ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

…Dalla-dallar Yadda Aka Kashe Kudin Tallafin Mai

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
Tallafin Mai

A cikin rahoton kwamitin tattalin arziki na Nijeriya (NESG) ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kashe jimillar tsabar kudi na Naira tiriliyan 3.64 wajen bayar da tallafin man fetur tun daga shekarar 2015 har zuwa 2021.

Haka kuma rahoton ya kara da cewa adadin kudaden da gwamnatin tarayya ta kashe wajen biyan tallafin man fetur ya karu da naira biliyan 307 a shekarar 2015 zuwa naira tiriliyon 1.77 a shekarar 2021.

  • Kotu Ta Daure Matashin Da Ya Tura Wa Matar Aure Hotunan Batsa A Kebbi
  • Tomas Bach Ya Taya CMG Murna

Wanda ya nuna cewa an samu karin kashi 477 a cikin shekaru shida.

ADVERTISEMENT

Duka wadannan suna cikin rahoton NESG na tattalin arziki na shekarar 2022 mai taken ‘Sake fasalin tattalin arzikin ta yadda zai inganta’, wanda ya bayyana adadin kudaden da gwamnatin tarayya za ta kashe wajen biyan tallafin man fetur a 2022 duk da barazanar da ake samu na farashin danyen mai a kasuwar duniya.

A makon da ya gabata ne, gwamnatin tarayya ta amince da kashe naira tiriliyan 3 wajen bayar da tallafin man fetur a tsakanin watan Yuli zuwa Disambar 2022.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tun a farko, aiwatar da dokar man fetur wanda zai kawo karshen bayar da tallafin man fetur zai fara aiki ne a watan Fabrairun 2022, amma sai aka dage zuwa watan Yulin 2022, sakamakon matsinlambar daga kungiyar kwadugo ta kasa (NLC) da kungiyar ‘yan kasuwa (TUC), aka kara watanni 18.

Sai dai kuma NESG ta bayyana cewa rahoton 2021 yana cike da kalubale da ya turnike na shekarar 2022, sakamakon matsalolin da harkokin kasuwanci suka fuskanta saboda annoba da ta sa sai da gwamnatin tarayya ta bayar da tallafi na jinkai ga ‘yan kasa.

An dai kiyasta cewa tattalin arzikin zai karu da kashi 3.2 a cikin wannan shekarar.

Hakazalika, ofishin Akanta Janar na kasa (AGF) ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kashe naira tiriliyan 4.194 wajen bayar da tallafin mai ga ‘yan kasuwa a tsakanin watan Junairun 2017 zuwa watan Yunin 2022.

Ofishin ya kara da cewa an biya naira biliyan 126.539 a watan Disambar 2017, an biya naira biliyan 691.586 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2018, an biya naira biliyan 537.209 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2019, an biya naira biliyan 133.625 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2020, sannan an biya naira biliyan 1.159 a tsakanin watan Janairu zuwa Disambar 2021, yayin da aka biya naira tiriliyan 1.545 a tsakanin watan Janairu zuwa watan Yunin 2022.

Jerin biyan kudaden tallafin yana nan a shafi na biyu a cikin kundin da Daraktan sa ido na ofishin Akanta Janar, Mista Sylba Okolieaboh ya mika wa kwamitin majalisa da ke bincike kan tallafin mai karkashin jagorancin Hon. Abdulkadir Abdullahi.

Haka ita ma ministar kudi da kasafi da tsare-tsaren kasa, Zainab Ahme ta bayyana cewa a duk rana gwamnatin tarayya tana kashi naira biliyan 18.39 wajen bayar da tallafin man fetur.

Ministar ta bayyana hakan ne a gaban kwamitin majalisar wakilai da ke binciken bayar da tallafin mai tun daga shakarar 2013 har zuwa 2022.

A farkon rabin shakarar 2022, kamfanin mai na kasa (NNPC) ya ce ya samu naira tiriliyan 2.6 a wajen sayar da danyan mai.

Sai dai gwamnatin tarayya tana tsammanin za ta kashe naira tiriliyan 6.7 wajen bayar da tallafin mai a 2023. A cikin rahoton NNPC, ya bayyana cewa gwamnatin tarayya ta kashe naira tiriliyan 4.838 wajen bayar da tallafin mai a cikin shekaru bakwai har zuwa watan Mayun 2022.

Rahoton ya kara da cewa a duk wata ana samun karuwar farashin tallafin man da kashi 989 daidai da naira biliyan 254.8 har zuwa watan Mayun 2022, wanda aka samu naira biliyan 23.4 a karshen 2015.

Rahoton NNPC ya nuna cewa an kashe naira biliyan 99.00 da naira biliyan 141.63 da naira biliyan 722.30 da naira biliyan 578.07 da naira biliyan 133.73, wadanda aka kashe a shekarun 2016, 2017, 2018, 2019 da 2020, yayin da aka kashe naira tiriliyan 1.573 a 2021.

A 2022 kadai a tsakanin watan Janairu zuwa Fabrairu, an kashe naira biliyan 396.72 wajen bayar da tallafin man fetur.

Majalisar kasa ta amince a kashe zunzurutun kudade da suka kai naira tiriliyan 4 kan bayar da tallafin mai a 2022.

Gwamnatin tarayya ta bakin ministan yada labarai, Alhaji Lai Mohammed ta kashe naira tiriliyan 10.413 wajen bayar da tallafin mai a tsakanin 2006 zuwa 2019.

Tallafin Mai
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

Bukatar Samar Da Isasshen Taki Cikin Sauki Ga Manoma

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.