• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunkuri na dakile katsalandan siyasa a bangaren shari’a, shugabar kotun daukaka kara, Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta mayar da dukkan kararrakin zaben da ke gaban kotun na jihohi 36 guda 1,209 zuwa rassanta na Abuja da Legas.

Don haka, an shaida wa LEADERSHIP cewa duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraren kararrakin zabe a jihohi 36 na kasar nan za a saurare tare da zantar da hukunci a rassan kotun daukaka kara da ke Abuja da Legas.

  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Watsi Da Kudurin Dokar Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar

Bisa daukar wannan mataki da Dongban-Mensem ta yi, rassan kotun daukaka kara guda biyu ne kawai daga cikin 20 za su tantance duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe a fadin kasar nan.

Umurnin ya shafi zabukan gwamnoni, na ‘yan majalisar tarayya da na jihohi, wanda aka shigar a gaban kotun daukaka kara bayan da kotun sauraron kararrakin zabe ta zantar da hukuncinta.

Wata majiya mai tushe daga shalkwatan kotun daukaka kara da ke Abuja ta bayyana cewa, dukkan kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe guda 1,209 da aka shigar kan zaben 2023, an tura su Abuja da Legas domin saurare da zantar da hukunci.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Tuni dai aka bukaci dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu, wadanda suka daukaka kara da su bayar da hadin kai kan wannan umarni ta hanyar komawa ko dai Legas ko Abuja domin ci gaba da shari’arsu.

Binciken da wannan jarida ta yi ya nuna cewa Dongban-Mensem ta yi hakan ne a matsayin martani ga dimbin koke-koke da zanga-zangar da jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu suka yi, inda suke zargin alkalan kotun sauraron kararrakin zabe da hada kai da gwamnonin wajen karkatar da gaskiya a lokacin shari’a a jihohinsu.

Jam’iyyar APC mai mulki da kuma jam’iyyun adawa biyu, PDP da LP da fusatatun ‘yan takararsu sun koka a cikin korafe-korafe daban-daban ga shugabannin kotun daukaka kara kan yadda alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe suka hada kai da gwamnoninwajen takwara shari’ar zabe domin goyan bayansu.

Wannan yana daga cikin babban dalilin da ya sa Dongban-Mensem ta dauki mataki domin tsaftace bangaren shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa za a gurfanar da wasu alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe a gaban hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa (NJC) domin su fuskanci hukunci.

LEADERSHIP ta gano cewa, Dongban-Mensem ta dauki matakin mayar da duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a kotun daukaka kara zuwa Abuja da Legas sakamakon korafe-korafen aka shigar.

Don haka, sashen kotun daukaka kara na Abuja ne zai saurara tare da zantar da hukunci kan duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a jihohi 19 na yamkin arewacin Nijeriya.

Haka zalika, hukuncin da suka fitowa daga kotun sauraron karar zabe na jihohi 17 da ke kudancin Nijeriya, bangaren kotun na Legas ne zai saurara tare da zantar da hukunci.
Ban da haka, an gano cewa Dongban-Mensem ta tabbatar da cewa matakin zai tabbatar da ‘yancin kan bangaren shari’a, musamman kotun daukaka kara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun Daukaka KaraKotun sauraron kararrakin zabemai shari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

Next Post

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Zabe
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Noma

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.