ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Haya Ya Maka Mai Gida A Kotu Kan Kin Sayar Masa Da Gidan Da Ya Ke Haya

by Sadiq
4 years ago
Dan Haya

Wata babbar kotu a Jihar Legas ta yi watsi da karar da wani dan haya mai suna Ademola Onitiju, ya shigar a kan mai gidan da ta ba shi haya sabo da ta ji sayar masa da gidan.

A shekarar 2021, Onitiju, wanda sojan sama ne (mai ritaya) kuma ma’aikacin shari’a, ya kai Theodosia Ogunnaike kotu a kan ta ki sayar masa da gida mai dakuna hudu a Dolphin Estate a Ikoyi, amma ta sayar wa da wani gidan bayan da shi dan hayar nata ta fara yin ciniki.

  • Kwamishinan Benuwe Da Aka Sace Ya Kubuta
  • Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Dakile Hari A Kaduna

Dan hayar, mai shekaru 59, wanda ya fara zama a gidan a watan Disambar 2015, ya ce tun da fari, mai gidan ta yi masa tayin ya siya, amma kuma bai biya kudin ba bayan ya amsa cewa ya yarda zai saya.

ADVERTISEMENT

Onitiju, ya ce da farko an nemi ya biya Naira miliyan 170 kudin gidan amma sai ya biya Naira miliyan 90 a maimakon haka, sai mai gidan ta ki amincewa.

Ya kara da cewa, a lokacin da ake tattaunawa, ya sayar da kadarori biyu na gadonsu domin ya samu damar sayan gidan a farashin Naira miliyan 135 wanda ya ce shi a haka zai saya.

LABARAI MASU NASABA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

Ya ce, ya nemi matar da bashi lambar asusun bankinta domin ya biya kudin ta nan, amma ba ta ba shi komai ba har sai da aka sayar da gidan ga wani Samuel Dare, wani Kanal din soja.

Ogunnaike, wadda bazawara ce ta ce gidan na ‘yarta ne amma ita ke kular mata da shi.

Matar, ta ce Onitiju ya kasance ya na biyan kudin hayarsa na Naira miliyan 4.5 a asusun ajiyarta na banki duk shekara kuma ba a kara kudin hayar ba a lokacin zamansa sabo da su na zaune lafiya.

Uwargidan ta ce an fara ba Onitiju tayin sayen gidan, amma ba shi da kudin da zai biya.

Daga nan sai ta dakatar da tayin da aka yi wa jami’in sojan sama mai ritaya bayan ya yi tayin kudi guda biyu na Naira miliyan 90 da kuma Naira miliyan 100, inda daga nan ne ta bude kofar sayar da gidan ga kowa.

A hukuncin da ta yanke Bola Okikiolu-Ighile, shugabar alkalan kotun, ta ce shaidun Onitiju da ke gaban kotu ba su da wani karfi da za su kare korafin da ya shigar ba kuma ba shi da gaskiya a shari’ar.

Daga baya kotun ta yi watsi da karar.

MASU ALAKA

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa
Al'ajabi

Ana Zargin Jami’in Kwastam Da Kashe Kansa A Bauchi Saboda Damuwa

June 9, 2026
EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas
Al'ajabi

EFCC Ta Cafke Lauyan Bogi Da Mallakar Hatimin Kungiyar Lauyoyi Ta Nijeriya Na Jabu A Legas

April 21, 2026
Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar
Al'ajabi

Yadda Aka Gano Ƙasusuwan Dabba Mai Shekara Miliyan 100 A Nijar

March 8, 2026
Next Post
Cristiano Ronaldo Ya Musanta Jita-Jitar Amince Wa Tayin Fan Miliyan 173 Na Al Nassr 

Cristiano Ronaldo Ya Musanta Jita-Jitar Amince Wa Tayin Fan Miliyan 173 Na Al Nassr 

LABARAI MASU NASABA

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

Sin Ta Zama Abin Koyi Na Sauyi Da Ci Gaba Ga Kasashe Da Dama, In Ji Shalva Papuashvili

June 13, 2026
Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

Garkuwa Da Mutane Na Barazana Ga Dalibai Miliyan 1.9 Masu Jarrabawar WAEC A Sassan Nijeriya

June 13, 2026
Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Amfani Da Tsaron Kasa Wajen Danne Wasu Kamfanonin Sinawa

June 13, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.