• English
  • Business News
Sunday, October 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Dalla-dallar Yadda Aka Kashe Kudin Tallafin Mai

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
Tallafin Mai

A cikin rahoton kwamitin tattalin arziki na Nijeriya (NESG) ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kashe jimillar tsabar kudi na Naira tiriliyan 3.64 wajen bayar da tallafin man fetur tun daga shekarar 2015 har zuwa 2021.

Haka kuma rahoton ya kara da cewa adadin kudaden da gwamnatin tarayya ta kashe wajen biyan tallafin man fetur ya karu da naira biliyan 307 a shekarar 2015 zuwa naira tiriliyon 1.77 a shekarar 2021.

  • Kotu Ta Daure Matashin Da Ya Tura Wa Matar Aure Hotunan Batsa A Kebbi
  • Tomas Bach Ya Taya CMG Murna

Wanda ya nuna cewa an samu karin kashi 477 a cikin shekaru shida.

Duka wadannan suna cikin rahoton NESG na tattalin arziki na shekarar 2022 mai taken ‘Sake fasalin tattalin arzikin ta yadda zai inganta’, wanda ya bayyana adadin kudaden da gwamnatin tarayya za ta kashe wajen biyan tallafin man fetur a 2022 duk da barazanar da ake samu na farashin danyen mai a kasuwar duniya.

A makon da ya gabata ne, gwamnatin tarayya ta amince da kashe naira tiriliyan 3 wajen bayar da tallafin man fetur a tsakanin watan Yuli zuwa Disambar 2022.

LABARAI MASU NASABA

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

Tun a farko, aiwatar da dokar man fetur wanda zai kawo karshen bayar da tallafin man fetur zai fara aiki ne a watan Fabrairun 2022, amma sai aka dage zuwa watan Yulin 2022, sakamakon matsinlambar daga kungiyar kwadugo ta kasa (NLC) da kungiyar ‘yan kasuwa (TUC), aka kara watanni 18.

Sai dai kuma NESG ta bayyana cewa rahoton 2021 yana cike da kalubale da ya turnike na shekarar 2022, sakamakon matsalolin da harkokin kasuwanci suka fuskanta saboda annoba da ta sa sai da gwamnatin tarayya ta bayar da tallafi na jinkai ga ‘yan kasa.

An dai kiyasta cewa tattalin arzikin zai karu da kashi 3.2 a cikin wannan shekarar.

Hakazalika, ofishin Akanta Janar na kasa (AGF) ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kashe naira tiriliyan 4.194 wajen bayar da tallafin mai ga ‘yan kasuwa a tsakanin watan Junairun 2017 zuwa watan Yunin 2022.

Ofishin ya kara da cewa an biya naira biliyan 126.539 a watan Disambar 2017, an biya naira biliyan 691.586 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2018, an biya naira biliyan 537.209 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2019, an biya naira biliyan 133.625 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2020, sannan an biya naira biliyan 1.159 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2021, yayin da aka biya naira tiriliyan 1.545 a tsakanin watan Janairu zuwa watan Yunin 2022.

Jerin biyan kudaden tallafin yana nan a shafi na biyu a cikin kundin da Daraktan sa ido na ofishin Akanta Janar, Mista Sylba Okolieaboh ya mika wa kwamitin majalisa da ke bincike kan tallafin mai karkashin jagorancin Hon. Abdulkadir Abdullahi.

Haka ita ma ministar kudi da kasafi da tsare-tsaren kasa, Zainab Ahme ta bayyana cewa a duk rana gwamnatin tarayya tana kashi naira biliyan 18.39 wajen bayar da tallafin man fetur.

Ministar ta bayyana hakan ne a gaban kwamitin majalisar wakilai da ke binciken bayar da tallafin mai tun daga shakarar 2013 har zuwa 2022.

A farkon rabin shakarar 2022, kamfanin mai na kasa (NNPC) ya ce ya samu naira tiriliyan 2.6 a wajen sayar da danyan mai.

Sai dai gwamnatin tarayya tana tsammanin za ta kashe naira tiriliyan 6.7 wajen bayar da tallafin mai a 2023. A cikin rahoton NNPC, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kashe naira tiriliyan 4.838 wajen bayar da tallafin mai a cikin shekaru bakwai har zuwa watan Mayun 2022.

Rahoton ya kara da cewa a duk wata ana samun karuwar farashin tallafin man da kashi 989 daidai da naira biliyan 254.8 har zuwa watan Mayun 2022, wanda aka samu naira biliyan 23.4 a karshen 2015.

Rahoton NNPC ya nuna cewa an kashe naira biliyan 99.00 da naira biliyan 141.63 da naira biliyan 722.30 da naira biliyan 578.07 da naira biliyan 133.73, wadanda aka kashe a shekarun 2016, 2017, 2018, 2019 da 2020, yayin da aka kashe naira tiriliyan 1.573 a 2021.

A 2022 kadai a tsakanin watan Janairu zuwa Fabrairu, an kashe naira biliyan 396.72 wajen bayar da tallafin man fetur.

Majalisar kasa ta amince a kashe zunzurutun kudade da suka kai naira tiriliyan 4 kan bayar da tallafin mai a 2022.

Gwamnatin tarayya ta bakin ministan yada labarai, Alhaji Lai Mohammed ta kashe naira tiriliyan 10.413 wajen bayar da tallafin mai a tsakanin 2006 zuwa 2019.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya
Da ɗumi-ɗuminsa

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna
Manyan Labarai

Ƴan Bindiga Sun Kai Hari Ofishin Ƴansanda, Sun Kashe 2 A Kaduna

October 18, 2025
Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi
Manyan Labarai

Yajin Aikin ASUU: Majalisar Dattawa Ta Tsoma Baki, Za Ta Gana Da Ministan Ilimi

October 18, 2025
Next Post
Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

LABARAI MASU NASABA

gombe

Ɗaliban Jihar Gombe Sun Samu Ƙarin Kashi 100 Na Kuɗin Tallafin Karatu

October 18, 2025
Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

Ɗaliban Fasaha Sun Ɓullo Da Dabarar Tsaro Ta Harkar Noma

October 18, 2025
An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

An Bude Taron Sanin Makamar Aiki Na Cika Shekaru 80 Da Kafuwar MDD A Wuhan Na Kasar Sin

October 18, 2025
Tsadar Rayuwa Da Karuwar Ta’addanci Na Ci Gaba Da Tagayyara ‘Yan Nijeriya

DHQ Ta Ƙaryata Rahoton Yunƙurin Yi Wa Tinubu Juyin Mulki

October 18, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Kai Samame Maboyar ‘Yan Ta’adda, Sun Kwato Miyagun Kwayoyi A Gombe

October 18, 2025
Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

Kamfanin Gine-Gine Na CCECC Ya Fara Gina Wani Titin Mota Da Zai Rage Cunkoso A Birnin Abuja Na Tarayyar Najeriya

October 18, 2025
ASUU

Cikin Wata 9 Farfesoshi 309 Sun Bar Aiki A Jami’o’in Gwamnati, In Ji ASUU

October 18, 2025
Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

Masanin Ilimin Physics Chen Ning Yang Ya Rasu Yana Da Shekaru 103

October 18, 2025
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

October 18, 2025
Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

Kasar Sin Ta Gargadi Amurka Game Da Yunkurin Samarwa Yankin Taiwan Makamai

October 18, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.