ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, November 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Karancin Mai

Kungiyar dillalan mai ta kasa (lPMAN) ta bayyana dalilin da ya sa aka samun karancin man fetur ta yadda ‘yan kasuwan suke shan wahala wajen samun canjin kudade na kasashen waje.

Babban jami’in gudanarwa na kungiyar lPMAN, Mike Osatuyi shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a Legas ranar Lahadi da ta gabata.

  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022
  • Gwamna Zulum Ya Bayar Da Umurnin Cafke ‘Ƴan Bangar Siyasar Borno

Mista Osatuyi ya kara da cewa ya zama wajibi su bayyana wa mutane yadda aka samu karancin man fetur sakamakon dogon layi da kuma wahala wajen samun mai a wasu sassan Nijeriya.

ADVERTISEMENT

Ya zargi kamfanin mai na kasa (NNPC) da dakatar da shigo da isassan mai da zai wadata kasar nan. Mista Osatuyi ya jaddada cewa a halin yanzu ‘yan kasuwa ba za su iya ci gaba da sayar da man kan farashin da aka kayyade ba, saboda rashin daidaituwar farasha a ma’aciyar man.

“Muna fuskantar karancin mai sakamakon babu man da yawa. A halin yanzu farashin man a ma’aciyar man na masu zaman kansu yana tsakanin naira 205 zuwa naira 210, sabanin a baya da ake sayar da shi kan naira 162.50.

LABARAI MASU NASABA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

“Kamfanin NNPC shi ne kadai yake dauko tataccen man daga waje, wanda hakan ke yi wa ‘yan kasuwan wahala samu,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ci gaba da cewa ‘ya’yan kungiyarsu suna sayan mai duk lita daya a kan naira 200 a ma’aciyar mai ta masu zaman kansu, wanda hakan zai yi musu mahala su yawar da man kan kayadaddan farashi.

“Bayan haka, wannan yanayin ya bai wa masu ma’aciyar mai damar sayar da man fiye da farashin gwamnati.

“Lokacin da muka hada da kudaden sufuri da kuma riba, sai kowacce lita daya ta kasance a kan naira 217. Saboda haka nawa ake so ‘yan kasuwa su sayar da man, sannan kuma muna yin wannan kasuwancin ne domin mu sami riba.

“Mambobinmu suna fuskantar karin farashin a ma’aciyar man, sannan kuma suna shan wahala kafin su sami man.

“Idan akwai man, me zai sa ba za mu sayar ba, amma babu man me. Mambobinmu suna sayar da man a gidajen man kan naira 230 zuwa 240 kan kawacce lita daya,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ce gwamnati ta lura cewa zai yi mata wahala ta ci gaba da bayar da tallafin man wanda ya sa har ta sauya fasalin kamfanin man na kasa domin samun damar magance matsalar.

Ya bukaci gwamnati ta bar kamfanoni masu zaman kansu su dunga shigo da man fetur da dizil da kuma kalanzir. A cewarsa, cire hannun gwamnati wajen shigo da man shi ne zai bayar da damar cikakken hannanta bangaren man a hannun ‘yan kasuwa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?
Nazari

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7
Da ɗumi-ɗuminsa

Da Ɗumi-ɗumi: PDP Ta Kori Wike, Fayose, Anyanwu Da Wasu Mutane 7

November 15, 2025
Yanzu Satar Da Kuka Yi Ba Ta Da Amfani: Kwankwaso Ga Gwamnonin APC
Manyan Labarai

Sanusi II Kaɗai Muka Sani A Matsayin Halataccen Sarkin Kano – Kwankwaso

November 15, 2025
Next Post
2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai - Atiku

LABARAI MASU NASABA

DSS

Hukumar DSS Ta Kama Wani Kan Zargin Ƙerawa Da Rarraba Makamai A Filato

November 16, 2025
ECOWAS

A Zamanantar Da Tsarin Karatu A Makarantun Koyar Da Ilimin Addinin Musulunci – ECOWAS

November 16, 2025
APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

APOSUN Ta Jaddada Aniyarta Na Daƙile Hada-hadar Haramtattun Kuɗaɗe

November 16, 2025
Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

Yadda Za A Magance Yawan Faɗace-faɗace A Wasannin Gasar Firimiyar Nijeriya

November 16, 2025
Kwankwaso

NNPP Tana Da Ƙwarin Gwiwar Riƙe Kano Da Lashe Jihohin Arewa A Zaɓen 2027 – Ajuji

November 16, 2025
Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

Meke Kawo Yanke Hukunce-hukunce Masu Karo Da Juna Daga Kotuna?

November 16, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

Kuri’un Jin Ra’ayi Na CGTN Sun Shaida Adawar Sassan Kasa da Kasa Da Burin Masu Tsattsauran Ra’ayi Na Japan Na Ruguza Odar Kasa Da Kasa Ta Bayan Yakin Duniya Na 2 Dangane Da Batun Taiwan

November 15, 2025
Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

Hukumar Kwallon Kafa Ta Kasar Turkiyya Ta Dakatar Da ‘Yan Wasa 1024 Saboda Laifin Caca

November 15, 2025
Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

Sin Ta Bayyana Damuwa Dangane Da Matakin Amurka Na Ingiza Daftarin Tsawaita Aikin Tawagar UNISFA 

November 15, 2025
Za A Yi Gwanjon Rigunan Messi Na Gasar Kofin Duniya Ta 2022 Da Kudi Tsagwagwa

Ina Son Kasancewa Cikin Koshin Lafiya Kafin Buga Gasar Kofin Duniya Na Shekarar 2026 – Messi

November 15, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.