• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunkuri na dakile katsalandan siyasa a bangaren shari’a, shugabar kotun daukaka kara, Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta mayar da dukkan kararrakin zaben da ke gaban kotun na jihohi 36 guda 1,209 zuwa rassanta na Abuja da Legas.

Don haka, an shaida wa LEADERSHIP cewa duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraren kararrakin zabe a jihohi 36 na kasar nan za a saurare tare da zantar da hukunci a rassan kotun daukaka kara da ke Abuja da Legas.

  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Watsi Da Kudurin Dokar Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar

Bisa daukar wannan mataki da Dongban-Mensem ta yi, rassan kotun daukaka kara guda biyu ne kawai daga cikin 20 za su tantance duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe a fadin kasar nan.

Umurnin ya shafi zabukan gwamnoni, na ‘yan majalisar tarayya da na jihohi, wanda aka shigar a gaban kotun daukaka kara bayan da kotun sauraron kararrakin zabe ta zantar da hukuncinta.

Wata majiya mai tushe daga shalkwatan kotun daukaka kara da ke Abuja ta bayyana cewa, dukkan kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe guda 1,209 da aka shigar kan zaben 2023, an tura su Abuja da Legas domin saurare da zantar da hukunci.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Tuni dai aka bukaci dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu, wadanda suka daukaka kara da su bayar da hadin kai kan wannan umarni ta hanyar komawa ko dai Legas ko Abuja domin ci gaba da shari’arsu.

Binciken da wannan jarida ta yi ya nuna cewa Dongban-Mensem ta yi hakan ne a matsayin martani ga dimbin koke-koke da zanga-zangar da jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu suka yi, inda suke zargin alkalan kotun sauraron kararrakin zabe da hada kai da gwamnonin wajen karkatar da gaskiya a lokacin shari’a a jihohinsu.

Jam’iyyar APC mai mulki da kuma jam’iyyun adawa biyu, PDP da LP da fusatatun ‘yan takararsu sun koka a cikin korafe-korafe daban-daban ga shugabannin kotun daukaka kara kan yadda alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe suka hada kai da gwamnoninwajen takwara shari’ar zabe domin goyan bayansu.

Wannan yana daga cikin babban dalilin da ya sa Dongban-Mensem ta dauki mataki domin tsaftace bangaren shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa za a gurfanar da wasu alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe a gaban hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa (NJC) domin su fuskanci hukunci.

LEADERSHIP ta gano cewa, Dongban-Mensem ta dauki matakin mayar da duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a kotun daukaka kara zuwa Abuja da Legas sakamakon korafe-korafen aka shigar.

Don haka, sashen kotun daukaka kara na Abuja ne zai saurara tare da zantar da hukunci kan duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a jihohi 19 na yamkin arewacin Nijeriya.

Haka zalika, hukuncin da suka fitowa daga kotun sauraron karar zabe na jihohi 17 da ke kudancin Nijeriya, bangaren kotun na Legas ne zai saurara tare da zantar da hukunci.
Ban da haka, an gano cewa Dongban-Mensem ta tabbatar da cewa matakin zai tabbatar da ‘yancin kan bangaren shari’a, musamman kotun daukaka kara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun Daukaka KaraKotun sauraron kararrakin zabemai shari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

Next Post

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Noma

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.