• English
  • Business News
Monday, September 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Da BUA Za Su Bayyana A Gaban Majalisa Kan Badakalar Haraji

by Sadiq
1 year ago
in Manyan Labarai
0
Dangote Da BUA Za Su Bayyana A Gaban Majalisa Kan Badakalar Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta umarci kamfanonin Dangote da BUA su bayyana a gabanta don amsa tambayoyi kan zirarewar kudaden harajin Gwamnatin Tarayya.

Kamfanonin simintin BUA da Dangote na cikin jerin kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyin Gwamnatin Tarayya 113 da za su amsa tambayoyi kan wannan lamari.

  • Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
  • Zanga-Zanga: NSCDC Ta Shirya Aikewa Da Jami’ai 30,000 Faɗin Nijeriya

Shugaban kwamitin binciken kudaden jama’a na majalisar, Bamidele Salam ne, ya sanar cewa shugabannin kamfanonin ko manyan akantocinsu ne za su hallara domin amsa tambayoyin.

Ya ce binciken zai mayar da hankali ne kan rashin biyan kudaden haraji ga gwamnati, rashin bin ka’idojin da doka ta shimfida wajen biya, da kuma zirarewar kudaden.

Ya ce binciken zai fara ne daga ranar 30 ga watan nan na Yuli zuwa 8 ga Agusta, 2024, kuma majalisar za ta yi tsattsuran hukunci kan duk kamfani ko cibiyar gwamnati da ta ki amsa gayyatar.

Labarai Masu Nasaba

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu

Sanarwar ta ce ana bukatar, “kamfanonin su zo da duk takardun da ake bukata.”

Bankunan First Bank, Zenith Bank, Guarantee Trust, Access Bank, Polaris, FCMB, Fidelity da Keystone na cikin masu amsa tambayoyin.

Kazalika kamfanin hakar mai na Shell Develompent Company da kamfanin lemon kwalba 7Up da kamfanin mai na Durbi Oil.

Sauran kamfonin abinci irin su C-Way Food & Beverages da kamfanin madarar Fan Milk da kamfanin Rite Food Ltd; Guinness Nigeria Plc; Pabod Int’l Breweries; Champion Breweries; Agio Power Plant (Kwale Okpai Power Plant); Euro-Global and Disability Plc.

Hukumomi da cibiyoyin gwamnati da za a bincika sun hada da; Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci, wadda za a bincika kan zargin karkatar da kudaden tallafin COVID-19.

Sannan za a binciki Cibiyar Yaki da Yaɗuwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) kan zargin karkatar da kudaden yaki da COVID-19.

Hukumar Gidan Radio ta Kasa (FRCN) kuma za ta amsa tambayoyi kan zirarewar kudaden shiga ta kafar Remita.

Sai Majalisar Karamar Hukumar Gwagwalada da za ta amsa tambayoyi kan zargin almundahana da rahoton shekarar 2020 da ofishin babban mai binciken kudi na kasa ya bankado.

Sauran da ake zargi a rahoton sun hada da: Ma’aikatar Tsaro, Matatar Mai ta Kaduna, Kamfanin Wutar Lantarki ta Kasa na kuma Hukumar Iskar Gas ta Kasa (NLNG) da Ma’aikatar Sufuri ta Kasa

Akwai kuma Hukumar Kula da Kamfanonin Gwamnati (BPE), Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare, Jami’ar Sojoji da ke Jihar Borno, Ma’aikatar Ma’adinai, Hukumar Kogin Neja Delta, Ma’aikatar harkokin waje, Ma’aikatar Ilimi da Hukumar Jarabawa ta Kasa (NECO).

Hakazalika akwai Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da Kamfanin Dillanccin Labaran Njjeriya (NAN) da Hukumar Aikin Dan Sanda da Cibiyar Yaki da Cutar Kuturta da Tarin Fuka da Hukumar Kidaya ta Kasa da sauransu da suka hada jami’o’i da kwalejin ilimi da cibiyoyin lafiya da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUADangoteHarajiMajalisar Wakilai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Jirgin Arik Daga Yin Jigilar Fasinjoji Saboda Bashi

Next Post

Za Mu Dauki Fansar Kisan Haniyeh – Iran

Related

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 
Manyan Labarai

An Lalata Tamfatsetsiyar Gonar Wiwi A Taraba Tare Da Kama Dan Shekaru 70 A Anambra 

16 hours ago
Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu
Manyan Labarai

Legas Ta Laƙume Aikin Naira Tiriliyan 3.9 Cikin Shekaru Biyun Tinubu

2 days ago
A Karo Na 3 Cikin Wata Guda, Jirgin Ruwa Ya Sake Kifewa A Sakkwato
Manyan Labarai

A Karo Na 3 Cikin Wata Guda, Jirgin Ruwa Ya Sake Kifewa A Sakkwato

2 days ago
Gwamnatin Katsina Za Ta Sayo Babura 700 da Motoci 20 Don Samar Da Tsaro
Manyan Labarai

Gwamnatin Katsina Za Ta Sayo Babura 700 da Motoci 20 Don Samar Da Tsaro

2 days ago
Mutane Da Dama Sun Ɓace Yayin Da Jirgin Ruwa Ya Kife A Sakkwato
Manyan Labarai

Mutane Da Dama Sun Ɓace Yayin Da Jirgin Ruwa Ya Kife A Sakkwato

2 days ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 51, 876 Sun Mika Wuya A Arewa Maso Gabas
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutum 117, Sun Kama Masu Laifi 150 Cikin Mako Guda

2 days ago
Next Post
Za Mu Dauki Fansar Kisan Haniyeh – Iran

Za Mu Dauki Fansar Kisan Haniyeh – Iran

LABARAI MASU NASABA

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

Xi Jinping Ya Gana Da Narendra Modi 

August 31, 2025
Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

Xi Jinping Da Uwargidansa Peng Liyuan Sun Shirya Liyafar Maraba Da Baki Na Kasa Da Kasa Ga Mahalarta Taron SCO

August 31, 2025
Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

Gobarar Tankar Mai Ta Lakume Manyan Motoci 4 A Legas

August 31, 2025
Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

Za A Wallafa Makalar Xi Game Da Farfado Da Kasa Bisa Karfin Ruhin Turjiya Ga Zalunci

August 31, 2025
Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

Kano Na Asarar Biliyan 1 Duk Shekara Dalilin Rashin Yin Gwanjon Tsofaffin Kayan

August 31, 2025
Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

Kasar Sin Ta Inganta Wuraren Tunawa Da Tarihi Don Bikin Samun Nasara Kan Zaluncin Japanawa

August 31, 2025
Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

Jami’an Senegal Sun Yaba Da Ci Gaban Da Aka Samu Wajen Aiwatar Da Sakamakon Taron FOCAC Na Beijing

August 31, 2025
Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

Ɗan Majalisa Zai Saya Wa Makinde Fam Ɗin Takarar Shugaban Ƙasa A 2027

August 31, 2025
Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

Fim Din Kasar Sin Kan Kisan Kiyashin Nanjing Ya Ja Hankulan Masu Kallo A Nijeriya

August 31, 2025
Hatsarin Jirgin Kasa: Gwamna Uba Sani Ya Ba Da Umarnin Talllafawa Fasinjojin Da Ke Cikin Jirgin

Hatsarin Jirgi: Babu Batun Zagon-ƙasa Ga Harkokin Sufurin Jiragen Ƙasan Abuja-Kaduna – Gwamnati

August 31, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.