• English
  • Business News
Friday, October 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Karancin Mai

Kungiyar dillalan mai ta kasa (lPMAN) ta bayyana dalilin da ya sa aka samun karancin man fetur ta yadda ‘yan kasuwan suke shan wahala wajen samun canjin kudade na kasashen waje.

Babban jami’in gudanarwa na kungiyar lPMAN, Mike Osatuyi shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a Legas ranar Lahadi da ta gabata.

  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022
  • Gwamna Zulum Ya Bayar Da Umurnin Cafke ‘Ƴan Bangar Siyasar Borno

Mista Osatuyi ya kara da cewa ya zama wajibi su bayyana wa mutane yadda aka samu karancin man fetur sakamakon dogon layi da kuma wahala wajen samun mai a wasu sassan Nijeriya.

Ya zargi kamfanin mai na kasa (NNPC) da dakatar da shigo da isassan mai da zai wadata kasar nan. Mista Osatuyi ya jaddada cewa a halin yanzu ‘yan kasuwa ba za su iya ci gaba da sayar da man kan farashin da aka kayyade ba, saboda rashin daidaituwar farasha a ma’aciyar man.

“Muna fuskantar karancin mai sakamakon babu man da yawa. A halin yanzu farashin man a ma’aciyar man na masu zaman kansu yana tsakanin naira 205 zuwa naira 210, sabanin a baya da ake sayar da shi kan naira 162.50.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

“Kamfanin NNPC shi ne kadai yake dauko tataccen man daga waje, wanda hakan ke yi wa ‘yan kasuwan wahala samu,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ci gaba da cewa ‘ya’yan kungiyarsu suna sayan mai duk lita daya a kan naira 200 a ma’aciyar mai ta masu zaman kansu, wanda hakan zai yi musu mahala su yawar da man kan kayadaddan farashi.

“Bayan haka, wannan yanayin ya bai wa masu ma’aciyar mai damar sayar da man fiye da farashin gwamnati.

“Lokacin da muka hada da kudaden sufuri da kuma riba, sai kowacce lita daya ta kasance a kan naira 217. Saboda haka nawa ake so ‘yan kasuwa su sayar da man, sannan kuma muna yin wannan kasuwancin ne domin mu sami riba.

“Mambobinmu suna fuskantar karin farashin a ma’aciyar man, sannan kuma suna shan wahala kafin su sami man.

“Idan akwai man, me zai sa ba za mu sayar ba, amma babu man me. Mambobinmu suna sayar da man a gidajen man kan naira 230 zuwa 240 kan kawacce lita daya,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ce gwamnati ta lura cewa zai yi mata wahala ta ci gaba da bayar da tallafin man wanda ya sa har ta sauya fasalin kamfanin man na kasa domin samun damar magance matsalar.

Ya bukaci gwamnati ta bar kamfanoni masu zaman kansu su dunga shigo da man fetur da dizil da kuma kalanzir. A cewarsa, cire hannun gwamnati wajen shigo da man shi ne zai bayar da damar cikakken hannanta bangaren man a hannun ‘yan kasuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna
Manyan Labarai

Yadda DSS Suka Kama Masu Safarar Makamai Ga ‘Yan Bindiga A Jihar Kaduna

October 23, 2025
Next Post
2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

Fahimtar Sabon Tunani: Samar Da Wadata Ga Dukkan Jama’a Ta Daidaita Gibin Dake Tsakanin Hamshakai Da Matalauta

October 23, 2025
Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

Shugaban Senegal: Kasar Sin Ta Zama Abin Koyi Ga Kasashe Masu Tasowa

October 23, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayakan Boko Haram 6, Sun Kama Wasu A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 50, Sun Daƙile Hare-Hare A Borno

October 23, 2025
Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

Me Ake Fatan Gani A Shirin Sin Na Raya Kasa Na Shekaru Biyar Biyar Na Gaba

October 23, 2025
Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

Harkokin Ciniki Da Zuba Jari Tsakanin Sin Da Afirka Sun Samu Ci Gaba Mafi Girma a Shekaru 5 Da Suka Gabata

October 23, 2025
Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

Uwargidan Tinubu Ta Ƙaddamar Da Ɗakin Karatu Na E-learning A Zamfara

October 23, 2025
Kungiyar IOMed Za Ta Taka Rawar Gani Wajen Gina Al’umma Mai Makomar Bai Daya 

Kasar Sin Ta Karyata Rahoto Na Zuki-ta-malle Da Wata Cibiyar Binciken Amurka Ta Fitar Game Da Hadin Gwiwar Sin Da Yammacin Afirka

October 23, 2025
An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

An Kammala Taron JKS Inda Aka Amince Da Shawarwari Kan Shirin Ci Gaban Kasar Sin Na Shekaru Biyar-biyar Karo Na 15

October 23, 2025
Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

Tinubu Ya Rantsar Da Amupitan A Matsayin Sabon Shugaban INEC

October 23, 2025
Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

Sanarwar Bayan Taron Jks: Mene Ne Sirrin Kwarin Gwiwar Kasar Sin?

October 23, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.