• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisa Ya Bayar Da Tallafi Tare Da Koyar Da Sana’o’i A Zariya

by Idris Umar
3 years ago
Zariya

Daruruwan mutane ne suka amfana da tallafi daga dan majalisa mai wakiltar karamar karamar hukumar Sabon Gari ta jihar Kaduna.

 

Tallafin da dan majalisa ya bayar ya taba bangarori da dama na rayuwar al’umar karamar hukumarsa ta Sabon Gari.

  • ‘Yan Ta’adda Sun Kashe Mutane 44 A Burkina Faso

Baya ga tallafin abinci da dan majalisa ya bayar ga darurun jama’a tuni ya shirya taron koyar da sana’ar dogaro da kai ga daruruwan jama’arsa.

 

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Wakilinmu ya ziyarci dukkan bangaren da ake bayar da horon don tabbatar wa idonsa abin da ke gudana a wajen. Wajen da ake bayar da horon ga daruruwag al’ummar ta karamar hukumar guda 2 ne kuma duk cike yake da mutane

 

Da yake zantawa da manema labarai, mai taimakawa dan majalisar a bangaren harkar gudanarwa, Kwamred Ishak Adamu (A.D.O) ya bayyana dukkan abubuwan da dan majalisan ya gudanar a ‘yan kwanakin nan wato kafin shigar watan Azumi da cikin watan azumin duk a matsayin tallafi ga jama’arsa karkashin jam’iyarsu ta APC.

 

Ishak Adamu ya ce, “A yanzu haka mutane 700 ake ba horo maza da mata da samari da har da tsofafi dukkansu ana basu horo ne na koyan kananan sana’o’i kamar yadda za su iya hada alkaki na zamani ko yadda za su hada kek na zamani kuma in sun kammala samun horon dan majalisa zai ba su naira dubu ashiri da biyar (#25,000) ga ko wanne da ya sami horon don yin jali.”

 

Mataimakin na musamman ya kara da cewa satin da ya gabata ma dan majalisar ya bayar da buhun shinkafa manya da kanana guda (1,500) ga jama’a da tallafin buhun Gero guda (700) ga jama’a don samun albarka.

 

Ishak Adamu ya tabbatar da cewa duk a satin daya gabata dan majalisa Garba Datti Muhammad Babawo ya saya wa hukumar kula da hadura hanya ta kasa mota ta daukar mara lafiya (ambulance)

 

“Kuma yanzu haka ya kawo wa dukkan gundumomi (11) da ake da su a fadin karamar hukumar Sabon Gari Fitillar Sola mai haske titi guda (100).”

 

Ya ce abin mamaki da alfahari shi ne da yawan aikin da shi dan majalisan ya yi a yanzu ya yi su ne bayan an shelanta ya fadi zabe duk da sun ce suna kalubalantar sakamakon zaben a matsayin an tafka magudi ne tsagwaro.

 

Malama Rukayya Muhammad daga unguwar Gabar Sabon gari tana daga cikin matan da suka sami tallafin bisa hakan, ta nuna Jin dadin horon da ta samu kuma za ta yi amfani da ilmin da ta samu kuma za yi amfani da jarin da aka ba ta domin kula da kanta.

 

Muhammad Sani daga gundumar Basawa shi ma ya sami tallafin kuma yayi wa dan majalisar fatan alheri da rokon Allah ya ba shi nasara a duk inda ya sa gabansa.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Zariya
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa
Manyan Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro
Manyan Labarai

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Next Post
Buhari Ya Yi Ta’aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

Buhari Ya Yi Ta'aziyyar Matar Aminu Dantata Da Ta Rasu

LABARAI MASU NASABA

Zariya

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.