ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 17, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Su Guji Shuka Da Wuri, Su Rungumi Inshora – Masu Ruwa Da Tsaki

by Abubakar Abba
2 years ago
Daminar

Masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, sun gargadi manoma a kan su guji yin shuka da wuri a kakar noman bana; ko da kuwa an samu ruwan sama a nan kurkusa.

A cewar tasu, bisa kwarewar da suke da ita a wannan fanni, suna ganin yin shukar da wuri zai iya sanyawa Irin da suka shuka ya yi saurin lalacewa.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Neman Zama Madaukakiya Tare Da Sake Waiwayar Dokokin Kasa Da Kasa
  • Firaministan Kasar Sin: Bikin Baje Koli Na Canton Fair Zai Ci Gaba Da Haskakawa A Sabon Zamani

Haka zalika, sun shawarce su wajen tabbatar da yin nazari a kan samun sauyin yanayi, kafin fara yin shuka a gonakinsu.

ADVERTISEMENT

A hirar daban-daban da jaridar LEADERSHIP ta yi da masu ruwa da tsakin sun bayyana cewa, manoman da suke da kwarewa a wannan fanni; ko kadan ka da su dogara a kan saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu na wannan shekara, domin ka da Irin da suka shuka ya lalace.

Haka zalika, a nasa bangaren; Shugaban Kungiyar Manoma ta Kasa, Reshen Kudu Maso Yamma (AFAN), Dakta Babafemi Oke, ya shawarci manoman da su sanya gonakinsu a cikin tsarin inshorar aikin noma, wanda hakan zai ba su damar kare amfaninsu da suka shuka daga tafka asarar da za ta iya afkuwa.

LABARAI MASU NASABA

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

Otunba ya ce, ka da manoman su yi gaggawar yin shuka; don takamarsu na ganin saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu, inda ya yi nuni da cewa, manoman da ke da kwarewa, ya zama wajibi su yi amfani da ita wajen gyarawa da kuma aiwatar da sharar gonakinsu.

A cewarsa, samun saukar ruwan sama na farko da na biyu, ba shi ne yake nuna samun saukar ruwan sama a kan lokaci ba, musamman duba da illar da za ta iya afkuwa; musamman a sakamakon samun sauyin yanayi.

Ya ci gaba da cewa, koda-yake ruwan saman da ya kamata ya fara sauka a tsakanin watan Afirilu, sai yanzu ya fara sauka a wannan wata da muke ciki na Fabirairu a Arewacin tsakiyar kasar nan. Don haka, akwai bukatar manoma su sanya ido kwarai da gaske kafin su kai ga fara yin shuka.

Har ila yau, ya kuma bukaci manoman da su tabbatar sun sayi Irin noma daga wurin hukumomin aikin noma da aka yi wa rijista, kamar irin su ADP, don gudun ka da su tabka mummunar asara.

Shi ma wani kwararren manomi, Prince Adegbenro Nurudeen cewa ya yi, “Saboda matsalar da ke tattare da samun sauyin yanayi, yana da kyau manoma su yi nazari a kan sauyin yanayi da kuma nau’in Irin da za su shuka, duk kuwa da cewa na san manoma da da dama; wdanda za su kagara su yi shuka musamman ganin cewa, ana samun hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin kasar nan”.

Nurudeen ya ci gaba da cewa, “Domin samun yin girbi mai kyau a wannan shekara, dole ne manoma su tabbatar sun yi nazari a kan irin yanayin kasar noma tare da rumgumar dabia’r sauya aiwatar da shuka a gona, duba da yadda yanayin saukar ruwan saman zai kasance”.

Ya kara da cewa, bincike ya nuna; a wasu shiyyoyi na kasar nan, za a iya samun karancin saukar ruwan sama, inda kuma a wasu shiyyoyin, za a iya samun saukar ruwan saman yadda ya kamata.

Binciken da jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, duk da cewa yin shuka a lokacin damina na da kyau, amma yin hakan a lokacin samun ruwan sama kamar da bakin kwarya, zai iya haifar da samun matsaloi da dama; wadanda suka hada da afkuwar ambaliyar ruwan sama da ka iya janyo asarar amfanin da aka shuka.

Daminar
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari A Kan Wasu Cututtuka Da Ke Shafar Dabbobi Lokacin Damina
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ɗantsoho Ya Jinjina Wa Hukumar FCC Kan Sabbin Sauye-Sauyen Da Ta Samar

MASU ALAKA

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Noma Da Kiwo

Sharhi A Kan Dabarun Zamani Na Yin Auren Ƴaƴan Itatuwa

July 11, 2026
Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu
Noma Da Kiwo

Me Ya Sa Har Yanzu Manoma A Arewa Suka Gwammace Yin Noma Da Galmar Shanu

July 4, 2026
Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana
Noma Da Kiwo

Dalilin Masu Kiwon Kajin Gidan Gona Na Sukar Haɗakar Gwamnatin Tarayya Da Chana

July 3, 2026
Next Post
Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

LABARAI MASU NASABA

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

Mata Manoma Sun Gina Gada, Rijiyar Burtsatse A Danbare, Kano

July 17, 2026
Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

Yadda NDLEA Ke Fatattakar Dillalan Miyagun Kwayoyi Na Kudancin Amurka

July 17, 2026
Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

Gwamnan Da Bai Taba Samun Mulkin Jihar Kano Ba

July 17, 2026
An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

An Ceto Wasu Mutane Huɗu Da Aka Sace A Kogi

July 17, 2026
NPA Ta Tara Kudin Shiga Naira Biliyan 758.2 A 2024

Dalilin Da Ya Sa Kungiyar NCTR Ta Jinjina Wa Shugaban NPA

July 17, 2026
Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

Yunkurin Dauda Lawal Na Bunkasa Bangaren Ma’adanan Jihar Zamfara

July 17, 2026
Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

Gbajabiamila Ya Maka Daraktan Bogi Na PFIPC Kotu, Ya Nemi Diyyar Biliyan 15

July 17, 2026
Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

Bayan Ceto Daliban Oyo: Kallo Ya Koma Borno Da Yobe

July 17, 2026
Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

Batun Yawan Bashin Da Nijeriya Ke Ciyowa Daga Ketare

July 17, 2026
Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

Pew: Sin Ta fi Amurka Samun Amincewar Al’ummun Duniya

July 16, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.