Dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Argungu/Augie ta jihar Kebbi a majalisar tarayya, Sani Yakubu Noma ya bayyana cewa, ya kammala shirye-shiryen aurar da ‘ya’ya mata marayu 100.
Da yake zantawa da manema labarai a mahaifarsa da ke yankin Argungu a jihar Kebbi, dan majalisar ya ce, shirin auren na daya daga cikin gudunmawar da yake bayarwa wajen kyautata rayuwar marayu a mazabarsa.
- Majalisar Dokokin Kaduna Ta Dakatar Da Kansiloli 8, Ta Karɓe Ragamar Majalisar Kagarko
- Ruɗani A Kan Shari’ar Abba Da Gawuna: Kotu Ta Tabbatar Da Nasarar NNPP A Rubuce
Ya ce, za a daura auren ne a fadar mai martaba Sarkin Argungu, Alhaji Sama’ila Muhammad Mera a ranar Asabar.
“An kafa kwamiti don samun nasarar aiwatar da taron. Wadanda aka zaba domin a daura musu auren sun fito ne daga kananan hukumomi biyu da nake wakilta a Majalisar Dokoki ta kasa.
“Tuni, na sayi gadaje, katifu, kayan daki masu mahimmanci da sauran kayayyakin aure ga wadanda suka ci gajiyar shirin,” in ji shi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp