• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Dalilin Ci Gaba Da Fuskantar Karancin Mai A Fadin Nijeriya – Dillalai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar dillalan mai ta kasa (lPMAN) ta bayyana dalilin da ya sa aka samun karancin man fetur ta yadda ‘yan kasuwan suke shan wahala wajen samun canjin kudade na kasashen waje.

Babban jami’in gudanarwa na kungiyar lPMAN, Mike Osatuyi shi ya bayyana hakan lokacin da yake zantawa da kamfanin dillancin labarai na Nijeriya (NAN) a Legas ranar Lahadi da ta gabata.

  • CMG Ya Lashe Lambobin Yabo 4 Na Watsa Shirye-shirye Na Gasar Wasannin Olympics Ta Beijing 2022
  • Gwamna Zulum Ya Bayar Da Umurnin Cafke ‘Ƴan Bangar Siyasar Borno

Mista Osatuyi ya kara da cewa ya zama wajibi su bayyana wa mutane yadda aka samu karancin man fetur sakamakon dogon layi da kuma wahala wajen samun mai a wasu sassan Nijeriya.

Ya zargi kamfanin mai na kasa (NNPC) da dakatar da shigo da isassan mai da zai wadata kasar nan. Mista Osatuyi ya jaddada cewa a halin yanzu ‘yan kasuwa ba za su iya ci gaba da sayar da man kan farashin da aka kayyade ba, saboda rashin daidaituwar farasha a ma’aciyar man.

“Muna fuskantar karancin mai sakamakon babu man da yawa. A halin yanzu farashin man a ma’aciyar man na masu zaman kansu yana tsakanin naira 205 zuwa naira 210, sabanin a baya da ake sayar da shi kan naira 162.50.

Labarai Masu Nasaba

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

“Kamfanin NNPC shi ne kadai yake dauko tataccen man daga waje, wanda hakan ke yi wa ‘yan kasuwan wahala samu,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ci gaba da cewa ‘ya’yan kungiyarsu suna sayan mai duk lita daya a kan naira 200 a ma’aciyar mai ta masu zaman kansu, wanda hakan zai yi musu mahala su yawar da man kan kayadaddan farashi.

“Bayan haka, wannan yanayin ya bai wa masu ma’aciyar mai damar sayar da man fiye da farashin gwamnati.

“Lokacin da muka hada da kudaden sufuri da kuma riba, sai kowacce lita daya ta kasance a kan naira 217. Saboda haka nawa ake so ‘yan kasuwa su sayar da man, sannan kuma muna yin wannan kasuwancin ne domin mu sami riba.

“Mambobinmu suna fuskantar karin farashin a ma’aciyar man, sannan kuma suna shan wahala kafin su sami man.

“Idan akwai man, me zai sa ba za mu sayar ba, amma babu man me. Mambobinmu suna sayar da man a gidajen man kan naira 230 zuwa 240 kan kawacce lita daya,” in ji shi.

Mista Osatuyi ya ce gwamnati ta lura cewa zai yi mata wahala ta ci gaba da bayar da tallafin man wanda ya sa har ta sauya fasalin kamfanin man na kasa domin samun damar magance matsalar.

Ya bukaci gwamnati ta bar kamfanoni masu zaman kansu su dunga shigo da man fetur da dizil da kuma kalanzir. A cewarsa, cire hannun gwamnati wajen shigo da man shi ne zai bayar da damar cikakken hannanta bangaren man a hannun ‘yan kasuwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DillalaiIPMANKarancin MaiMan feturNNPC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jerin Kayayyakin Da INEC Ta Yi Asara Bayan Kai Mata Hare-hare A Ofisoshinta

Next Post

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

Related

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu
Manyan Labarai

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

5 hours ago
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki
Manyan Labarai

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

16 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

18 hours ago
Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su
Manyan Labarai

Ƴan Majalisa Na Binciken Cibiyoyin Ci Gaban Masana’antu 30 Da Aka Yi Watsi Da Su

23 hours ago
Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas
Manyan Labarai

Tinubu Ya Sasanta Wike, Fubara, Da Ƴan Majalisar Ribas

23 hours ago
Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja
Manyan Labarai

Rundunar Sojin Nijeriya Ta Tabbatar Da Kisan Jami’anta A Kaduna Da Neja

1 day ago
Next Post
2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai – Atiku

2023: Gwamnatinmu Za Ta Farfaɗo Da Harkar ilimi Da Walwalar Malamai - Atiku

LABARAI MASU NASABA

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

Za a Binne Ɗantata A Madina, Za Ai Yi Sallar Ga’ibi A Kano

June 28, 2025
Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

Me Ya Sa Syria Ta Bari Ana Amfani Da Sararin Samaniyarta Wajen Kai Wa Iran Hari?

June 28, 2025
Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

Wace Nahiya Ce Ta Fi Iya Ƙwallon Ƙafa Tsakanin Turai Da Kudancin Amurka?

June 28, 2025
Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

Ƙasashen Afrika 10 Da Suka Fi Girman Kasafin Kudi A 2025

June 28, 2025
Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

Ƙungiyar Lauyoyi Musulmi Reshen Kaduna Ta Yi Allah-Wadai Da Kisan Matafiya A Filato

June 28, 2025
Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

Shahararren Ɗan Kasuwa Aminu Dantata Ya Rasu

June 28, 2025
Hoton Tallan Taliyar Indomie

Indomie Ta Kaddamar Da Shirin Gangamin Abinci Mai Gina Jiki Na ‘Ingantaccen Abinci Domin Nasara’

June 28, 2025
Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.