ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

by Leadership Hausa
4 years ago
Taki

Manoman Nijeriya kamar takwarorinsu na wasu kasashen Afrika suna fama da matsalar karancin Takin zamani, wanda shi ne daya daga cikin abubuwa masu muhimmanci da ake bukata a gona don samar da abinci tare da kawo karshen matsalar rashin abinci da ake fuskanta a kasar nan dama nahiyar Afrika gaba daya.

Dumamar yanayi da matsalolin da ya haifar ya kai ga tilasta amfani da Takin zamani a gonakinmu don kara bunkasa albarkar kasa wanda hakan zai kai ga samar da yabanya mai yawa.

  • Sin Ta Yi Watsi Da Rahoton MDD Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama A Xinjiang
  • Jami’an KAROTA Sun Cafke Tirela Makare Da Giya A Kano

Tabbas amfani da Takin zaman ya taimaka wajen samun karin girbin abin da aka shuka wanda hakan kuma yana taimakawa wajen tabbatar da wadatar abinci a fadin kasar nan dama yankin Afriki gaba daya.

ADVERTISEMENT

Amma kuma duk da muhimmanci Takin zamani ga harkar noma a wannan lokacin, Takin ya yi matukar karanci ga shi kuma da tsananin tsada, Taki na neman gagarar kanana da matsakaitar manona, musamman ganin yadda aka siyasantar da rabawa in gwamnati ta samar don manona su amfana.

Bayani ya nuna cewa, a halin yanzu farashin Takin NPK da Urea ya kai Naira 20, 000 a kasuwannin mu.

LABARAI MASU NASABA

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

Abin takaici a nan shi ne yadda tallafin da gwamnati ke ikirarin tana sanya wa don amfanar talaka baya isa ga wadanda suka fi bukata, Takin ya fada hannun mugayen ‘yan kasuwa wadanda suka tsawalla masa kudi, suka kuma boye shi don a wasu wuraren ko da kudin ka samun Takin yana da mautukar wahala ga kanana da matsaikaitan manoma.

Mun damu matuka a kan karancin Takin zamani don kuwa hakan ya kara matsalar da manoman mu ke ciki ne, musamman ganin suna fuskantar matsaloli a wasu wuraren da suka hada da ayyukan ‘yanta’adda, wadannan matsaloli ne masu tayar da hankula don a wasu wuraren harkar noman ma ta tsaya cik.

Saboda haka fuskantar tsadar Takin zamani a irin wannan lokacin abu ne da zai dagula lissafin manoma gaba daya zai kuma haifar da karancin abinci a cikin al’umma.

Kwanakin baya, babban sakataren Kungiyar Masu Sarrafa Takin Zamani a Nijeriya, (FEPSAN), Gideon Nagedu ya yi ikirarin cewa, Takin Urea, ne kadai ake fuskantar karancinsa a Nijeriya, wai kuma hakan na faruwa ne saboda karancin Iskar Gas da ake fuskanta a Nijeriya, sai dai kuma wasu bayanai sun nuna cewa karancin Takin da ake fuskanta ba wai ya tsaya a kan Takin Urea kada ba ne.

 Duk kuwa cewa, muna sane da cewa, annobar cutar Korona da aka fuskanta a Duniya da yadda aka takaita zirga-zirga da kuma yakin da ake yi a halin yanzu a tsakanin Rasha da Yukiren ya taimaka wajen haifar da karancin Takin zamani, amma muna kira ga Gwamnati a dukkan matakai da su tabbatar da daukar matakan da suka dace don kawo kaeshen karancin Takin da ake fuskanta a halin yanzu don kuwa barazana ce ga samar da wadataccen abinci ga al’umma.

A daida wannan lokaci kuma ya kamata mu ne jin dalilin da ya sa Kamfanonin Takin Zamani na cikin gida suka kasa fuskantar samar da issasun takin zamanin ga manoman Nijeriya.

In har da gaske ake yi na kokarin samar da issashe Takin zamani ga manoman Nijeriya to ya zama tilas kamfanonin takin zmani na cikin gida su farfado don ganin sun cike gibin Takin da ke bukata a cikin gida har a fara tallafa wa wasu kasashen Afrika.

Wadannan matakan sun zama dole saboda ganin muhimmancin Takin zamani ga harkar noma a wannan lokacin.

Idan za a iya tunawa a shekarar 2016, gwamnatin tarayya ta sanya hannun a wata yarjejeniyar samar da Takin zamani tsakaninta da wani kamfanin kasar Morocco, an shirya amfani da Iskar Gas ta Nijeriya da kuma sinadarin phosphate daga kasar Maroco don samar da issashen Takin.

Gwamnati ta bayyana cewa, yarjejeniyar ta samar da shirin yadda za a yi amfani da Iskar Gas na Nijeriya da Phosphate daga kasar Moroco don samar da Tan 750,000 na sinadarin Ammonia da tan Miliyan daya na Takin Phosphate a duk shekara daga nan zuwa shekarar 2025.

Babu tantama zuba jari a bangaren samar da Takin zamani zai matukar taimakawa Nijeriya a kokarinta na samar da isashen abinci ga al’ummarta hakan kuma zai taimaka wajen bunkasa tattalin arzikin kasa.

Dole a wannan gabar a yaba wa Kamfanin Dangote a bisa kokarinshi na samar da takin zamani a cikin gida ta yadda ya kafa katafaren kamfanin Takin zamani da aka kiyasta kudinsa ya kai Dala Biliyan 2.5.

Mun tabbatar da cewa, kamar mafi yawa ‘yan Nijeriya, Kamfanin Taki na Dangote zai bayar da gaggarumar gudummawa wajen ganin an samu wadataccen Takin zamani a kasa yayin da za a iya fitar da rarrar zuwa kasashe Afrika da sauran kasashen duniya.

Akwai dalilai da dama da dole gwamnati ta sanya hankali a kula da bangaren harkar noma, ciki kuwa akwai cewa a halin yanzu bangaren yana samar da aikin yi ga fiye da kashi 33 na ‘yan Nijeriya, gona ne kuma bangaren tattalin arzikin kasa da ya fi kowanne samar wa da al’umma aikin yi, don haka dole gwamnati ta sanya ido a kan ganin bunkasar bangaren.

Taki
Leadership Hausa
Website |  + postsBio
  • Leadership Hausa
    Karuwar Farin Jinin Gwamna Umaru Bago A Siyasar Jihar Neja
  • Leadership Hausa
    Kyakkyawan Tsarin Laken Asiri Zai Dakile Shirin Magudin Zabe A Nijeriya —Mohammed
  • Leadership Hausa
    Batun Dawo Da Tallafin Mai Da Atiku Ya Yi Na Ci Gaba Da Tayar Da Kura
  • Leadership Hausa
    Batun Guguwar Kakar Yakin Neman Zabukan 2027 A Nijeriya

MASU ALAKA

Abin Da Ya Sa Gidauniyar NADF Da Bankin Manoma Suka Yi Haḍaka
Noma Da Kiwo

Kha’amuna Khadi Ta Karɓi Jagorancin Gudanarwa Ta Bankin Noma

August 1, 2026
Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya
Noma Da Kiwo

Dalilin Da Ya Sa Aka Horar Da Manoman Tumatir 100 A Garin Zariya

July 18, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Next Post
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.