• English
  • Business News
Saturday, May 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume

by Yusuf Shuaibu
5 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata mai wakiltar mazabar Borno ta arewa, Ali Ndume, ya bayyana rashin amincewarsa da kudirin gyaran haraji, da ya tsallake karatu na biyu a majalisar dattawa.

Da yake jawabi a matsayin bako a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels, tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawan ya soki lokacin da za aka bujiro da kudirin, yana mai cewa kamata ya yi a mayar da hankali kan gyara harkokin mulki kafin a sake fasalin haraji.

  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara

An dai bayyana cewa majalisar dattawa ta amince da kudirin dokar haraji guda hudu a karatu na biyu a ranar Alhamis ta hanyar kada kuri’a.

Kudirorin sun hada da kudirin kafa hukumar tattara kudaden shiga ta hadin gwiwa, kotun daukaka kara ta haraji, da kuma ofishin mai kula da haraji, duk wani bangare na shirin sake fasalin haraji na Shugaban kasa Bola Tinubu.

Sai dai Sanata Ndume ya bayyana damuwarsa game da kudirorin, inda ya ba da misali da batutuwa irin su lokacin da bai dace ba, batun cire haraji, karin haraji, da kuma rashin amincewa daga wurin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Ya kuma bayyana cewa kasar na kashe sama da kashi 50 cikin 100 na kasafin kudinta wajen kashe kudade na yau da kullun da kuma biyan basussuka.

“Eh, yana da kyau a yi gyara. Amma ko da gyaran ne za a yi dole ne a ba da fifiko a lokacin da ya dace, kuma a tabbatar da ra’ayin ‘yan Nijeriya domin wannan dimokuradiyya ce. Gwamnati ce ta jama’a, wanda mutane suka zabeta da hannunsu.

“Na farko a Nijeriya abin da ya kamata mu yi shi ne gyara harkokin gwamnati. Ma’aikatanmu da kashe-kashen kudade marasa amfani da aka yi a kasafin kudin shekarar 2024, wanda aka kashe kusan kashi 50 zuwa 60 na kasafin kudin da kansa. Har zuwa Nuwamba kuma ba a aiwatar da kashi 20 na kasafin kudin ba. Amma idan ka duba kudaden da ake kashewa akai-akai, ya riga ya kare.

“Saboda haka, sama da naira tiriliyan 15 zuwa 20 ne ke shiga cikin ma’aikata, da biyan basussuka, da kuma kashe-kashe na yau da kullum. Ya kamata mu gyara gwamnati, ba kawai bangaren zartarwa ba, muna bukatar sake fasalin gwamnati gaba daya,” in ji shi.

Sanatan ya kuma nuna damuwarsa kan cewa, idan har ma ya zama doka, to majalisar dattawa ta dauke shi tamkar wani kudiri na shugaban kasa ne, wanda hakan ya zai kara karfafa zaman doya da manza tsakanin majalisar da bangren zartarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiNdume
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 

Next Post

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
Ndume
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

Gwamna Lawal Ya Jaddada Aniyar Inganta Kiwon Lafiya A Jihar Zamfara

May 16, 2025
Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

Shugaban Senegal: Ana Fatan Ci Gaba Da Zurfafa Zumuncin Dake Tsakanin Sin Da Senegal

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Daina Kassara Kamfanonin Fasaha Da Na AI Na Sin

May 16, 2025
JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

JAMB Ta Ƙaddamar Da Binciken Gaggawa Kan Sakamakon Jarrabawar Bana Bayan Jerin Ƙorafe-Ƙorafe 

May 16, 2025
Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

Gwamnatin Tarayya Na Ƙoƙarin Farfaɗo Da Sashin Raba Wutar Lantarki A Nijeriya

May 16, 2025
CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

CMG Ya Gabatar Da Fasahar Tsara Shirye-Shiryen Bidiyo Da Rediyo Bisa Fasahar Sadarwa Ta 5G A ITU

May 16, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 2, Sun Ƙwato Shanun Sata 1,000 A Taraba

May 16, 2025
Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

Xi Jinping Ya Jaddada Wajibcin Koyi Da Nagartattun Halayen Wasu Mutane Masu Bukata Ta Musamman

May 16, 2025
Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

Kasar Sin Ta Cimma Burinta A Fannin Kulla Yarjejeniyoyin Fasaha Kafin Lokacin Da Ta Tsara

May 16, 2025
Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

Firaministan Sin: Tattalin Arzikin Sin Na Habaka Yadda Ya Kamata Yayin Da Kasar Ke Samun Ci Gaba

May 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.