• English
  • Business News
Tuesday, July 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Rububin Sayen Kuri’u A Tsakanin ‘Yan Siyasa – Kwamishinan Zabe

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Tambarin Dimokuradiyya
0
sayen kuri'u
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kwamishinan hukumar zaben Jihar Ribas, Obo Effanga ya bayyana cewa babban abin da ke rusa ci gaban kasar nan shi ne, yadda mafi yawancin ‘yan siyasan Nijeriya suke sayan kuri’u.

Ya ce hukumar zabe tana gudanar da wasu shirye-shirye masu karfi da zai tabbar dakile wannan mummunar dabi’a.

  • Hadin Gwiwar Afirka Da Sin Na Taimakawa Raya Duniya

A kwanan nan ne hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) tana nada Effanga a matsayin kwamishinan zaben Jihar Ribas. Ya bayyana hakan ne a lokacin wata liyafa da ta gudana a Abuja.

Ya ce, “A yanzu yadda ‘yan siyasa ke sayan kuri’u ya nuna cewa wadannan kuri’u suna da matukar muhimmanci kuma dole da su ne za su iya samun nasara a zabe. Saboda a yanzu ana kirga kuri’un mutane shi ya sa ‘yan siyasa suke bin duk wata hanya da za su sayi kuri’u,” in ji Effanga.

Ya kara da cewa ‘yan siyasa sun gano cewa watakila wannan ce hanya mafi saukin samun nasara shi ya sa suke bai wa mutane kudi domin su saye kuri’unsu.
Ya ce a bangaren INEC, duk mutumin da ya cancanci jefa kuri’a za a bar shi ya yi zabe. A cewarsa, lokacin da mutum ya yi zabe za a kirga kuri’arsa sa’ilin da aka kammala zabe.

Labarai Masu Nasaba

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

Ya ci gaba da cewa dabi’ar sayan kuri’a tana matukar kawo matsala ga ci gaban kasa.
Kwamishinan zabe ya ce duk dan Nijeriya da yake da sha’awar samun dimokuradiyya mai inganci, ya tabbatar da cewa bai sayar da kuri’arsa ba. Ya ce hakan zai iya faruwa ne a lokacin da aka fadakar da ‘yan Nijeriya illar sayar da kuri’arsu.

Effanga ya ce gudanar da zabe a kan tsari shi ke karfafa dimokuradiyya, wannan shi ya sa manyan mutane a Nijeriya suka tashi tsaye na ganin cewa hukumar zabe ba ta samu cin gashin kanta ba, wannan ne ya sa mafi yawancin zaben kananan hukumomi ake tafka magudi na ganin sai jam’iyya mai mulki ta samu nasara.

Kwamishinan zabe ya bayyana cewa yin rajistar zabe fiye da daya ya janyo mafi yawancin mutane ba za su samu nasarar jefa kuri’a ba. Ya ce an dakatar da katin zabe na mafi yawancin mutane saboda sun yi rajista fiye da guda daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Buhari Ya Rantsar Da Dakta Bello A Matsayin Shugaban Hukumar Raba Dai-Dai

Next Post

Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

Related

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai
Tambarin Dimokuradiyya

Cacar Baki Ta Kaure Tsakanin Fadar Shugaban Kasa Da Peter Obi Kan Tallafin Mai

2 weeks ago
APC
Tambarin Dimokuradiyya

Sauya Sheka Ya Sa APC Ta Samu Gagarumin Rinjaye A Majalisun Tarayya

2 weeks ago
Adawa
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

3 weeks ago
‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yancin Kananan Hukumomi: Shekara Daya Da Hukuncin Kotun Koli Amma Ba A Aiwatar Ba

1 month ago
Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?
Tambarin Dimokuradiyya

Ko Kwamitin Saraki Zai Iya Ceto PDP Daga Rikicin Cikin Gida?

1 month ago
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Tambarin Dimokuradiyya

‘Yan Adawa Na Cacakar APC A Yankin Arewa Maso Yamma Bisa Goyon Bayan Tazarcen Tinubu

1 month ago
Next Post
Yadda ‘Hackers’ Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

Yadda 'Hackers' Ke Amfani Da Smishing Wajen Yin Kutse

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.