• English
  • Business News
Wednesday, October 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Su Guji Shuka Da Wuri, Su Rungumi Inshora – Masu Ruwa Da Tsaki

by Abubakar Abba
1 year ago
Daminar

Masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, sun gargadi manoma a kan su guji yin shuka da wuri a kakar noman bana; ko da kuwa an samu ruwan sama a nan kurkusa.

A cewar tasu, bisa kwarewar da suke da ita a wannan fanni, suna ganin yin shukar da wuri zai iya sanyawa Irin da suka shuka ya yi saurin lalacewa.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Neman Zama Madaukakiya Tare Da Sake Waiwayar Dokokin Kasa Da Kasa
  • Firaministan Kasar Sin: Bikin Baje Koli Na Canton Fair Zai Ci Gaba Da Haskakawa A Sabon Zamani

Haka zalika, sun shawarce su wajen tabbatar da yin nazari a kan samun sauyin yanayi, kafin fara yin shuka a gonakinsu.

A hirar daban-daban da jaridar LEADERSHIP ta yi da masu ruwa da tsakin sun bayyana cewa, manoman da suke da kwarewa a wannan fanni; ko kadan ka da su dogara a kan saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu na wannan shekara, domin ka da Irin da suka shuka ya lalace.

Haka zalika, a nasa bangaren; Shugaban Kungiyar Manoma ta Kasa, Reshen Kudu Maso Yamma (AFAN), Dakta Babafemi Oke, ya shawarci manoman da su sanya gonakinsu a cikin tsarin inshorar aikin noma, wanda hakan zai ba su damar kare amfaninsu da suka shuka daga tafka asarar da za ta iya afkuwa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

Otunba ya ce, ka da manoman su yi gaggawar yin shuka; don takamarsu na ganin saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu, inda ya yi nuni da cewa, manoman da ke da kwarewa, ya zama wajibi su yi amfani da ita wajen gyarawa da kuma aiwatar da sharar gonakinsu.

A cewarsa, samun saukar ruwan sama na farko da na biyu, ba shi ne yake nuna samun saukar ruwan sama a kan lokaci ba, musamman duba da illar da za ta iya afkuwa; musamman a sakamakon samun sauyin yanayi.

Ya ci gaba da cewa, koda-yake ruwan saman da ya kamata ya fara sauka a tsakanin watan Afirilu, sai yanzu ya fara sauka a wannan wata da muke ciki na Fabirairu a Arewacin tsakiyar kasar nan. Don haka, akwai bukatar manoma su sanya ido kwarai da gaske kafin su kai ga fara yin shuka.

Har ila yau, ya kuma bukaci manoman da su tabbatar sun sayi Irin noma daga wurin hukumomin aikin noma da aka yi wa rijista, kamar irin su ADP, don gudun ka da su tabka mummunar asara.

Shi ma wani kwararren manomi, Prince Adegbenro Nurudeen cewa ya yi, “Saboda matsalar da ke tattare da samun sauyin yanayi, yana da kyau manoma su yi nazari a kan sauyin yanayi da kuma nau’in Irin da za su shuka, duk kuwa da cewa na san manoma da da dama; wdanda za su kagara su yi shuka musamman ganin cewa, ana samun hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin kasar nan”.

Nurudeen ya ci gaba da cewa, “Domin samun yin girbi mai kyau a wannan shekara, dole ne manoma su tabbatar sun yi nazari a kan irin yanayin kasar noma tare da rumgumar dabia’r sauya aiwatar da shuka a gona, duba da yadda yanayin saukar ruwan saman zai kasance”.

Ya kara da cewa, bincike ya nuna; a wasu shiyyoyi na kasar nan, za a iya samun karancin saukar ruwan sama, inda kuma a wasu shiyyoyin, za a iya samun saukar ruwan saman yadda ya kamata.

Binciken da jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, duk da cewa yin shuka a lokacin damina na da kyau, amma yin hakan a lokacin samun ruwan sama kamar da bakin kwarya, zai iya haifar da samun matsaloi da dama; wadanda suka hada da afkuwar ambaliyar ruwan sama da ka iya janyo asarar amfanin da aka shuka.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Osun Ta Horar Da Mata 500 Amfani Da Takin Gargajiya

October 11, 2025
Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe
Noma Da Kiwo

Dalilin IFAD Na Zuba Naira Biliyan 16 A Fannin Noma A Benuwe

October 11, 2025
Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara
Noma Da Kiwo

Yadda Haɗa Jinsin Shanu A Zamance Zai Ƙara Samar Da Madara

October 11, 2025
Next Post
Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

LABARAI MASU NASABA

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

Yajin Aikin: Ɗalibai Sun Bai Wa ASUU Da Gwamnatin Tarayya Wa’adin Kwana 7 Su Warware Rikicinsu

October 15, 2025
Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

Gwamna Diri Da ’Yan Majalisa 23 Na Bayelsa Sun Fice Daga PDP

October 15, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

2027: Babu Ɗan Siyasar Da Zai Iya Ƙalubalantar Tinubu — Fadar Shugaban Ƙasa

October 15, 2025
Tinubu Ya Nemi Jihohi Su Dakatar Da Karbar Haraji A Kan Masu Safarar Kayan Abinci

Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ƙa’ida Ba Barazana Ce Ga Tsaro A Yammacin Afirka – Tinubu

October 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Hana Manoma Girbi A Zamfara, Al’umma Na Neman Taimako

October 15, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama Mutum 105, Sun Ƙwato Ƙwayoyi Sama Da 5,000 A Jigawa

October 15, 2025
Sojoji Sun Kama Ƙasurgumin Ɗan Bindiga, Sun Kashe Shugaban IPOB

Sojoji Sun Ceto Mutum 9 Da Aka Sace A Kwara

October 15, 2025
Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

Dalilin Da Ya Sa Mutane Ke Dawowa Jam’iyyar APC — Shettima

October 15, 2025
Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

Ma’aikatar Kasuwancin Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Shiga Tattaunawar Cinikayya Da Sahihiyar Zuciya

October 14, 2025
Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

Uwar Gidan Shugaban Sin Ta Ziyarci Wajen Nune-nunen Karfafawa Mata Gwiwa A Bangaren Fasahohin Zamani

October 14, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.