, a ranar 20 ga watan Agusta, gwamnatin tarayya ta kafa hadakar kwamitin ma’aikatu mai mambobi 10 don aiwatar da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomi.

Mambobin kwamitin sun hada da ministan kudi, Wale Edun; babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi SAN; ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Bagudu; Akanta-Janar na tarayya; Oluwatoyin Madein da gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Olayemi Cardoso.

Sauran sun hada da sakatare janar na ma’aikatar kudi ta tarayya, Misis Lydia Jafiya, shugaban hukumar kula da rarraba asusun gwamnatin tarayya, Mohammed Shehu, da wakilan gwamnonin jihohi da na kananan hukumomi.

Babban aikin kwamitin dai shi ne, tabbatar da ganin an bai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin cin gashin kansu, tare da ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata ba tare da tsangwama daga gwamnatocin jihohi ba.

Kwamitin wanda sakataren gwamnatin tarayya, George Akume ya jagoranta, ya kammala tare da mika aikinsa a ranar 13 ga watan Oktoba.

A ranar Talatar da ta gabata ne wani bincike da jaridar The PUNCH ta gudanar ya nuna cewa akalla kananan hukumomi 164 a jihohi takwas ne har yanzu ba su gudanar da zabe ba, kuma akwai yiwuwar gwamnatin tarayya ta kwace kason kamar yadda kotun koli ta zartar.

A halin yanzu dai, shugaban hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce hukumarsa za ta sanya ido a kan yadda ake gudanar da kasafin kudin daukacin kananan hukumomin kasar nan.

Olukoyede, a wata hira da aka buga a mujallar hukumar, wanda wakilinmu ya samu kwafinsa a ranar Lahadi, ya bayyana cewa hukumar EFCC za ta sanya ido kan yadda ake gudanar da kasafin kudin na dukkan kananan hukumomin kasar nan.

Ya koka da yadda gwamnatocin jihohi ke yin tasiri a kan albarkatun kananan hukumomin.

Shugaban EFCC ya ce hukumar ta fadada ayyukanta a fadin kasar nan. Ya kuma sha alwashin cewa duk wani jami’in karamar hukumar da ya karkatar da kudade za a kama shi kuma a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.

Shi ma shugaban kungiyar kananan hukumomi a Nijeriya, Aminu Kaita, ya tabbatar da cewa har yanzu ana ci gaba da rabon kason kudaden kananan hukumomin daga asusun tarayya.

Kaita ya shaida cewa, “Muna aiki tukuro. Rana ta karshe shi ne Oktoba, kuma bai wuce ba tukuna. Don haka muna aiki a kan hakan.”

EFCC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027

July 11, 2026
Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
Tambarin Dimokuradiyya

Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

July 11, 2026
makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Next Post
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.