• English
  • Business News
Saturday, July 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja

by Abubakar Abba
2 years ago
in Noma Da Kiwo
0
Dalilin Karancin Kwan Gidan Gona A Jihar Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ana ci gaba da fuskantar karancin kwan gidan gona a Jihar Neja, biyo bayan rufe gidajen gona da ake ci gaba da yi a fadin jihar.

Wannan dai ya afku ne, sakamakon tsadar kayan abincin kajin da masu sana’ar ke ci gaba da fuskanta.

  • Za Mu Tabbatar An Hukunta Masu Zaluntar Kananan Yara Da Mata – Kwamishina Rabi Salisu
  • Matsayin Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Japan Na Zuba Dagwalon Nukiliya A Cikin Teku Bai Sauya Ba

Rahotanni sun bayyana cewa, kwan kajin gidan gonar da ake turo wa zuwa jihar, musamman daga Jihar Oyo ya yi matukar raguwa, saboda tsadar da man fetur ya yi bayan cire tallafin man da Gwamnatin Tarayya ta yi.

Haka zalika, an ruwaito cewa yanzu farashin kowane kiret guda da ake sayo wa daga gidan gona a jihar, ya doshi naira 2,200 sabanin yadda ake sayar da shi a baya kan naira 1,800.

Har ila yau, akwai kuma kalubalen rashin kyakkyawan yanayi da ke shafar yawan kwan da ya kamata a samu a gidan gona, wanda haka ke sa kajin na mutuwa.

Labarai Masu Nasaba

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Wani mai sayen kwan, mai suna Isah Suleiman ya bayyana cewa, ya zagaya zuwa shaguna da dama don sayen kwan, amma bai samu ba.

Shi kuwa wani mai saye da sayar da kwan da ke Kasuwar Tunga a jihar, mai suna Christopher Ukaegbu ya bayyana cewa, kwan ya yi karanci a duk fadin jihar; kusan sama da mako biyu da suka wuce.

Shi ma wani manajan kajin gidan gonar da ke garin Minna a jihar ta Neja, Mista Adeyemo Adewale ya bayyana cewa, an samu karancin kwan da kuma tsadarsa a makon da ya gabata tare da tashin farashin abincinsu.

Bugu da kari, Mista Adeyemo ya ce, gidan gona da dama a jihar ta Neja da ake kiwon kajin gidan gonan; yawancinsu sun rufe, musamman saboda tsadar abincin da ake ciyar da kajin da kuma kwan da wasu manyan gidan gona da ke kawo wa Jihar Neja daga Jihar Oyo, sun dakatar sakamakon tsadar man fetur ya yi.

Adeyemo ya ci gaba da cewa, a kwanan baya wani gidan gona  da yake a garin Minna, da ake  kiwata kajin gidan gona wanda yawansu ya kai 3,000, tuni an rufe shi sakamakon wannan tsada ta abincin kaji, hatta mu ma da muka ci gaba da yin kiwon muna kokarin ne kawai, in ji shi.

A cewarsa, buhu daya na abincin kajin da muke saya a kan naira 8,500 a watan da ya wuce, yanzu kowane buhu ya tashi zuwa Naira 9,500.

Haka nan, masu gidan gonar da suka ci gaba da kiwata kajin, sun gaza samar da yawan kwan da ake bukata a kasuwanni, inda sauran mutane kuma ke ci gaba da nuna bukatarsu ta kwan.

Ya kara da cewa, a yanzu haka a gidan gonar tasa ba za a iya samar da bukatar kwan da mutane ke bukata ba na kaso 50 cikin 100 ba, inda ya ce, wasu masu zuwa gonar don sayen kwan, na far zuwa ne tun misalin karfe biyar na Asuba, domin sayen kwan da kuma kaji wadanda aka kyankyashe.

“Gidajen gona da dama da ake kiwon kaji a jihar, sun rufe sannan kuma kwan da ake kawo wa jihar daga kudancin kasar nan, ya ragu sakamakon tsadar da man fetur ya yi, sannan akasari, mun dogara ne a kan man dizel da muke zuba wa injin janareto,” in ji shi.

Saboda haka, a yanzu farashin man dizel ya karu daga naira 750 zuwa Naira 1, 050 kowace lita, wanda hakan ya kara jawo rufe gidajen gonar da ake kiwata wadannan kaji.

Shi ma wani manajan gidan gona da ake kiwata kaji na gidan gonar lSani Ahmadu, ya danganta karancin kwan kan wannan tsada ta man fetur da kuma tashin farashin abincinsu.

Kazalika ya kara da cewa, bukatar da ake da ita ta kwan a fadin jihar, ta fi karfin gidan gonar su iya samar da yawan kwan da ake bukata a jihar.

“Bukatar na da yawan gaske kuma ba mu da kwan da ake bukata a halin yanzu, ya kara da cewa, zuwan masu yi wa kasa hidima a sansaninsu da ke jihar, ya kara bukatar kwan a sansanin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Samuel Eto’o Na Fuskantar Zarge-zarge A Kamaru

Next Post

An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

Related

Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Noma Da Kiwo

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

7 days ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

7 days ago
Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya
Noma Da Kiwo

Dalilin Kwararru Na Bukatar Kafa Cibiyoyin Bincike Kan Nau’ikan Dabbobi A Nijeriya

2 weeks ago
Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci
Noma Da Kiwo

Tinubu Ya Kaddamar Da Sabon Shirin Aikin Noma Don Samar Da Wadataccen Abinci

2 weeks ago
Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar
Noma Da Kiwo

Madarar Shanu Da Nijeriya Ke Samarwa Ta Karu Da Tan Miliyan 1.4 A Shekara Biyar

3 weeks ago
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (6)
Noma Da Kiwo

Nijeriya Da Brazil Sun Ƙulla Yarjejeniyar Horar Da Matasa Kiwon Dabbobi

4 weeks ago
Next Post
An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

An Horas Da Makiyaya Dabarun Shuka Ciyawar Shanu A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Dangote

Dalilin Da Ya Sa Dangote Ya Jinjina Wa Hukumar NPA

July 18, 2025
Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

Philippines Na Zama Tushen Tashin Hankali A Tekun Kudancin Kasar Sin

July 18, 2025
2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

2027: Atiku, Obi Da Amaechi Za Su Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Takarar Shugaban Kasa A ADC

July 18, 2025
Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

Kasar Sin Ta Gano Ma’adanin Yuraniyom Mafi Daraja A Karkashin Kasa Mai Zurfi

July 18, 2025
majalisar kasa

Kirkirar Sabbin Jihohi Da Kananan Hukumomi Sun Dabaibaye Sauraron Jin Ra’ayoyin Gyaran Tsarin Mulki

July 18, 2025
Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

Ƙwallon Mata: Nijeriya Ta Lallasa Zambia Da Ci 5-0

July 18, 2025
Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

Yawan Jarin Waje Da Sin Ta Samu Ya Haura Dalar Amurka Biliyan 700

July 18, 2025
A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

A Karon Farko Dino Melaye Ya Bayyana A Gaban Kotu A Matsayin Lauya

July 18, 2025
Biyan Tukuici: Gwamna Yusuf Ya Ƙaddamar Da Tallafin Naira 50,000 Ga Mata 5,200 Duk Wata A Kano

Biyan ‘Yan Fansho Naira Biliyan 22: NUP Da NLC Sun Bukaci A Yi Koyi Da Gwamna Abba

July 18, 2025
Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

Sin Ta Yi Allah Wadai Da Hare-Haren Da Isra’ila Ta Kai Syria

July 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.