• English
  • Business News
Sunday, August 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dalilin Ware Naira Biliyan 19.5 Da Asusun Bunkasa Aikin Noma Ya Yi

by Abubakar Abba
3 weeks ago
in Noma Da Kiwo
0
Wa’adin Da Tinubu Ya Bai Wa Manoman Da Suka Ci Bashin ‘Anchor Borrowers’ Ya Cika
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Bunkasa Aikin Noma na Kasa (NADF), ya ware Naira biliyan 19.5, domin samar da garabasar kashi 50 cikin 100, kan Irin noma da takin zamani da kuma maganin feshe.

A cewar Asusun ya yi haka ne, domin sama wa manoma kimanin 50,000 sauki, wanda za a gudanar a karkashin shirin kara habaka aikin noma na kasa.

  • Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • “Sin Daya Tak A Duniya”, Matsaya Ce Da Al’ummun Duniya Suka Kafe Kai Da Fata a Kai

An zabo amfanin gona hazu ne da suka hada da; Shinkafa, Masara, Rogo da kuma Waken Suya.

Kazalika, za a gudanar da shirin ne a daukacin shiyoyi shida na fadin wannan kasa.

A jawabinsa a wajen kaddamar da aikin, wanda aka gudanar a a babban birnin tarayyar Abuja, Babban Daraktan Asusun, Mohammed Abu Ibrahim ya bayyana cewa; an tsara shirin ne, musamman domin tallafa wa manoman kasar nan da kara samar da wadataccen abinci a kasar da kuma kara habaka tattalin arzikin kasar baki-daya.

Labarai Masu Nasaba

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

Ya kara da cewa, Asusun ya kuma gano fannonin aikin noman kasar da ya kamata a kara bunkasa su, wanda hakan ya sanya Asusun ya dauki wannan mataki.

Ya ci gaba da cewa, duba da irin amfanin gonar da manoma ke nomawa a kasar, musamman kananan manoma da kuma ribar da suke samu daga fannin, wani abu ne da Asusun ya dauka da ke da matukar muhimmanci, wanda kuma hakan ne ya kara bai wa Asusun kwarin guiwar shirin fara kaddamar da aikin.

Shi kuwa a nasa jawabin, Lanre Wilton-Wadell, mai taimaka wa Babban Sakataren a Asusun, ya yi bayani kan yadda za a gudanar da aikin.

Ya bayyana cewa, Asusun zai bayar da kashi 100 na Irin noma da takin zanani da kuma magungunan feshi, wanda za a gudanar a karkashin shirin aikin noma na kasa.

Ya ci gaba da cewa, bayan an girbe amfanin gonar, Asusun zai biya wadanda suka sarrafa amfanin gonar kashi 50 cikin 100 na jimillar kayan aikin noman da aka kashe kudade a kansu.

“Mun fito da wannan shiri ne, duba da cewa; ana samun rarrabuwa a kasuwannin kasar da kuma samar da dama ga masu sarrafa amfanin gona tare da kara habaka amfanin da manoman kasar ke nomawa,” in ji Lanre.

“Mun yi duba a kan hanyar da zamu tabbatar da mun hada manoma, yadda za su samu damar kai amfanin da suka noma zuwa kasuwanni kai tsaye tare kuma da samun damar ci gaba da sarrafa amfanin gonar da aka girbe,” a cewar Lanre.

Ya bayyana cewa, kashi 70 cikin 100 na manoman kasar, musamman kanannan manoma na fuskantar kalubalen ilimi, kan ingantaccen Irin noman da ya kamata su yi amfani da shi da kwarewar aikin noma.

Kazalika, ya sanar da cewa; su ma masu sarrafa amfanin gonar, ba sa iya samun ci gaba da samun amfanin da za su sarrafa, saboda ayyuakan masu tare manoman suna saye amfanin da suka noma a farashi mai sauki


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Noma
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Next Post

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

Related

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir
Noma Da Kiwo

Manyan Ƙalubale Takwas Da Ke Shafar Farashin Tumatir

1 day ago
Sin Ta Gaggauta Aikin Gyara Da Kyautata Ababen Aikin Gona
Noma Da Kiwo

Asusun NADF, OCP Da Gwamnatin Katsina Sun Kaddamar Da Noman Hekta 50

1 week ago
Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Na Shirin Dakatar Da Shigo Da Kifi Daga Ketare

1 week ago
Abinci
Noma Da Kiwo

Dalilin Gwamnatin Tarayya Na Yin Hadaka Da Jihar Nasarawa Don Bunkasa Noma

2 weeks ago
Shettima
Noma Da Kiwo

Nijeriya Za Ta Rika Samun Naira Tiriliyan Uku A Aikin Tatsar Rogo Duk Shekara – Kashim

2 weeks ago
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

3 weeks ago
Next Post
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

LABARAI MASU NASABA

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

ADC Ta Yi Allah-wadai Da Rufe Gidan Rediyon Badeggi FM A Neja

August 3, 2025
Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

Gwamnatin Katsina Ta Gabatar Da Matsayarta A Taron Jin Ra’ayiyin Jama’a

August 3, 2025
Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

Borno Za Ta Sake Tsugunar Da ‘Yan Gudun Hijira 5,000 Kafin Damuna Ta Kare

August 3, 2025
Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

Samun Kuɗi Ya Fi Samun Ɗaukaka Wahala A Kannywood -Baba Sadiƙ

August 3, 2025
Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

Ministan Yaɗa Labarai Ya Buƙaci A Kwantar Da Hankali Kan Dakatar Da Gidan Rediyon Badeggi FM

August 3, 2025
Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

Hanyoyin Da Za A Bi A Rage Yawan Zawarawa

August 3, 2025
Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

Ban Yi Danasanin Shiga Harkar Fim Ba – Baba Ƙarami

August 3, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

Gwamnatin Tarayya Za Ta Aiwatar da Shirin Daƙile Sulalewar Kuɗaɗen Haraji

August 3, 2025
Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

Dalilin Da Ya Sa Kashi 50 Na Ƙanana Da Matsakaitan Sana’oi Ke Durƙushewa A Nijeriya– FRC

August 3, 2025
Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

Sanata Buba Ya ƙaryata Jita-jitar Cewa Majalisa Ta Amince da ƙirƙiro Sabbin Jihohi 12

August 2, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.