• English
  • Business News
Friday, May 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Haya Ya Maka Mai Gida A Kotu Kan Kin Sayar Masa Da Gidan Da Ya Ke Haya

by Sadiq
2 years ago
in Al'ajabi
0
Dan Haya Ya Maka Mai Gida A Kotu Kan Kin Sayar Masa Da Gidan Da Ya Ke Haya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Wata babbar kotu a Jihar Legas ta yi watsi da karar da wani dan haya mai suna Ademola Onitiju, ya shigar a kan mai gidan da ta ba shi haya sabo da ta ji sayar masa da gidan.

A shekarar 2021, Onitiju, wanda sojan sama ne (mai ritaya) kuma ma’aikacin shari’a, ya kai Theodosia Ogunnaike kotu a kan ta ki sayar masa da gida mai dakuna hudu a Dolphin Estate a Ikoyi, amma ta sayar wa da wani gidan bayan da shi dan hayar nata ta fara yin ciniki.

  • Kwamishinan Benuwe Da Aka Sace Ya Kubuta
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Dakile Hari A Kaduna

Dan hayar, mai shekaru 59, wanda ya fara zama a gidan a watan Disambar 2015, ya ce tun da fari, mai gidan ta yi masa tayin ya siya, amma kuma bai biya kudin ba bayan ya amsa cewa ya yarda zai saya.

Onitiju, ya ce da farko an nemi ya biya Naira miliyan 170 kudin gidan amma sai ya biya Naira miliyan 90 a maimakon haka, sai mai gidan ta ki amincewa.

Ya kara da cewa, a lokacin da ake tattaunawa, ya sayar da kadarori biyu na gadonsu domin ya samu damar sayan gidan a farashin Naira miliyan 135 wanda ya ce shi a haka zai saya.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

Ya ce, ya nemi matar da bashi lambar asusun bankinta domin ya biya kudin ta nan, amma ba ta ba shi komai ba har sai da aka sayar da gidan ga wani Samuel Dare, wani Kanal din soja.

Ogunnaike, wadda bazawara ce ta ce gidan na ‘yarta ne amma ita ke kular mata da shi.

Matar, ta ce Onitiju ya kasance ya na biyan kudin hayarsa na Naira miliyan 4.5 a asusun ajiyarta na banki duk shekara kuma ba a kara kudin hayar ba a lokacin zamansa sabo da su na zaune lafiya.

Uwargidan ta ce an fara ba Onitiju tayin sayen gidan, amma ba shi da kudin da zai biya.

Daga nan sai ta dakatar da tayin da aka yi wa jami’in sojan sama mai ritaya bayan ya yi tayin kudi guda biyu na Naira miliyan 90 da kuma Naira miliyan 100, inda daga nan ne ta bude kofar sayar da gidan ga kowa.

A hukuncin da ta yanke Bola Okikiolu-Ighile, shugabar alkalan kotun, ta ce shaidun Onitiju da ke gaban kotu ba su da wani karfi da za su kare korafin da ya shigar ba kuma ba shi da gaskiya a shari’ar.

Daga baya kotun ta yi watsi da karar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Dan HayaGidaKotuLegas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Da Dumi-Dumi: Hazard Ya Yi Ritaya Da Buga Wa Belgium Kwallo

Next Post

Cristiano Ronaldo Ya Musanta Jita-Jitar Amince Wa Tayin Fan Miliyan 173 Na Al Nassr 

Related

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano
Al'ajabi

An Kama Amarya Kan Zargin Kashe Mijinta Bayan Kwana 9 Da Aurensu A Kano

3 days ago
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi
Al'ajabi

‘Yansanda Sun Kama Matashi Kan Zargin Kashe Mahaifinsa Har Lahira A Jigawa

3 days ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

’Yansanda Sun Kama ‘Yar Shekara 40 Bisa Zargin Yi Wa Almajiri Fyaɗe A Bauchi

2 weeks ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Al'ajabi

Matashi Ya Kashe Mahaifiyarsa Da Taɓarya A Bauchi

2 months ago
‘Yansanda Sun Dakile Harin Da ‘Yan Bindiga Suka Kai Kan Wasu Rukunin Gidaje A Katsina
Al'ajabi

Wani Jami’in Ɗansanda Ya Bindige Kansa Har Lahira A Jihar Nasarawa

3 months ago
Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja
Al'ajabi

Yadda Ittihadil Ummah Ta Gabatar Da Walimar Yaye Dalibai Dattawa Da Suka Sauke Alku’arni A Abuja

4 months ago
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Musanta Jita-Jitar Amince Wa Tayin Fan Miliyan 173 Na Al Nassr 

Cristiano Ronaldo Ya Musanta Jita-Jitar Amince Wa Tayin Fan Miliyan 173 Na Al Nassr 

LABARAI MASU NASABA

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

Sin Da Rasha Za Su Karfafa Hadin Gwiwa Don Kare Karfin Ikon Dokokin Duniya

May 9, 2025
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Halarci Bukukuwan A Moscow

May 9, 2025
AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

AIRLIN Ta Buƙaci Ƴan Arewa Su Ƙara Ƙaimi Wajen Rijistar Katin Zaɓe Da Na Shaidar Ɗan Ƙasa 

May 9, 2025
Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

Rabe-Raben Aikin Hajji Da Abubuwan Da Aka Halasta Ga Mahajjaci

May 9, 2025
Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

Matatar Mai: Har Yanzu ‘Kabal’ A Ɓangaren Mai Na Yaƙar Nasararmu – Dangote

May 9, 2025
Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

Farfaɗo Da Mutuncin Nijeriya Ta Hanyar Buɗe Kofofin Kasuwanci Da Ƙasashen Waje

May 9, 2025
Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

Hukuncin Tarar Dala Miliyan 220 Da Kotu Ta Ci Kamfanin Meta Ya Yi Daidai

May 9, 2025
Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

Xi Da Putin Sun Gana Da Manema Labarai Tare

May 8, 2025
Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

Man Utd Ta Lallasa Bilbao, Ta Kai Wasan Ƙarshe Na Gasar Europa

May 8, 2025
Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

Xi: Hadin Gwiwa Tsakanin Sin Da Rasha Na Samar Da Daidaito Ga Duniya Mai Cike Da Tashin Hankali

May 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.