• English
  • Business News
Tuesday, July 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume

by Yusuf Shuaibu
7 months ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
Dalilin Da Ya Sa Nake Yakar Kudirin Sake Fasalin Haraji – Sanata Ndume
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata mai wakiltar mazabar Borno ta arewa, Ali Ndume, ya bayyana rashin amincewarsa da kudirin gyaran haraji, da ya tsallake karatu na biyu a majalisar dattawa.

Da yake jawabi a matsayin bako a shirin siyasa na gidan talabijin na Channels, tsohon mai tsawatarwa na majalisar dattawan ya soki lokacin da za aka bujiro da kudirin, yana mai cewa kamata ya yi a mayar da hankali kan gyara harkokin mulki kafin a sake fasalin haraji.

  • Hukumar NDLEA Ta Kama Mutane 14,480 A Cikin Watanni 10 – Marwa
  • Gwamna Lawal Ya Jaddada Ƙudurinsa Na Bai Wa Ɓangaren Shari’a ‘Yanci Don Samar Da Adalci A Zamfara

An dai bayyana cewa majalisar dattawa ta amince da kudirin dokar haraji guda hudu a karatu na biyu a ranar Alhamis ta hanyar kada kuri’a.

Kudirorin sun hada da kudirin kafa hukumar tattara kudaden shiga ta hadin gwiwa, kotun daukaka kara ta haraji, da kuma ofishin mai kula da haraji, duk wani bangare na shirin sake fasalin haraji na Shugaban kasa Bola Tinubu.

Sai dai Sanata Ndume ya bayyana damuwarsa game da kudirorin, inda ya ba da misali da batutuwa irin su lokacin da bai dace ba, batun cire haraji, karin haraji, da kuma rashin amincewa daga wurin ‘yan Nijeriya.

Labarai Masu Nasaba

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

Ya kuma bayyana cewa kasar na kashe sama da kashi 50 cikin 100 na kasafin kudinta wajen kashe kudade na yau da kullun da kuma biyan basussuka.

“Eh, yana da kyau a yi gyara. Amma ko da gyaran ne za a yi dole ne a ba da fifiko a lokacin da ya dace, kuma a tabbatar da ra’ayin ‘yan Nijeriya domin wannan dimokuradiyya ce. Gwamnati ce ta jama’a, wanda mutane suka zabeta da hannunsu.

“Na farko a Nijeriya abin da ya kamata mu yi shi ne gyara harkokin gwamnati. Ma’aikatanmu da kashe-kashen kudade marasa amfani da aka yi a kasafin kudin shekarar 2024, wanda aka kashe kusan kashi 50 zuwa 60 na kasafin kudin da kansa. Har zuwa Nuwamba kuma ba a aiwatar da kashi 20 na kasafin kudin ba. Amma idan ka duba kudaden da ake kashewa akai-akai, ya riga ya kare.

“Saboda haka, sama da naira tiriliyan 15 zuwa 20 ne ke shiga cikin ma’aikata, da biyan basussuka, da kuma kashe-kashe na yau da kullum. Ya kamata mu gyara gwamnati, ba kawai bangaren zartarwa ba, muna bukatar sake fasalin gwamnati gaba daya,” in ji shi.

Sanatan ya kuma nuna damuwarsa kan cewa, idan har ma ya zama doka, to majalisar dattawa ta dauke shi tamkar wani kudiri na shugaban kasa ne, wanda hakan ya zai kara karfafa zaman doya da manza tsakanin majalisar da bangren zartarwa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HarajiNdume
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Kano Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Fadar Sarkin Kano 

Next Post

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Related

Ko Yanzu Tinubu Ya Yi Rawar Gani, Kuma Yana Ƙoƙari Sosai – Buhari
Rahotonni

Muhimman Abubuwa 10 Da Kowa Zai So Ya Sani Game Da Marigayi Shugaban Ƙasa Buhari

2 days ago
Kashim Shettima Ya Mayar Da Martani Kan Tsadar Rayuwa
Tambarin Dimokuradiyya

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

4 days ago
Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

Hadakar Jam’iyyar ADC Ta Fara Dusashe Karfin PDP A Wasu Jihohin Nijeriya

4 days ago
Nijeriya Na Fuskantar Siyasa Mara Tabbas —  Peter Obi
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Takarar Shugaban Kasa Zan Yi Ba Mataimaki Ba – Peter Obi

4 days ago
Yadda Taron Kungiyar Gwagwarmayar Talakawa Ta Kaya Kan Zaben 2023 A Zariya
Tambarin Dimokuradiyya

INEC Ta Ayyana 16 Ga Agusta Don Gudanar Da Zaben Cike Gurbi A Jihohi 12

2 weeks ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Tambarin Dimokuradiyya

APC: Ko Sadaukarwar Ganduje Za Ta Dakile Barazanar Jam’iyyun Adawa A Zaben 2027?

2 weeks ago
Next Post
Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

Kafofin Yada Labarai Fiye Da 2600 A Duk Fadin Duniya Za Su Yada Shagalin Murnar Bikin Bazara Da CMG Zai Gabatar

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

Xi Ya Gana Da Shugabannin Tawagogin Kasa Da Kasa Masu Halartar Taron SCO

July 15, 2025
An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

An Gudanar Da Taro Game Da Sana’ar Sarrafa Sinadarai Na Kasa Da Kasa Karo Na 12 A Beijing

July 15, 2025
Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

Yawan Karuwar GDPn Sin A Rabin Farkon Bana Ya Kai 5.3%

July 15, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 20, Sun Ƙona Gidaje A Ƙauyukan Filato

July 15, 2025
Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

Shugaba Xi Ya Gabatar Da Jawabi Ga Taron Koli Game Da Aikin Raya Birane 

July 15, 2025
Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

Ƴansanda Sun Cafke Mutane Biyu Bisa Zargin Kashe Ɗan Ƙasar China

July 15, 2025
Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

Taron Matasan Sin Da Afrika Kan Tsaro Zai Kirkiro Wata Sabuwar Mahanga Ta Magance Matsalolin Tsaro

July 15, 2025
Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

Girman Kai Da Son Zuciya Ba Za Su Sa A Amince Ko Ba Da Hadin Kai Ba

July 15, 2025
Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

Bayan Shekaru 6 A Hannun Boko Haram, Wasu Yara Biyu Sun Kuɓuta

July 15, 2025
Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

Mai Gaskiya Ya Koma Gida: Za A Yi Jana’izar Buhari A Daura

July 15, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.