ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Su Guji Shuka Da Wuri, Su Rungumi Inshora – Masu Ruwa Da Tsaki

by Abubakar Abba
2 years ago
Daminar

Masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, sun gargadi manoma a kan su guji yin shuka da wuri a kakar noman bana; ko da kuwa an samu ruwan sama a nan kurkusa.

A cewar tasu, bisa kwarewar da suke da ita a wannan fanni, suna ganin yin shukar da wuri zai iya sanyawa Irin da suka shuka ya yi saurin lalacewa.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Neman Zama Madaukakiya Tare Da Sake Waiwayar Dokokin Kasa Da Kasa
  • Firaministan Kasar Sin: Bikin Baje Koli Na Canton Fair Zai Ci Gaba Da Haskakawa A Sabon Zamani

Haka zalika, sun shawarce su wajen tabbatar da yin nazari a kan samun sauyin yanayi, kafin fara yin shuka a gonakinsu.

ADVERTISEMENT

A hirar daban-daban da jaridar LEADERSHIP ta yi da masu ruwa da tsakin sun bayyana cewa, manoman da suke da kwarewa a wannan fanni; ko kadan ka da su dogara a kan saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu na wannan shekara, domin ka da Irin da suka shuka ya lalace.

Haka zalika, a nasa bangaren; Shugaban Kungiyar Manoma ta Kasa, Reshen Kudu Maso Yamma (AFAN), Dakta Babafemi Oke, ya shawarci manoman da su sanya gonakinsu a cikin tsarin inshorar aikin noma, wanda hakan zai ba su damar kare amfaninsu da suka shuka daga tafka asarar da za ta iya afkuwa.

LABARAI MASU NASABA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

Otunba ya ce, ka da manoman su yi gaggawar yin shuka; don takamarsu na ganin saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu, inda ya yi nuni da cewa, manoman da ke da kwarewa, ya zama wajibi su yi amfani da ita wajen gyarawa da kuma aiwatar da sharar gonakinsu.

A cewarsa, samun saukar ruwan sama na farko da na biyu, ba shi ne yake nuna samun saukar ruwan sama a kan lokaci ba, musamman duba da illar da za ta iya afkuwa; musamman a sakamakon samun sauyin yanayi.

Ya ci gaba da cewa, koda-yake ruwan saman da ya kamata ya fara sauka a tsakanin watan Afirilu, sai yanzu ya fara sauka a wannan wata da muke ciki na Fabirairu a Arewacin tsakiyar kasar nan. Don haka, akwai bukatar manoma su sanya ido kwarai da gaske kafin su kai ga fara yin shuka.

Har ila yau, ya kuma bukaci manoman da su tabbatar sun sayi Irin noma daga wurin hukumomin aikin noma da aka yi wa rijista, kamar irin su ADP, don gudun ka da su tabka mummunar asara.

Shi ma wani kwararren manomi, Prince Adegbenro Nurudeen cewa ya yi, “Saboda matsalar da ke tattare da samun sauyin yanayi, yana da kyau manoma su yi nazari a kan sauyin yanayi da kuma nau’in Irin da za su shuka, duk kuwa da cewa na san manoma da da dama; wdanda za su kagara su yi shuka musamman ganin cewa, ana samun hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin kasar nan”.

Nurudeen ya ci gaba da cewa, “Domin samun yin girbi mai kyau a wannan shekara, dole ne manoma su tabbatar sun yi nazari a kan irin yanayin kasar noma tare da rumgumar dabia’r sauya aiwatar da shuka a gona, duba da yadda yanayin saukar ruwan saman zai kasance”.

Ya kara da cewa, bincike ya nuna; a wasu shiyyoyi na kasar nan, za a iya samun karancin saukar ruwan sama, inda kuma a wasu shiyyoyin, za a iya samun saukar ruwan saman yadda ya kamata.

Binciken da jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, duk da cewa yin shuka a lokacin damina na da kyau, amma yin hakan a lokacin samun ruwan sama kamar da bakin kwarya, zai iya haifar da samun matsaloi da dama; wadanda suka hada da afkuwar ambaliyar ruwan sama da ka iya janyo asarar amfanin da aka shuka.

Daminar
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Duk Da Sabani Tsakanin Ɗangote Da NNPC Jiragen Ruwa Ɗauke Da Man Fetur Sun Iso Nijeriya
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

MASU ALAKA

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa
Noma Da Kiwo

Nazari Kan Muhimmancin Rungumar Kiwon Awaki A Tsakanin Matasa

June 20, 2026
Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA
Noma Da Kiwo

Ƙungiyar KADCCAM Ta Jinjina Wa Hukumar Samar Da Abinci Ta FOA

June 20, 2026
Kungiyar Manoman Citta Ta Kasa Ta Yaba Wa Gwamnatin Tarayya Kan Tallafin Da Take Ba Su
Noma Da Kiwo

Manoman Citta Sun Soki Gwamnatin Delta Kan Mayar Da Su Saniyar Ware

June 19, 2026
Next Post
Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

LABARAI MASU NASABA

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa’ — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026
Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

Tsaro: Dasuki Ya Bukaci Tinubu Ya Gyara Alaka Da Nijar Domin Kare Iyakokin Arewa-Maso-Yamma

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.