• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

byYusuf Shuaibu
3 years ago
Karancin Mai

Kungiyar dillalan mai ta kasa (lPMAN) ta bayyana dalilin da ya sa aka samun karancin man fetur ta yadda ‘yan kasuwan suke shan wahala wajen samun canjin kudade na kasashen waje.

Babban jami’in gudanarwa na kungiyar lPMAN, Mike Osatuyi shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a Legas ranar Lahadi da ta gabata.

  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022
  • Gwamna Zulum Ya Bayar Da Umurnin Cafke ‘Ƴan Bangar Siyasar Borno

Mista Osatuyi ya kara da cewa ya zama wajibi su bayyana wa mutane yadda aka samu karancin man fetur sakamakon dogon layi da kuma wahala wajen samun mai a wasu sassan Nijeriya.

Ya zargi kamfanin mai na kasa (NNPC) da dakatar da shigo da isassan mai da zai wadata kasar nan. Mista Osatuyi ya jaddada cewa a halin yanzu ‘yan kasuwa ba za su iya ci gaba da sayar da man kan farashin da aka kayyade ba, saboda rashin daidaituwar farasha a ma’aciyar man.

“Muna fuskantar karancin mai sakamakon babu man da yawa. A halin yanzu farashin man a ma’aciyar man na masu zaman kansu yana tsakanin naira 205 zuwa naira 210, sabanin a baya da ake sayar da shi kan naira 162.50.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

“Kamfanin NNPC shi ne kadai yake dauko tataccen man daga waje, wanda hakan ke yi wa ‘yan kasuwan wahala samu,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ci gaba da cewa ‘ya’yan kungiyarsu suna sayan mai duk lita daya a kan naira 200 a ma’aciyar mai ta masu zaman kansu, wanda hakan zai yi musu mahala su yawar da man kan kayadaddan farashi.

“Bayan haka, wannan yanayin ya bai wa masu ma’aciyar mai damar sayar da man fiye da farashin gwamnati.

“Lokacin da muka hada da kudaden sufuri da kuma riba, sai kowacce lita daya ta kasance a kan naira 217. Saboda haka nawa ake so ‘yan kasuwa su sayar da man, sannan kuma muna yin wannan kasuwancin ne domin mu sami riba.

“Mambobinmu suna fuskantar karin farashin a ma’aciyar man, sannan kuma suna shan wahala kafin su sami man.

“Idan akwai man, me zai sa ba za mu sayar ba, amma babu man me. Mambobinmu suna sayar da man a gidajen man kan naira 230 zuwa 240 kan kawacce lita daya,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ce gwamnati ta lura cewa zai yi mata wahala ta ci gaba da bayar da tallafin man wanda ya sa har ta sauya fasalin kamfanin man na kasa domin samun damar magance matsalar.

Ya bukaci gwamnati ta bar kamfanoni masu zaman kansu su dunga shigo da man fetur da dizil da kuma kalanzir. A cewarsa, cire hannun gwamnati wajen shigo da man shi ne zai bayar da damar cikakken hannanta bangaren man a hannun ‘yan kasuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung
Manyan Labarai

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
Next Post
2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version