• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dangote Da BUA Za Su Bayyana A Gaban Majalisa Kan Badakalar Haraji

by Sadiq
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Dangote Da BUA Za Su Bayyana A Gaban Majalisa Kan Badakalar Haraji
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Majalisar Wakilai ta umarci kamfanonin Dangote da BUA su bayyana a gabanta don amsa tambayoyi kan zirarewar kudaden harajin Gwamnatin Tarayya.

Kamfanonin simintin BUA da Dangote na cikin jerin kamfanoni masu zaman kansu da cibiyoyin Gwamnatin Tarayya 113 da za su amsa tambayoyi kan wannan lamari.

  • Zanga-Zanga: Gwamnatin Yobe Ta Bayar Da Umarnin Rufe Makarantun Jihar
  • Zanga-Zanga: NSCDC Ta Shirya Aikewa Da Jami’ai 30,000 Faɗin Nijeriya

Shugaban kwamitin binciken kudaden jama’a na majalisar, Bamidele Salam ne, ya sanar cewa shugabannin kamfanonin ko manyan akantocinsu ne za su hallara domin amsa tambayoyin.

Ya ce binciken zai mayar da hankali ne kan rashin biyan kudaden haraji ga gwamnati, rashin bin ka’idojin da doka ta shimfida wajen biya, da kuma zirarewar kudaden.

Ya ce binciken zai fara ne daga ranar 30 ga watan nan na Yuli zuwa 8 ga Agusta, 2024, kuma majalisar za ta yi tsattsuran hukunci kan duk kamfani ko cibiyar gwamnati da ta ki amsa gayyatar.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Sanarwar ta ce ana bukatar, “kamfanonin su zo da duk takardun da ake bukata.”

Bankunan First Bank, Zenith Bank, Guarantee Trust, Access Bank, Polaris, FCMB, Fidelity da Keystone na cikin masu amsa tambayoyin.

Kazalika kamfanin hakar mai na Shell Develompent Company da kamfanin lemon kwalba 7Up da kamfanin mai na Durbi Oil.

Sauran kamfonin abinci irin su C-Way Food & Beverages da kamfanin madarar Fan Milk da kamfanin Rite Food Ltd; Guinness Nigeria Plc; Pabod Int’l Breweries; Champion Breweries; Agio Power Plant (Kwale Okpai Power Plant); Euro-Global and Disability Plc.

Hukumomi da cibiyoyin gwamnati da za a bincika sun hada da; Ma’aikatar Noma da Samar da Abinci, wadda za a bincika kan zargin karkatar da kudaden tallafin COVID-19.

Sannan za a binciki Cibiyar Yaki da Yaɗuwar Cututtuka ta Kasa (NCDC) kan zargin karkatar da kudaden yaki da COVID-19.

Hukumar Gidan Radio ta Kasa (FRCN) kuma za ta amsa tambayoyi kan zirarewar kudaden shiga ta kafar Remita.

Sai Majalisar Karamar Hukumar Gwagwalada da za ta amsa tambayoyi kan zargin almundahana da rahoton shekarar 2020 da ofishin babban mai binciken kudi na kasa ya bankado.

Sauran da ake zargi a rahoton sun hada da: Ma’aikatar Tsaro, Matatar Mai ta Kaduna, Kamfanin Wutar Lantarki ta Kasa na kuma Hukumar Iskar Gas ta Kasa (NLNG) da Ma’aikatar Sufuri ta Kasa

Akwai kuma Hukumar Kula da Kamfanonin Gwamnati (BPE), Ma’aikatar Kasafi da Tsare-tsare, Jami’ar Sojoji da ke Jihar Borno, Ma’aikatar Ma’adinai, Hukumar Kogin Neja Delta, Ma’aikatar harkokin waje, Ma’aikatar Ilimi da Hukumar Jarabawa ta Kasa (NECO).

Hakazalika akwai Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) da Kamfanin Dillanccin Labaran Njjeriya (NAN) da Hukumar Aikin Dan Sanda da Cibiyar Yaki da Cutar Kuturta da Tarin Fuka da Hukumar Kidaya ta Kasa da sauransu da suka hada jami’o’i da kwalejin ilimi da cibiyoyin lafiya da sauransu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BUADangoteHarajiMajalisar Wakilai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Jirgin Arik Daga Yin Jigilar Fasinjoji Saboda Bashi

Next Post

Za Mu Dauki Fansar Kisan Haniyeh – Iran

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

19 hours ago
Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Soke Hawan Sallah, Ya Bayyana Dalili

1 day ago
Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi
Manyan Labarai

Saƙon Barka Da Sallah: Tinubu Ya Baiyana Tabbacin Ci Gaban Nijeriya, Da Sauyin Tattalin Arziƙi

1 day ago
Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa
Manyan Labarai

Abubuwan Da Ba A Fada Ba Game Da Mummunar Ambaliyar Ruwan Mokwa

1 day ago
Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

2 days ago
Next Post
Za Mu Dauki Fansar Kisan Haniyeh – Iran

Za Mu Dauki Fansar Kisan Haniyeh – Iran

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.