ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daminar Bana: Manoma Su Guji Shuka Da Wuri, Su Rungumi Inshora – Masu Ruwa Da Tsaki

by Abubakar Abba
2 years ago
Daminar

Masu ruwa da tsaki a fannin aikin noma, sun gargadi manoma a kan su guji yin shuka da wuri a kakar noman bana; ko da kuwa an samu ruwan sama a nan kurkusa.

A cewar tasu, bisa kwarewar da suke da ita a wannan fanni, suna ganin yin shukar da wuri zai iya sanyawa Irin da suka shuka ya yi saurin lalacewa.

  • Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Neman Zama Madaukakiya Tare Da Sake Waiwayar Dokokin Kasa Da Kasa
  • Firaministan Kasar Sin: Bikin Baje Koli Na Canton Fair Zai Ci Gaba Da Haskakawa A Sabon Zamani

Haka zalika, sun shawarce su wajen tabbatar da yin nazari a kan samun sauyin yanayi, kafin fara yin shuka a gonakinsu.

ADVERTISEMENT

A hirar daban-daban da jaridar LEADERSHIP ta yi da masu ruwa da tsakin sun bayyana cewa, manoman da suke da kwarewa a wannan fanni; ko kadan ka da su dogara a kan saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu na wannan shekara, domin ka da Irin da suka shuka ya lalace.

Haka zalika, a nasa bangaren; Shugaban Kungiyar Manoma ta Kasa, Reshen Kudu Maso Yamma (AFAN), Dakta Babafemi Oke, ya shawarci manoman da su sanya gonakinsu a cikin tsarin inshorar aikin noma, wanda hakan zai ba su damar kare amfaninsu da suka shuka daga tafka asarar da za ta iya afkuwa.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

Otunba ya ce, ka da manoman su yi gaggawar yin shuka; don takamarsu na ganin saukar ruwan sama na farko da kuma na biyu, inda ya yi nuni da cewa, manoman da ke da kwarewa, ya zama wajibi su yi amfani da ita wajen gyarawa da kuma aiwatar da sharar gonakinsu.

A cewarsa, samun saukar ruwan sama na farko da na biyu, ba shi ne yake nuna samun saukar ruwan sama a kan lokaci ba, musamman duba da illar da za ta iya afkuwa; musamman a sakamakon samun sauyin yanayi.

Ya ci gaba da cewa, koda-yake ruwan saman da ya kamata ya fara sauka a tsakanin watan Afirilu, sai yanzu ya fara sauka a wannan wata da muke ciki na Fabirairu a Arewacin tsakiyar kasar nan. Don haka, akwai bukatar manoma su sanya ido kwarai da gaske kafin su kai ga fara yin shuka.

Har ila yau, ya kuma bukaci manoman da su tabbatar sun sayi Irin noma daga wurin hukumomin aikin noma da aka yi wa rijista, kamar irin su ADP, don gudun ka da su tabka mummunar asara.

Shi ma wani kwararren manomi, Prince Adegbenro Nurudeen cewa ya yi, “Saboda matsalar da ke tattare da samun sauyin yanayi, yana da kyau manoma su yi nazari a kan sauyin yanayi da kuma nau’in Irin da za su shuka, duk kuwa da cewa na san manoma da da dama; wdanda za su kagara su yi shuka musamman ganin cewa, ana samun hauhawar farashin kayan abinci a dukkanin fadin kasar nan”.

Nurudeen ya ci gaba da cewa, “Domin samun yin girbi mai kyau a wannan shekara, dole ne manoma su tabbatar sun yi nazari a kan irin yanayin kasar noma tare da rumgumar dabia’r sauya aiwatar da shuka a gona, duba da yadda yanayin saukar ruwan saman zai kasance”.

Ya kara da cewa, bincike ya nuna; a wasu shiyyoyi na kasar nan, za a iya samun karancin saukar ruwan sama, inda kuma a wasu shiyyoyin, za a iya samun saukar ruwan saman yadda ya kamata.

Binciken da jaridar LEADERSHIP ta gudanar ya nuna cewa, duk da cewa yin shuka a lokacin damina na da kyau, amma yin hakan a lokacin samun ruwan sama kamar da bakin kwarya, zai iya haifar da samun matsaloi da dama; wadanda suka hada da afkuwar ambaliyar ruwan sama da ka iya janyo asarar amfanin da aka shuka.

Daminar
Abubakar Abba
+ postsBio
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Kamfanin Simintin Ɗangote Ya Ƙaddamar Da Shirye-shiryen Tallafa Wa Mazauna Jihar Biniwe
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Dalilin Gwamnatin Kwara Na Zuba Dala Biliyan 70 A Fannin Kiwon Dabbobi
  • Abubakar Abba
    https://hausa.leadership.ng/author/abubakar-abba/
    Cibiyar IAR Ta Gudanar Da Ayyukan Bincike 140 Kan Sabbin Amfanin Gona 

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi
Noma Da Kiwo

Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Sabbin Cibiyoyin Kula Da Lafiyar Dabbobi

May 31, 2026
Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani
Noma Da Kiwo

Abin Da Ya Sa Gwamnatin Taraba Ta Sayo Sabbin Kayan Noma Na Zamani

May 31, 2026
Laifukan Intanet: Kotun Abuja Ta Karɓi Rahoton DSS, Ta Ba Da Belin Wani Ɗan Gwagwarmaya
Noma Da Kiwo

IAR Ta Fara Horas Da Malaman Gona Don Fuskantar Daminar Bana

May 24, 2026
Next Post
Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

Kamfanin Takin Indorama Ya Samu Bashin Dala Miliyan 75

LABARAI MASU NASABA

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.