ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

by Leadership Hausa
4 years ago
Taki

Manoman Nijeriya kamar takwarorinsu na wasu kasashen Afrika suna fama da matsalar karancin Takin zamani, wanda shi ne daya daga cikin abubuwa masu muhimmanci da ake bukata a gona don samar da abinci tare da kawo karshen matsalar rashin abinci da ake fuskanta a kasar nan dama nahiyar Afrika gaba daya.

Dumamar yanayi da matsalolin da ya haifar ya kai ga tilasta amfani da Takin zamani a gonakinmu don kara bunkasa albarkar kasa wanda hakan zai kai ga samar da yabanya mai yawa.

  • Sin Ta Yi Watsi Da Rahoton MDD Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama A Xinjiang
  • Jami’an KAROTA Sun Cafke Tirela Makare Da Giya A Kano

Tabbas amfani da Takin zaman ya taimaka wajen samun karin girbin abin da aka shuka wanda hakan kuma yana taimakawa wajen tabbatar da wadatar abinci a fadin kasar nan dama yankin Afriki gaba daya.

ADVERTISEMENT

Amma kuma duk da muhimmanci Takin zamani ga harkar noma a wannan lokacin, Takin ya yi matukar karanci ga shi kuma da tsananin tsada, Taki na neman gagarar kanana da matsakaitar manona, musamman ganin yadda aka siyasantar da rabawa in gwamnati ta samar don manona su amfana.

Bayani ya nuna cewa, a halin yanzu farashin Takin NPK da Urea ya kai Naira 20, 000 a kasuwannin mu.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Abin takaici a nan shi ne yadda tallafin da gwamnati ke ikirarin tana sanya wa don amfanar talaka baya isa ga wadanda suka fi bukata, Takin ya fada hannun mugayen ‘yan kasuwa wadanda suka tsawalla masa kudi, suka kuma boye shi don a wasu wuraren ko da kudin ka samun Takin yana da mautukar wahala ga kanana da matsaikaitan manoma.

Mun damu matuka a kan karancin Takin zamani don kuwa hakan ya kara matsalar da manoman mu ke ciki ne, musamman ganin suna fuskantar matsaloli a wasu wuraren da suka hada da ayyukan ‘yanta’adda, wadannan matsaloli ne masu tayar da hankula don a wasu wuraren harkar noman ma ta tsaya cik.

Saboda haka fuskantar tsadar Takin zamani a irin wannan lokacin abu ne da zai dagula lissafin manoma gaba daya zai kuma haifar da karancin abinci a cikin al’umma.

Kwanakin baya, babban sakataren Kungiyar Masu Sarrafa Takin Zamani a Nijeriya, (FEPSAN), Gideon Nagedu ya yi ikirarin cewa, Takin Urea, ne kadai ake fuskantar karancinsa a Nijeriya, wai kuma hakan na faruwa ne saboda karancin Iskar Gas da ake fuskanta a Nijeriya, sai dai kuma wasu bayanai sun nuna cewa karancin Takin da ake fuskanta ba wai ya tsaya a kan Takin Urea kada ba ne.

 Duk kuwa cewa, muna sane da cewa, annobar cutar Korona da aka fuskanta a Duniya da yadda aka takaita zirga-zirga da kuma yakin da ake yi a halin yanzu a tsakanin Rasha da Yukiren ya taimaka wajen haifar da karancin Takin zamani, amma muna kira ga Gwamnati a dukkan matakai da su tabbatar da daukar matakan da suka dace don kawo kaeshen karancin Takin da ake fuskanta a halin yanzu don kuwa barazana ce ga samar da wadataccen abinci ga al’umma.

A daida wannan lokaci kuma ya kamata mu ne jin dalilin da ya sa Kamfanonin Takin Zamani na cikin gida suka kasa fuskantar samar da issasun takin zamanin ga manoman Nijeriya.

In har da gaske ake yi na kokarin samar da issashe Takin zamani ga manoman Nijeriya to ya zama tilas kamfanonin takin zmani na cikin gida su farfado don ganin sun cike gibin Takin da ke bukata a cikin gida har a fara tallafa wa wasu kasashen Afrika.

Wadannan matakan sun zama dole saboda ganin muhimmancin Takin zamani ga harkar noma a wannan lokacin.

Idan za a iya tunawa a shekarar 2016, gwamnatin tarayya ta sanya hannun a wata yarjejeniyar samar da Takin zamani tsakaninta da wani kamfanin kasar Morocco, an shirya amfani da Iskar Gas ta Nijeriya da kuma sinadarin phosphate daga kasar Maroco don samar da issashen Takin.

Gwamnati ta bayyana cewa, yarjejeniyar ta samar da shirin yadda za a yi amfani da Iskar Gas na Nijeriya da Phosphate daga kasar Moroco don samar da Tan 750,000 na sinadarin Ammonia da tan Miliyan daya na Takin Phosphate a duk shekara daga nan zuwa shekarar 2025.

Babu tantama zuba jari a bangaren samar da Takin zamani zai matukar taimakawa Nijeriya a kokarinta na samar da isashen abinci ga al’ummarta hakan kuma zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.

Dole a wannan gabar a yaba wa Kamfanin Dangote a bisa kokarinshi na samar da takin zamani a cikin gida ta yadda ya kafa katafaren kamfanin Takin zamani da aka kiyasta kudinsa ya kai Dala Biliyan 2.5.

Mun tabbatar da cewa, kamar mafi yawa ‘yan Nijeriya, Kamfanin Taki na Dangote zai bayar da gaggarumar gudummawa wajen ganin an samu wadataccen Takin zamani a kasa yayin da za a iya fitar da rarrar zuwa kasashe Afrika da sauran kasashen duniya.

Akwai dalilai da dama da dole gwamnati ta sanya hankali a kula da bangaren harkar noma, ciki kuwa akwai cewa a halin yanzu bangaren yana samar da aikin yi ga fiye da kashi 33 na ‘yan Nijeriya, gona ne kuma bangaren tattalin arzikin kasa da ya fi kowanne samar wa da al’umma aikin yi, don haka dole gwamnati ta sanya ido a kan ganin bunkasar bangaren.

Taki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Tallafa Wa Yara Masu Buƙatu Na Musamman Shi Ne Burina
  • Leadership Hausa
    Dole Mata Su Rungumi Sana’o’i Domin Tsira Daga Takaicin Zamani —Ramatu Bello
  • Leadership Hausa
    Batun Dakile Shan Taba Sigari A Tsakanin Yara A Nijeriya
  • Leadership Hausa
    Har Yanzu Akwai Sauran Rina A Kaba Game Da Makomar Yara A Nijeriya

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.