• English
  • Business News
Saturday, September 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunkuri na dakile katsalandan siyasa a bangaren shari’a, shugabar kotun daukaka kara, Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta mayar da dukkan kararrakin zaben da ke gaban kotun na jihohi 36 guda 1,209 zuwa rassanta na Abuja da Legas.

Don haka, an shaida wa LEADERSHIP cewa duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraren kararrakin zabe a jihohi 36 na kasar nan za a saurare tare da zantar da hukunci a rassan kotun daukaka kara da ke Abuja da Legas.

  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Watsi Da Kudurin Dokar Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar

Bisa daukar wannan mataki da Dongban-Mensem ta yi, rassan kotun daukaka kara guda biyu ne kawai daga cikin 20 za su tantance duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe a fadin kasar nan.

Umurnin ya shafi zabukan gwamnoni, na ‘yan majalisar tarayya da na jihohi, wanda aka shigar a gaban kotun daukaka kara bayan da kotun sauraron kararrakin zabe ta zantar da hukuncinta.

Wata majiya mai tushe daga shalkwatan kotun daukaka kara da ke Abuja ta bayyana cewa, dukkan kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe guda 1,209 da aka shigar kan zaben 2023, an tura su Abuja da Legas domin saurare da zantar da hukunci.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Tuni dai aka bukaci dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu, wadanda suka daukaka kara da su bayar da hadin kai kan wannan umarni ta hanyar komawa ko dai Legas ko Abuja domin ci gaba da shari’arsu.

Binciken da wannan jarida ta yi ya nuna cewa Dongban-Mensem ta yi hakan ne a matsayin martani ga dimbin koke-koke da zanga-zangar da jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu suka yi, inda suke zargin alkalan kotun sauraron kararrakin zabe da hada kai da gwamnonin wajen karkatar da gaskiya a lokacin shari’a a jihohinsu.

Jam’iyyar APC mai mulki da kuma jam’iyyun adawa biyu, PDP da LP da fusatatun ‘yan takararsu sun koka a cikin korafe-korafe daban-daban ga shugabannin kotun daukaka kara kan yadda alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe suka hada kai da gwamnoninwajen takwara shari’ar zabe domin goyan bayansu.

Wannan yana daga cikin babban dalilin da ya sa Dongban-Mensem ta dauki mataki domin tsaftace bangaren shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa za a gurfanar da wasu alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe a gaban hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa (NJC) domin su fuskanci hukunci.

LEADERSHIP ta gano cewa, Dongban-Mensem ta dauki matakin mayar da duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a kotun daukaka kara zuwa Abuja da Legas sakamakon korafe-korafen aka shigar.

Don haka, sashen kotun daukaka kara na Abuja ne zai saurara tare da zantar da hukunci kan duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a jihohi 19 na yamkin arewacin Nijeriya.

Haka zalika, hukuncin da suka fitowa daga kotun sauraron karar zabe na jihohi 17 da ke kudancin Nijeriya, bangaren kotun na Legas ne zai saurara tare da zantar da hukunci.
Ban da haka, an gano cewa Dongban-Mensem ta tabbatar da cewa matakin zai tabbatar da ‘yancin kan bangaren shari’a, musamman kotun daukaka kara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun Daukaka KaraKotun sauraron kararrakin zabemai shari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

Next Post

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Noma

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

LABARAI MASU NASABA

Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

Shugaban Rundunar Sojin Sama Ya Buƙaci Ɗaukar Matakin Yaƙi Da Barazanar Tsaro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.