• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Gwamnatin Tarayya Da Hukumar FAO Na Zuba Dala Biliyan 3.14 A Fannin Noma

byAbubakar Abba
2 weeks ago
Noma

Gwamnatin tarayya ta kaddamar da shirye-shiryen zuba hannun jari a bangaren aikin noma na kimanin dala biliyan 3.14.

An aiwatar da shirin ne a karkashin hukumar kula da abinci da ayyukan noma ta majalisar dinkin duniya (FAO), zuba hannun jairin zai mayar da hankali a fanonin noman tumatir, rogo, masara, madarar shanu da kuma kiwon kifi.

  • Ana Fatan Majalisar Wakilan Amurka Za Ta Taka Muhimmiyar Rawa Wajen Raya Hadin Gwiwar Sin Da Amurka
  • Nazari Kan Littafin Baba Zube Na 5 (Gwamnati)

Babban Ministan Aikin Noma da Samar da Wadataccen Abinci, Sanata Abubakar Kyari, ya sanar da hakan ne a taron zuba hannun jari da ya gudana a Abuja.

Ya ce, gwamnatin tarayya za ta bayar da dauki na dala biliyan 1.75, inda kuma masu zaman kansu a fannin, za su bayar da dala biliyan 1.39.

“Za a gudanar da aikin ne da nufin tsamo miliyoyin ‘yan kasar nan daga talauci, samar da ayyukan yi, bunkasa samar da abinci mai gina jiki da sauran makamantansu,” in ji Kyari.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

Har ila yau, ya kara da cewa; kudaden shigar da za a samu, za su karu zuwa dala 657, inda kuma za a kara samun sama da tan miliyan 1.2.

Ya ci gaba da cewa, albarkatun da Nijeriya ta ke da su, kashi 20 a cikin dari ne kacal na miliyoyin hektar noman da ake da su a wannan kasa ake nomawa, wanda kuma na hektar noman rani ta haura miliyan uku.

Ministan ya kuma sanar da cewa, bisa sauye-sauyen da ake ci gaba da samar wa bangaren shiyoyin sarrafa amfanin gona don samun riba, samar da kayan aiki da kudden aikin noma da bankin manoma ke yi da sauransu.

Kyari ya kuma bai wa masu son zuba hannun jarin tabbacin samar musu da kyakkyawan yanayi, domin samun cin nasarar abin da aka sanya a gaba.

Shi kuwa, wakilin FAO a kasar nan Hussein Gadain, ya yaba wa gwamnatin; kan kokarin da take ci gaba da yi a shirin muradan karni wato SDGs.

Ya kuma jinjina wa salon shugabanci na mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima, wajen janyo masu zuba hannunn jari da samar da dabarun zamani.

Shi kuwa, jakadan tarayyar turai a kasar nan, Gautier Mignot, ya nanata ci gaba da bayar da goyon bayan Tarayyar Turai, wajen yin hadaka da kasar nan.

Ya ce, ko a kwanan baya, tarayyar turai, ta zuba hannun jarin da ya kai na Fam miliyan 80 a jihohi bakwai da ke kasar nan.

A cewarsa, wannan hadakar za ta taimaka wajen kara karfafa bunkasa fannin aikin noman wannan kasa baki-daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Yadda Za A Iya Samun Wadatacciyar Riba A Kiwon Jimina

October 3, 2025
Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo
Noma Da Kiwo

Hikimar Gwamnatin Tarayya Ta Tallafa Wa Manoman Jihar Edo

October 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Kaddamar Da Shirin Bunkasa Kiwon Kifi

September 27, 2025
Next Post
Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

Sabon Farashin Jigilar Mahajjata A 2026, Ƴan Arewa N8.2m, Ƴan Kudu N8.5m

LABARAI MASU NASABA

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025
Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

Wakilin Sin Ya Ba Da Shawarwari Uku Kan Yaki Da Ta’addanci

October 7, 2025
Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

Cika Shekaru 25 Da Kafuwa: ACF Ta Jadadda Kudirinta Na Samun Hadin Kai Da Zaman Lafiya

October 7, 2025
Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

Sauyin Yanayi: “Damfara” Ko Gudun Sauke Nauyi?

October 7, 2025
SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

SSANU, NASU Za Su Gudanar Da Zanga-zanga A Faɗin Nijeriya A Ranar 9 Ga Oktoba

October 7, 2025
Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

Daukacin Mambobin Majalisar Kare Hakkokin Dan Adam Ta MDD Sun Amince Da Kudurin Da Kasar Sin Ta Gabatar Kan Kare Hakkokin Tattalin Arziki Da Zamantakewa Da Al’adu

October 7, 2025
Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

Ɓatan-dabon Naira Tiriliyan 210: Kamfanin NNPCL Ya Buƙaci A Ƙara Masa Lokaci

October 7, 2025
Tinubu

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisa Kan Karɓo Bashin Dala Biliyan $2.347 Da $500m Na Sukuk 

October 7, 2025
Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version