ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rashin Ganin Shugabannin APC Yayin Ziyarar Shettima A Kano Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara

by Yusuf Shuaibu
12 months ago
Shettima

Rashin ganin shugabannin jam’iyyar APC na Jihar Kano a ziyarar ta’aziyya da Mataimakin Shugaban Kasa, Kashim Shettima ya kai ga iyalin Marigayin Alhaji Aminu Dantata, ya haifar da zazzafar muhawara a cikin jam’iyyar.

Rahotanni sun bayyana cewa yayin da jami’an gwamnatin Jihar Kano da ke cikin jam’iyyar NNPP suka yi tururuwan tarbar mataimakin shugaban kasan, ba a ga duriyar shugabannin jam’iyyar APC na jihar ba a wurin wannan taron da ya gudana a ranar Alhamis.

  • Sin Na Goyon Bayan G20 Ta Ci Gaba Da Ba Da Kyakkyawar Gudummawa
  • Majalisar Tarayya Ta Karrama NPA Da Kyautar Gaskiya Da Riƙon Amana Ta 2025

Wannan lamari ya haifar da alamomin tambaya, yayin da wasu suna zargin cewa akwai rashi jituwa a cikin APC bayan saukar Dakta Abdullahi Umar Ganduje a matsayin shugaban jam’iyyar na kasa.

ADVERTISEMENT

Ganduje ya kasance tsohon gwamnan Jihar Kano, wanda har yanzu ke da tasiri a cikin harkokin siyasar jihar, ya yi murabus daga mukamin shugaban APC a ranar 27 ga Yuni, sakamakon lissafin siyasa da shirye-shiryen da aka yi a cikin jam’iyyar kafin zaben 2027.

Masana harkokin siyasa suna ganin cewa wasu daga cikin shugabannin APC a jihar ba su yi farin ciki da murabus din Ganduje a matsayin shugaban APC na kasa ba, kuma suna ganin cewa Shettima ya taka rawa wajen tilasta wa Ganduje yin murabus.

LABARAI MASU NASABA

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

Rahotanin sun bayyana cewa Shettima ya ziyarci Kano ne don yin ta’aziyyar rasuwar hamshakin dan kasuwa, Alhaji Aminu Dantata, wanda ya rasu kwanan nan, da kuma jajanta wa mutanen Kano kan wannan rashi.

Haka kuma rahotannin sun bayyana cewa a irin wadannan manyan taruka a Nijeriya, an saba ganin shugabannin jam’iyya da goyon baya su tarbi manyan jami’ai kamar mataimakin shugaban kasa, amma lamarin ya bambanta yayin ziyarar Shettima, wanda ya haifar da zazzafar muhawara.

Da yake musanta cewa akwai rikice-rikice na cikin gida a jam’iyyar, sakataren APC a Kano, Ibrahim Zakari Sarina, ya shaida cewa rashin halartar shugabannin jam’iyyar a ziyarar ta’aziyya da mataimakin shugaban kasa ya kawo Kano ya faru ne sakamakon rashin sadarwa.

“Mun san cewa ziyarar za ta kasance, amma sadarwa ta zo a makare. Kafin mu shirya, mun riga mun makara. Saboda gwamnatin ta riga ta shirya tun kafin mu isa wurin.

“A gaskiya wannan abu ba ya da alaka da kowanne irin lamari na siyasa. An sanar da mu a makare, har ita kanta gwamnatin jihar a makare aka sanar da ita. Daga baya mun aike da godyarmu ga mataimakin shugaban kasa bisa ziyara, kuma ya fahimci yanayin sosai,” in ji Sarina.

Duk da wannan bayani, an samu rarrabuwan kai a tsakanin ‘yan siyasa a jihar.

Wani jigo a APC a yankin Gwale, Abdullahi Kabiru, ya bayyana cewa ya ji takaicin rashin halartar shugabannin jam’iyyar. “Wannan shi ne mataimakin shugaban kasa na wannan kasa, kuma ba mu kasa shirya tarba a gare shi ba? Wannan ba karamin kuskure ba ne. Ko da an samu rashin kyakkyawan sadarwa, yana nuna cewa akwai rashin hadin kai,” in ji shi.

Ita kuwa wata mai kishin jam’iyya, Amina Sani daga Tarauni, ra’ayinta ya sha bamban. Ta ce, “Na gamsu da bayanin da jam’iyyar ta bayar. Abubuwa suna faruwa a siyasa, musamman lokacin da jadawalin ke canzawa. Amma ina fatan hakan ba zai zama sabani ba. Dole ne mu girmama shugabanninmu da ofisoshinsu ba tare da la’akari da kowanne bambancin siyasa ba.”

Da yake jawabi kan lamarnin, wani masana harkokin siyasa, Dakta Musa Auwal ya bayyana cewa dole ne jam’iyyar ta yi taka-tsantsan. “Ko lamarin ya faru da gangan ko akasin haka, a duk lokacin da aka samu rarrabukan na manyan shugabannin jam’iyya a fili, yana rage karfin jam’iyyar kuma yana karfafa ‘yan adawa.

“APC a Kano tana taka muhimmiyar rawa a siyasan kasar nan, kuma kowanne takaddama da ke tasowa Kano na shugabancin ko na siyasa na iya zama babban lamari da ke daukan tsawon lokaci ana tattaunawa a kai,” in ji shi.

Shettima
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

makarfi
Tambarin Dimokuradiyya

Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi

June 26, 2026
Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
Tambarin Dimokuradiyya

An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

June 26, 2026
Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
Tambarin Dimokuradiyya

Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

June 19, 2026
Next Post
Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

Nazari Kan Taraktoci 2,000 Da Tinubu Ya Kaddamar Don Bunkasa Noma

LABARAI MASU NASABA

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

Taƙaddamar Kafa Hukumar Bogi: Tinubu Ya Umarci A Yi Binciken Ƙwaƙwaf

July 10, 2026
Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

Ana Ci Gaba Da Tafka Muhawara Kan Shirin Gwamnati Na Haramta Masana’atun Sarrafa Robobi

July 10, 2026
Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

Asusun IMF Ya Rage Hasashen Bunkasar Tattalin Arzikin Duniya, Ya Kuma Kara Na Sin

July 9, 2026
Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

Alkaluman Farashin Kayayyakin Masarufi Na Kasar Sin Sun Karu Da Kaso 1 A Watan Yuni

July 9, 2026
‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

‘Yansandan Jihohi Za Su Bai Wa Gwamnoni Cikakken Iko Wajen Yaƙi Da Matsalar Tsaro — Gwamna Dauda

July 9, 2026
Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

Taron Intanet Na Sin Karo Na 25 Ya Bayyana Yadda Ake Amfani Da Fasahar AI A Rayuwar Yau Da Kullum

July 9, 2026
Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

Tunanin Xi Jinping kan JKS: Hikimar Mulki Ta Farfado Da Kasa Da Kuma Tasirinta A Duniya

July 9, 2026
Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

Rashin Tsaro: Tinubu Ya Gana Da Shugabannin Hukumomin Tsaro

July 9, 2026
Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

Motoci Masu Aiki Da Lantarki Kirar Kasar Sin Na Kara Samun Tagomashi A Kasuwannin Duniya

July 9, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

Gwamnatin Tarayya Ta Ɗaga Albashin Sojoji Daga Naira 49,000 Zuwa Naira 100,000 – Ministan Tsaro

July 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.