• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rububin Sayen Kuri’u A Tsakanin ‘Yan Siyasa – Kwamishinan Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
sayen kuri'u
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan hukumar zaben Jihar Ribas, Obo Effanga ya bayyana cewa babban abin da ke rusa ci gaban kasar nan shi ne, yadda mafi yawancin ‘yan siyasan Nijeriya suke sayan kuri’u.

Ya ce hukumar zabe tana gudanar da wasu shirye-shirye masu karfi da zai tabbar dakile wannan mummunar dabi’a.

  • Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya

A kwanan nan ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tana nada Effanga a matsayin kwamishinan zaben Jihar Ribas. Ya bayyana hakan ne a lokacin wata liyafa da ta gudana a Abuja.

Ya ce, “A yanzu yadda ‘yan siyasa ke sayan kuri’u ya nuna cewa wadannan kuri’u suna da matukar muhimmanci kuma dole da su ne za su iya samun nasara a zabe. Saboda a yanzu ana kirga kuri’un mutane shi ya sa ‘yan siyasa suke bin duk wata hanya da za su sayi kuri’u,” in ji Effanga.

Ya kara da cewa ‘yan siyasa sun gano cewa watakila wannan ce hanya mafi saukin samun nasara shi ya sa suke bai wa mutane kudi domin su saye kuri’unsu.
Ya ce a bangaren INEC, duk mutumin da ya cancanci jefa kuri’a za a bar shi ya yi zabe. A cewarsa, lokacin da mutum ya yi zabe za a kirga kuri’arsa sa’ilin da aka kammala zabe.

Labarai Masu Nasaba

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

Ya ci gaba da cewa dabi’ar sayan kuri’a tana matukar kawo matsala ga ci gaban kasa.
Kwamishinan zabe ya ce duk dan Nijeriya da yake da sha’awar samun dimokuradiyya mai inganci, ya tabbatar da cewa bai sayar da kuri’arsa ba. Ya ce hakan zai iya faruwa ne a lokacin da aka fadakar da ‘yan Nijeriya illar sayar da kuri’arsu.

Effanga ya ce gudanar da zabe a kan tsari shi ke karfafa dimokuradiyya, wannan shi ya sa manyan mutane a Nijeriya suka tashi tsaye na ganin cewa hukumar zabe ba ta samu cin gashin kanta ba, wannan ne ya sa mafi yawancin zaben kananan hukumomi ake tafka magudi na ganin sai jam’iyya mai mulki ta samu nasara.

Kwamishinan zabe ya bayyana cewa yin rajistar zabe fiye da daya ya janyo mafi yawancin mutane ba za su samu nasarar jefa kuri’a ba. Ya ce an dakatar da katin zabe na mafi yawancin mutane saboda sun yi rajista fiye da guda daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Rantsar Da Dakta Bello A Matsayin Shugaban Hukumar Raba Dai-Dai

Next Post

Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

Related

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027
Tambarin Dimokuradiyya

Shugaban INEC Ya Yi Kira Da A Sake Fasalin Tsarin Zabe Gabanin 2027

2 weeks ago
sayen kuri'u
Tambarin Dimokuradiyya

Amfani Da Karfin Gwamnati Kan ‘Yan Adawa Zai Jawo Wa Tinubu Illa A 2027 – Sule Lamido

2 weeks ago
‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Siyasa Na Gwagwarmaya Ne Kadai Wajen Neman Mukami Ba Wai Don Talakawa Ba — Bafarawa

2 weeks ago
Gwamnoni 9 Da Har Yanzu Ba Su Babe Da Iyayen Gidansu Ba
Tambarin Dimokuradiyya

Jihohi Sun Samu Naira Tiriliyan 1 Na Kudaden Kananan Hukumomi A Zango Na Daya

3 weeks ago
2027: Baba-Ahmed Ya Bukaci Tinubu Ya Janye, Ya Bar Matasa Su Yi Takara 
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Babu Dan Takarar Da Zai Iya Cin Zabe Ba Tare Da Goyon Bayan Arewa Ba – Baba Ahmed

3 weeks ago
arewa
Tambarin Dimokuradiyya

Kawunan Shugabannin Arewa Sun Rabu Kan Siyasar 2027

3 weeks ago
Next Post
Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

Yadda 'Hackers' Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.