• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata mai wakiltar mazabar Borno ta arewa, Ali Ndume, ya bayyana rashin amincewarsa da kudirin gyaran haraji, da ya tsallake karatu na biyu a majalisar dattawa.

Da yake jawabi a matsayin bako a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels, tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawan ya soki lokacin da za aka bujiro da kudirin, yana mai cewa kamata ya yi a mayar da hankali kan gyara harkokin mulki kafin a sake fasalin haraji.

  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara

An dai bayyana cewa majalisar dattawa ta amince da kudirin dokar haraji guda hudu a karatu na biyu a ranar Alhamis ta hanyar kada kuri’a.

Kudirorin sun hada da kudirin kafa hukumar tattara kudaden shiga ta hadin gwiwa, kotun daukaka kara ta haraji, da kuma ofishin mai kula da haraji, duk wani bangare na shirin sake fasalin haraji na Shugaban kasa Bola Tinubu.

Sai dai Sanata Ndume ya bayyana damuwarsa game da kudirorin, inda ya ba da misali da batutuwa irin su lokacin da bai dace ba, batun cire haraji, karin haraji, da kuma rashin amincewa daga wurin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ya kuma bayyana cewa kasar na kashe sama da kashi 50 cikin 100 na kasafin kudinta wajen kashe kudade na yau da kullun da kuma biyan basussuka.

“Eh, yana da kyau a yi gyara. Amma ko da gyaran ne za a yi dole ne a ba da fifiko a lokacin da ya dace, kuma a tabbatar da ra’ayin ‘yan Nijeriya domin wannan dimokuradiyya ce. Gwamnati ce ta jama’a, wanda mutane suka zabeta da hannunsu.

“Na farko a Nijeriya abin da ya kamata mu yi shi ne gyara harkokin gwamnati. Ma’aikatanmu da kashe-kashen kudade marasa amfani da aka yi a kasafin kudin shekarar 2024, wanda aka kashe kusan kashi 50 zuwa 60 na kasafin kudin da kansa. Har zuwa Nuwamba kuma ba a aiwatar da kashi 20 na kasafin kudin ba. Amma idan ka duba kudaden da ake kashewa akai-akai, ya riga ya kare.

“Saboda haka, sama da naira tiriliyan 15 zuwa 20 ne ke shiga cikin ma’aikata, da biyan basussuka, da kuma kashe-kashe na yau da kullum. Ya kamata mu gyara gwamnati, ba kawai bangaren zartarwa ba, muna bukatar sake fasalin gwamnati gaba daya,” in ji shi.

Sanatan ya kuma nuna damuwarsa kan cewa, idan har ma ya zama doka, to majalisar dattawa ta dauke shi tamkar wani kudiri na shugaban kasa ne, wanda hakan ya zai kara karfafa zaman doya da manza tsakanin majalisar da bangren zartarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiNdume
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 

Next Post

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

4 weeks ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

An Horas Da Kwararrun Ma’aikata Sama Da Dubu 500 Karkashin Hadin Gwiwar Sin Da Sassan Kasa Da Kasa A Fannin Inganta Kwarewar Ma’aikata

June 28, 2025
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

June 28, 2025
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.