ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Gwamnan Gombe Ya Kaddamar Da Sayar Da Taki Mai Rahusa

by Khalid Idris Doya
3 years ago
Gombe

Gwamnan Muhammadu Inuwa Yahaya na Jihar Gombe, ya kaddamar da sayar da takin zamani na daminar bana da nufin bunkasa noma a jihar.

Da yake kaddamar da takin a gidan gona na Lawanti da ke karamar hukumar Akko, gwamnan ya ce za a sayar da takin ne kan kudi Naira 19,000 kan kowane buhu, sabanin farashin kasuwa da ya kai kusan Naira 26,000, don samarwa manoman jihar sauki.

  • EFCC Ta Sallami Ortom Bayan Tsare Shi Na Tsawon Sa’o’i
  • Gamayyar Masu Ruwa Da Tsaki A Harkar Ilimi Sun Goyi Bayan Gwamnatin Kano Na Kwato Filayen Makarantu

Gwamnan ya ce, “Gwamnati ta sayo tirela 160 na takin kan kudi Naira biliyan biyu da miliyan dari takwas da talatin, karin kimanin tireloli 35 kenan a kan na bara.”

ADVERTISEMENT

Don tabbatar da cewa takin ya kai ga ainihin manoma, Gwamna Inuwa ya bayyana cewa gwamnatinsa ta samar da ingantaccen tsarin sayar da shi a dukkan gundumomin jihar 114 don tabbatar da cewa takin ya kai ga manoma na hakika tun daga tushe.

“Mun fahimci cewa tsadar taki da sauran kayayyakin amfanin gona na iya zama babban cikas ga manomanmu, don haka ne muke aiki tukuru wajen samar da wannan taki a farashi mai rahusa don ragewa manomanmu dawainiyar kudi.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Burinmu shi ne mu tallafa musu da muhimman kayan aikin noma don bunkasa amfanin gona da inganta kasa, da habaka ribar da suke samu, da kuma tabbatar da dorewar harkokin noma a jiharmu”.

Gwamnan ya ce gwamnatinsa ta gudanar da ayyuka da shirye-shirye daban-daban na inganta harkar noma a Gombe, don haka jihar ta shiga cikin harkoki da tsare-tsaren noma da dama a matakin jiha da shiyya da kuma kasa baki daya don bunkasa harkar ta noma.

“Gwamnati ta kuma samar da shirin tallafi na ‘NG-cares’ don samar da taki da sinadaran noma ga manomanmu kyauta, mun kuma hada gwiwa da ma’aikatar noma da raya karkara ta tarayya wajen horar da manoma kan noman masara da doya, inda aka bai wa wadanda suka amfana kayan aikin da suka dace don nomansu.”

Sai ya yi kira ga manoman su bai wa wadanda aka dorawa alhakin sayar da takin da rarraba shi a fadin jihar hadin kai don samun nasarar aikin.

Ya kuma gargade su, da su guji karkatar da takin.

Ya kara da cewa Jihar Gombe jiha ce ta noma, inda fiye da kaso 80 cikin dari na al’ummarta manoma ne, “Saboda haka tallafawa wannan bangare yana da matukar muhimmanci ga ci gaban tattalin arziki, da samar da abinci, da dorewar rayuwar jama’armu”.

Tun farko a jawabinsa na maraba, Daraktan Tsare-Tsare, Bincike da Kididdiga a Ma’aikatar Noma da Kiwo, Dakta Ibrahim Yakubu Usman, ya ce, an kafa kwamitocin yaki da rikicin makiyaya da manoma don magance rikice-rikice da allurar rigakafin cututtukan dabbobi masu yaduwa.

Gombe
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

Kroos Ya Kara Kwantiragin Shekara 1 A Real Madrid

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.