• English
  • Business News
Monday, June 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dan Majalisa Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Firamare A Adamawa

by Muh'd Shafi'u Saleh
1 year ago
in Labarai
0
Dan Majalisa Ya Kaddamar Da Ajujuwa 3 A Firamare A Adamawa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan majalisar wakilai mai wakiltar kananan hukumomin Numan/Demsa/Lamurde, Honarabul Kwamoti La’ori, ya kaddamar da ginin ajujuwan karatu uku, a makarantar firamare da ke garin Kwah a karamar hukumar Lamurde a jihar Adamawa.

Da yake jawabi a taron dan majalisa Kwamoti La’ori, ya gode wa Allah da ya ba shi damar cika alkawarin da ya yi wa jama’a lokacin yaƙin neman zaben ya ce ba iyawarsa ba ne, ya yi alkawarin ci gaba da yi wa jama’a hidima.

  • Hungary Na Sa Ran Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi A Dangantakarta Da Sin
  • NNPCL Ya Bayyana Ranar Da Matatar Man Fetur Ta Kaduna Za Ta Fara Aiki

La’ori ya kuma bukaci jama’a da su ci gaba da bai wa tsare-tsaren gwamna Ahamdu Umaru Fintiri, goyon baya domin tabbatar da samun zaman lafiya “idan kun samu bayanai ku sanar da gwamnati domin daukan mataki a kan lokaci”.

Ya kuma yi alkawarin isar da sakon gudanar da aikin babbar hanyar kamar yadda jama’ar yankin suka bukata ga hukumomin da suka dace.

Da ita ma ke jawabi shugabar malamai na makarantar Salome Nicoderius, ta nuna matukar farin ciki da jinjina wa dan majalisar bisa aikin gina ajujuwan da ya yi, ta kuma koka da karancin malamai a makarantar.

Labarai Masu Nasaba

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

A nasa jawabin, tsohon shugaban karamar hukumar Lamurde Bulus Daniel, ya bayyana siyasar fada da cewar dan majalisar da cewa abu ne da ya kamata a ce ‘yan siyasa sun koya.

Ya ce “idan mu ‘yan siyasa za mu yi koyi da irin siyasarka to kuwa za mu cimma nasara, ni da kan ne fitilar siyasa na, zan ci gaba da koyi da kai” in ji Bulus.

Da shi ma ke jawabi sarkin Kwah Mista Nickson Tamuna, ya bayyana dan majalisar a matsayin babban alfahari da kyautar da Allah ya yi wa jama’ar yankin da jihar Adamawa, ya kara da cewa “ka zo mana da alherin da ba zamu taba mantawa da shi ba, muna neman da kayi amfani matsayinka na ganin an gyara mana babban hanyar Lamurde zuwa Karim” in ji sarkin.

Baya ga karrama dan majalisa Kwamoti La’ori da mukamin (Inuwar Kwah), an kuma gudanar da rawar gargajiya na kabilun yankin a lokacin taron na jiya Litinin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AdamawaDan Majalisa
ShareTweetSendShare
Previous Post

Hungary Na Sa Ran Ziyarar Xi Za Ta Bude Sabon Babi A Dangantakarta Da Sin

Next Post

Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Related

Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga
Labarai

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

1 hour ago
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago
Manyan Labarai

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

4 hours ago
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano
Manyan Labarai

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

6 hours ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Dukkan Fasinjojin Motar Bas A Jihar Benuwe

9 hours ago
Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi
Labarai

Yanzu-yanzu: Zanga-zanga Ta Ɓarke A Jami’ar Neja Bayan Kashe Ɗalibi

11 hours ago
Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal
Labarai

Ina Da Isassun Kuɗi, Ban Ciwo Bashin Ko Kwabo Ɗaya Don Gyara Jihar Zamfara Ba – Gwamna Lawal

13 hours ago
Next Post
Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

Shugaban Serbia: Zan Rubuta Wani Littafi Don Tunawa Da Hulda Ta Da Xi Jinping

LABARAI MASU NASABA

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

Likitocin Kasar Sin Sun Gudanar Da Ayyukan Kiwon Lafiya Kyauta Ga Yara A Botswana

June 23, 2025
Minista Ya Buƙaci Kafafen Yaɗa Labarai Da Su Guji Tallata ’Yan Ta’adda Da ’Yan Bindiga

Gargaɗin Amurka: Gwamnati Ta Bayar Da Tabbaci Akwai Tsaro A Abuja

June 23, 2025
Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

Tawagar Likitocin Kasar Sin Sun Duba Marayu Marasa Lafiya Fiye Da 200 Kyauta A Zanzibar Ta Tanzaniya

June 23, 2025
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

June 23, 2025
Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

Za A Gudanar Da Taron Dandalin Davos Na Lokacin Zafi Karo Na 16 a Birnin Tianjin Na Sin

June 23, 2025
CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

CMG Ya Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Hadin Gwiwa Da Kwamitin Shirya Gasar Wasannin Olympics Ta Milano Cortina Ta Shekarar 2026

June 23, 2025
Karin Kudin Mai: Hakika An Ci Amanarmu, In Ji ‘Yan Kwadago

NNPC Ya Ƙara Kuɗin Fetur, Duba Sabon Farashin

June 23, 2025
Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

Binciken CGTN: Masu Bayyana Ra’ayoyi Na Kasa Da Kasa Sun Yi Allah Wadai Da Harin Amurka Kan Iran

June 23, 2025
Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

Ƴansanda Sun Gano  Ƙarin Bama-Bamai 9 Da Basu Fashe Ba A Kano

June 23, 2025
Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

Sin Na Fatan Kwamitin Sulhun MDD Zai Goyi Bayan Kuduri Game Da Halin Da Iran Ke Ciki

June 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.