• English
  • Business News
Saturday, July 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilan Mayar Da Daukaka Kararrakin Zabe 1,209 Zuwa Abuja Da Legas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A wani yunkuri na dakile katsalandan siyasa a bangaren shari’a, shugabar kotun daukaka kara, Mai Shari’a Monica Dongban-Mensem, ta mayar da dukkan kararrakin zaben da ke gaban kotun na jihohi 36 guda 1,209 zuwa rassanta na Abuja da Legas.

Don haka, an shaida wa LEADERSHIP cewa duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraren kararrakin zabe a jihohi 36 na kasar nan za a saurare tare da zantar da hukunci a rassan kotun daukaka kara da ke Abuja da Legas.

  • Zaben 2023: Takaddamar Kashi 94 Cikin 100 Na Kujerun Da Aka Lashe Ta Dora Shakku Kan INEC
  • Majalisar Dattawa Ta Yi Watsi Da Kudurin Dokar Bude Iyakokin Nijeriya Da Nijar

Bisa daukar wannan mataki da Dongban-Mensem ta yi, rassan kotun daukaka kara guda biyu ne kawai daga cikin 20 za su tantance duk wasu kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe a fadin kasar nan.

Umurnin ya shafi zabukan gwamnoni, na ‘yan majalisar tarayya da na jihohi, wanda aka shigar a gaban kotun daukaka kara bayan da kotun sauraron kararrakin zabe ta zantar da hukuncinta.

Wata majiya mai tushe daga shalkwatan kotun daukaka kara da ke Abuja ta bayyana cewa, dukkan kararrakin da suka taso daga hukuncin kotun sauraron kararrakin zabe guda 1,209 da aka shigar kan zaben 2023, an tura su Abuja da Legas domin saurare da zantar da hukunci.

Labarai Masu Nasaba

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

Tuni dai aka bukaci dukkan jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu, wadanda suka daukaka kara da su bayar da hadin kai kan wannan umarni ta hanyar komawa ko dai Legas ko Abuja domin ci gaba da shari’arsu.

Binciken da wannan jarida ta yi ya nuna cewa Dongban-Mensem ta yi hakan ne a matsayin martani ga dimbin koke-koke da zanga-zangar da jam’iyyun siyasa da ‘yan takararsu suka yi, inda suke zargin alkalan kotun sauraron kararrakin zabe da hada kai da gwamnonin wajen karkatar da gaskiya a lokacin shari’a a jihohinsu.

Jam’iyyar APC mai mulki da kuma jam’iyyun adawa biyu, PDP da LP da fusatatun ‘yan takararsu sun koka a cikin korafe-korafe daban-daban ga shugabannin kotun daukaka kara kan yadda alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe suka hada kai da gwamnoninwajen takwara shari’ar zabe domin goyan bayansu.

Wannan yana daga cikin babban dalilin da ya sa Dongban-Mensem ta dauki mataki domin tsaftace bangaren shari’a.

Rahotanni sun bayyana cewa za a gurfanar da wasu alkalan kotunan sauraron kararrakin zabe a gaban hukumar kula da harkokin shari’a ta kasa (NJC) domin su fuskanci hukunci.

LEADERSHIP ta gano cewa, Dongban-Mensem ta dauki matakin mayar da duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a kotun daukaka kara zuwa Abuja da Legas sakamakon korafe-korafen aka shigar.

Don haka, sashen kotun daukaka kara na Abuja ne zai saurara tare da zantar da hukunci kan duk wasu kararrakin zabe da aka shigar a jihohi 19 na yamkin arewacin Nijeriya.

Haka zalika, hukuncin da suka fitowa daga kotun sauraron karar zabe na jihohi 17 da ke kudancin Nijeriya, bangaren kotun na Legas ne zai saurara tare da zantar da hukunci.
Ban da haka, an gano cewa Dongban-Mensem ta tabbatar da cewa matakin zai tabbatar da ‘yancin kan bangaren shari’a, musamman kotun daukaka kara.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kotun Daukaka KaraKotun sauraron kararrakin zabemai shari'a
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kalubalen Da Zaben Gwamnonin Imo, Kogi Da Bayelsa Ke Fuskanta

Next Post

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

Related

Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

21 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

22 hours ago
Zaben Gwamnoni: Za Mu Ba Marada Kunya – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Kungiyoyi 110 Ne Ke Neman Rajistan Zama Jam’iyyun Siyasa A Yanzu Haka – INEC

23 hours ago
Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

3 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

3 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

4 weeks ago
Next Post
Noma

Dage Takunkumin CBN A Asusun Ajiyar Wasu Mutane Da Kamfanoni Ya Haifar Da Da Mai Ido

LABARAI MASU NASABA

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

Wang Yi Da Takwaransa Na Ghana Sun Aikewa Juna Sakon Murnar Cika Shekaru 65 Da Kulla Dangantakar Diplomasiyya A Tsakanin Kasashensu

July 5, 2025
Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

Sin Da Faransa Sun Amince Da Ingiza Cudanyar Mabanbantan Sassa Tare Da Samar Da Karin Tabbaci Ga Duniya

July 5, 2025
Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

Bukatar Ma’aurata Su Rika Bayyana Wa Junansu Gaskiyar Yanayin Samunsu

July 5, 2025
Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

Yadda Ake Gasasshen Biredi (Sandwich)

July 5, 2025
Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

Gyaran Jiki Da Kyawun Fata (5)

July 5, 2025
ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

ALGON Ta Taya Gwamnan Sani Murnar Samun Lambar Yabo Ta Kasa

July 5, 2025
Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

Kwankwaso Ba Zai Sake Yi Mana Takarar Shugabancin Ƙasa Ba A Zaɓen 2027 Ba – NNPP

July 5, 2025
Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

Cututtukan Da Aka Fi Fama Da Su lokacin Damina Da Yadda Za A Kauce Musu

July 5, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (8)

July 5, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

An Kama Matashin Da Ya Yi Garkuwa Da Abokinsa Tare Da Karbar Kudin Fansa

July 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.