ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

EFCC Za Ta Binciki Yadda Kudaden Kananan Hukumomi Ke Sulalewa

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
EFCC

Domin hana duk wani tirjiya daga gwamnonin jihohi, hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati (EFCC) za ta fara bibiyan kudaden da ake tura wa kananan hukumomin kai tsaye nan da watan Nuwamba 2024.

Shugaban kungiyar ma’aikatan kananan hukumomi na kasa, Hakeem Ambali ne ya bayyana hakan yayin wata tattaunawa ta musamman da ya yi da manema labarai a ranar Lahadi da ta gabata.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Layuka A Gidajen Mai Za Su Ragu Idan ‘Yan Kasuwa Suka Fara Sayan Mai A Wajenmu – Dangote

Hakan ya kasance kamar yadda hukumar yaki da yi wa tattalin arzikin kasa ta’annati ta tabbatar da aniyarta na sa ido sosai tare da bin diddigin yadda shugabannin kananan hukumomi ke kashe kudaden shiga daga asusun da gwamnatin tarayya ke warewa duk wata.

ADVERTISEMENT

Wannan sabon ci gaba ya nuna wani gagarumin sauyi na aiwatar da ikon mallakar kananan hukumomi kamar yadda kotun koli ta ba da umarni da kuma gabanin wa’adin ranar 31 ga Oktoba da aka sanya wa jihohi su gudanar da zaben shugabannin kananan hukumomi.

A watan Mayu ne gwamnatin tarayya ta shigar da kara a gaban kotun koli ta hannun babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi, inda ta shigar da kara domin kalubalantar ikon gwamnonin na karba da kuma hana kudaden da gwamnatin tarayya ke yi wa kananan hukumomi.

LABARAI MASU NASABA

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

Karar ta nemi hana gwamnonin jihohi rusa zababbun shugabannin kananan hukumomi tare da kafa kwamitocin riko.

Babban lauyan gwamnatin tarayya ya yi nuni da cewa kundin tsarin mulkin kasar nan ya ba da umarnin gudanar da zaben kananan hukumomi ta hanyar dimokuradiyya.

A ranar 11 ga Yuli, 2024, kotun koli ta zartar da hukunci da ke tabbatar da cin gashin kai na harkokin kudi na kananan hukumomi 774 da ke kasar nan.

Sai dai an samu jinkirin fara aiwatar da tsarin sakamakon dakatarwar da gwamnatin tarayya ta yi na tsawon watanni uku saboda damuwar da ta taso dangane da tasirinta na biyan albashi da kuma yadda za a iya gudanar da tsarin.

Har ila yau, a ranar 20 ga watan Agusta, gwamnatin tarayya ta kafa hadakar kwamitin ma’aikatu mai mambobi 10 don aiwatar da hukuncin da kotun koli ta yanke kan cin gashin kan kananan hukumomi.

Mambobin kwamitin sun hada da ministan kudi, Wale Edun; babban lauyan gwamnatin tarayya kuma ministan shari’a, Lateef Fagbemi SAN; ministan kasafin kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Abubakar Bagudu; Akanta-Janar na tarayya; Oluwatoyin Madein da gwamnan Babban Bankin Nijeriya, Olayemi Cardoso.

Sauran sun hada da sakatare janar na ma’aikatar kudi ta tarayya, Misis Lydia Jafiya, shugaban hukumar kula da rarraba asusun gwamnatin tarayya, Mohammed Shehu, da wakilan gwamnonin jihohi da na kananan hukumomi.

Babban aikin kwamitin dai shi ne, tabbatar da ganin an bai wa kananan hukumomi cikakken ‘yancin cin gashin kansu, tare da ba su damar gudanar da aiki yadda ya kamata ba tare da tsangwama daga gwamnatocin jihohi ba.

Kwamitin wanda sakataren gwamnatin tarayya, George Akume ya jagoranta, ya kammala tare da mika aikinsa a ranar 13 ga watan Oktoba.

A ranar Talatar da ta gabata ne wani bincike da jaridar The PUNCH ta gudanar ya nuna cewa akalla kananan hukumomi 164 a jihohi takwas ne har yanzu ba su gudanar da zabe ba, kuma akwai yiwuwar gwamnatin tarayya ta kwace kason kamar yadda kotun koli ta zartar.

A halin yanzu dai, shugaban hukumar EFCC, Ola Olukoyede, ya ce hukumarsa za ta sanya ido a kan yadda ake gudanar da kasafin kudin daukacin kananan hukumomin kasar nan.

Olukoyede, a wata hira da aka buga a mujallar hukumar, wanda wakilinmu ya samu kwafinsa a ranar Lahadi, ya bayyana cewa hukumar EFCC za ta sanya ido kan yadda ake gudanar da kasafin kudin na dukkan kananan hukumomin kasar nan.

Ya koka da yadda gwamnatocin jihohi ke yin tasiri a kan albarkatun kananan hukumomin.

Shugaban EFCC ya ce hukumar ta fadada ayyukanta a fadin kasar nan. Ya kuma sha alwashin cewa duk wani jami’in karamar hukumar da ya karkatar da kudade za a kama shi kuma a hukunta shi kamar yadda doka ta tanada.

Shi ma shugaban kungiyar kananan hukumomi a Nijeriya, Aminu Kaita, ya tabbatar da cewa har yanzu ana ci gaba da rabon kason kudaden kananan hukumomin daga asusun tarayya.

Kaita ya shaida cewa, “Muna aiki tukuro. Rana ta karshe shi ne Oktoba, kuma bai wuce ba tukuna. Don haka muna aiki a kan hakan.”

EFCC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

EFCC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Rashin Hadin Kan Atiku Da Obi Da Kwankwaso Na Iya Taimaka Wa Tazarcen Tinubu

May 16, 2026
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya Sun Shiga Rudani A Yayin Da Wa’adin Mika Sunayen Mambobi Ya Shude

May 15, 2026
Abincin Da Ya Kamata Ku Ci Lokacin Al’ada
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Hadakar ‘Yan Adawa Ta Rushe Yayin Da Tikitin Takarar Shugaban Kasa Ya Raba Kan Shugabannin ADC

May 9, 2026
Next Post
Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

Yawan Wutar Lantarkin Da Sin Ta Samar Ta Hanyar Dogaro Da Makamashi Mai Tsabta Ya Kai Kw/h Triliyan 2.51 Daga Watan Janairu Zuwa Satumba

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026
An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

An Gudanar Da Taron Kasa Da Kasa Na Magadan Gari Na 2026 A Beijing

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.