• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume

by Yusuf Shuaibu
9 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata mai wakiltar mazabar Borno ta arewa, Ali Ndume, ya bayyana rashin amincewarsa da kudirin gyaran haraji, da ya tsallake karatu na biyu a majalisar dattawa.

Da yake jawabi a matsayin bako a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels, tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawan ya soki lokacin da za aka bujiro da kudirin, yana mai cewa kamata ya yi a mayar da hankali kan gyara harkokin mulki kafin a sake fasalin haraji.

  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara

An dai bayyana cewa majalisar dattawa ta amince da kudirin dokar haraji guda hudu a karatu na biyu a ranar Alhamis ta hanyar kada kuri’a.

Kudirorin sun hada da kudirin kafa hukumar tattara kudaden shiga ta hadin gwiwa, kotun daukaka kara ta haraji, da kuma ofishin mai kula da haraji, duk wani bangare na shirin sake fasalin haraji na Shugaban kasa Bola Tinubu.

Sai dai Sanata Ndume ya bayyana damuwarsa game da kudirorin, inda ya ba da misali da batutuwa irin su lokacin da bai dace ba, batun cire haraji, karin haraji, da kuma rashin amincewa daga wurin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

Ya kuma bayyana cewa kasar na kashe sama da kashi 50 cikin 100 na kasafin kudinta wajen kashe kudade na yau da kullun da kuma biyan basussuka.

“Eh, yana da kyau a yi gyara. Amma ko da gyaran ne za a yi dole ne a ba da fifiko a lokacin da ya dace, kuma a tabbatar da ra’ayin ‘yan Nijeriya domin wannan dimokuradiyya ce. Gwamnati ce ta jama’a, wanda mutane suka zabeta da hannunsu.

“Na farko a Nijeriya abin da ya kamata mu yi shi ne gyara harkokin gwamnati. Ma’aikatanmu da kashe-kashen kudade marasa amfani da aka yi a kasafin kudin shekarar 2024, wanda aka kashe kusan kashi 50 zuwa 60 na kasafin kudin da kansa. Har zuwa Nuwamba kuma ba a aiwatar da kashi 20 na kasafin kudin ba. Amma idan ka duba kudaden da ake kashewa akai-akai, ya riga ya kare.

“Saboda haka, sama da naira tiriliyan 15 zuwa 20 ne ke shiga cikin ma’aikata, da biyan basussuka, da kuma kashe-kashe na yau da kullum. Ya kamata mu gyara gwamnati, ba kawai bangaren zartarwa ba, muna bukatar sake fasalin gwamnati gaba daya,” in ji shi.

Sanatan ya kuma nuna damuwarsa kan cewa, idan har ma ya zama doka, to majalisar dattawa ta dauke shi tamkar wani kudiri na shugaban kasa ne, wanda hakan ya zai kara karfafa zaman doya da manza tsakanin majalisar da bangren zartarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiNdume
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 

Next Post

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Related

Fursunoni Ba Za Su Samu Damar Kada Kuri’a Ba A Zaben 2023 – INEC
Tambarin Dimokuradiyya

Rudani Ya Kunno Kai Yayin Da INEC Ta Ki Amincewa Da Shugabancin ADC

1 week ago
‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Nijeriya Suna Shan Wahala A Lokacin Da Gwamnatin Tinubu Ta Fi Damuwa Da Aljihunta – Sule Lamido

1 week ago
Daraktoci Da Jami’an FCT 7 Na Fuskantar Tuhume-tuhume Kan Badakar Fili
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Idan Kana Son Tarwatsa PDP, To Ka Dawo Da Peter Obi – Wike

1 week ago
ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro
Tambarin Dimokuradiyya

ADC Ta Bukaci Tinubu Ya Kafa Dokar Ta Baci A Katsina Da Zamfara Kan Rashin Tsaro

2 weeks ago
katin zabe
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Bayyana Damuwarta Kan Katunan Zabe 360,000 Da Ba A Karba Ba A Kano

2 weeks ago
Jam’iyyar PDP Ta Janye Daga Shiga Zaɓen Ƙananan Hukumomi A Kebbi
Tambarin Dimokuradiyya

Shugabannin PDP Sun Shiga Dimuwa Yayin Da APC Ke Zawarcin Wasu Gwamnoninsu

2 weeks ago
Next Post
Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

Madabba’ar Sin Ta Ba Da Gudunmuwar Littattafai Ga Makarantun Koyar Da Sinanci A Nijeriya

September 13, 2025
An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

An Kaddamar Da Tashar Watsa Labarai Ta CMG A Chengdu

September 13, 2025
An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

An Gudanar Da Dandalin Tattauna Al’adu Na Kasa Da Kasa Na Golden Panda Na 2025 A Birnin Chengdu

September 13, 2025
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

September 13, 2025
Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

Kasar Sin Za Ta Kare Hakkin Kamfanoninta Ciki Har Da Tiktok

September 13, 2025
Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

Aleksandar Vucic: Serbia Na Goyon Bayan Shawarar Kula Da Harkokin Duniya Da Kasar Sin Ta Gabatar

September 13, 2025
Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

Etsu Nupe Ginshiƙin Zaman Lafiya Da Haɗin Kai Ne A Nijeriya — Ministan Yaɗa Labarai

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.