• English
  • Business News
Saturday, June 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daraktocin Da APC Ta Kora Sun Yi Zargin An Handame Biliyoyi A Jam’iyyar

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
in Siyasa
0
Daraktocin Da APC Ta Kora Sun Yi Zargin An Handame Biliyoyi A Jam’iyyar
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Rikici ya kara kamari a cikin jam’iyya mai mulki ta APC bayan korar daraktoci a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, inda suka zargi shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu da handame biliyoyi wanda suka tura masa a asusun sirri ba tare da sanin kwamitin gudanarwa ba.

Daraktocin da aka kora sun zargi shugaban jam’iyyarda handame naira biliyan uku daga asusun banki na sirri.

A ranar 22 ga watan Afriluce, Adamu ya dakatar dadukkan rassan daraktoci da keshalkwatan jam’iyyar a Abuja bisa zarginsu da cin hanci da rashawa.

  • Ba Mu Taba Ganin Ambaliyar Ruwa Mafi Muni A Nijeriya Kamar Ta Bana Ba – Gwamnati
  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Daraktocin sun hada da Elder Anietie Offong (Direktan walwala); Bartholomew I. Ugwoke (Daraktan bincike); Abubakar Suleiman (Daraktan kudade); Dakta Suleiman Abubakar (Daraktan gudanarwa); Salisu Na’inna Dambatta (Daraktan tallace-tallace) da kuma Dare Oketade (Daraktan lauyoyi).

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Adamu ya saura daraktocin. Tun lokacin da Adamu ya hau kan shugabancin jam’iyyar a ranar 1 ga watan Afrilu ya kafa kwamitin sauyi wanda tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Ali Saad Birnin Kudu ya ke jagoranta domin yin nazari kan shugabancin riko na Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni da sauran matsalolin da suke addabar jam’iyya.

Labarai Masu Nasaba

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

An dai bayyana cewa an kori daraktocin bias shawarar da kwamitin ya bayar.

Wakilin Jaridar Daily Trust ya bayyana cewa duk irin kokarin da ya yi na jin ta bakin kwamitin gudanarwa amma lamarin ya ci tura. Sai dai a makon da ya gabata lokacin da yake fira da manema labarai, Adamu ya zargi daraktocin da cin hanci da rashawa.

Ya ce shugabancinsa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga wurin kwamitin riko da Mai Mala Buni ya jagoranta.

Amma an musanta cewa bayanan da aka gabatar wajen korar daraktocin ciki har da shugaban sashin shari’a kwamitin bai bayar da shawara a sallame su ba tunda har yanzu ma’aikata ne na jam’iyya kuma dole a biya su hakkinsu.

Sun ce ikirarin da Adamu yake yi na cewa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga jagoranci Buni karya ya shirga, wanda hasalima suka zargi shi da bude asusun banki na sirri ba tare da amincewar kwamitin gudanarwa ba, sannan ya bukaci su saka masa naira biliyan uku a ciki.

Lokacin da aka tuntubi Adamu a wayar salula ya musanta ikirarin daraktocin, inda ya bayyana cewa an adana kudaden ne ba wai don a kasha ba.

“An dai adana wadannan kudade ne ba wai domin a kashe su ba wanda su kuma suke kallon akasin haka. Ni ba ni da abokin fada, domin ni ina fada ne da hujja. Duk wadanda suke zargin an kasha wadannan kudade su fito karara su bayyana hujjojinsu.

“Duk abin da nake yi a matsayina na Abdullahi Adamu na kan shawarci kwamitin gudanarwa domin amincewa da dukkan wani mataki da aka bijiro da shi,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCBadakalaDaraktociSanata Abdullahi Adamu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Next Post

Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

Related

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta
Siyasa

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

4 hours ago
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka
Manyan Labarai

Ganduje Ya Ajiye Shugabancin Jam’iyyar APC

8 hours ago
Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson
Siyasa

Zaɓen 2027 Ya Fi Damun Tinubu Fiye Da Gudanar Da Shugabanci – Sanata Dickson

12 hours ago
Gwamnatin APC Ta Kara Ingiza ‘Yan NIjeriya Cikin Bakin Talauci – PDP
Manyan Labarai

PDP Ta Soke Babban Taronta, Ta Dawo Da Anyanwu A Matsayin Sakatarenta

2 days ago
Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC
Manyan Labarai

Tinubu Ya Haƙura Da Tsayawa Takara A 2027 – Jigo A APC

4 days ago
An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027
Siyasa

An Fara Kiraye-Kirayen Tinubu Ya Zaɓi Barau Jibrin A Mataimakinsa Na 2027

4 days ago
Next Post
Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

Sin Na Kokarin Gaggauta Taimakawa Kasashen Afirka Da Kara Hadin Gwiwa Da Su

June 27, 2025
Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

Sin Da Amurka Sun Tabbatar Da Bayanan Tsarin Aiwatar Da Matsayar Da Aka Cimma Yayin Tattaunawar Cinikayya A Geneva

June 27, 2025
Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

Sojojin DRC: Ƴan Tawayen M23 Sun Kashe Fararen Hula 17

June 27, 2025
Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

Leicester City Ta Sallami Ruud van Nistelrooy A Matsayin Kocinta

June 27, 2025
Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

Xinjiang Ta Bude Hanyar Jigilar Kayayyaki Ta Kasa Da Kasa Zuwa Afirka Ta Farko

June 27, 2025
Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

Abubuwan Da Tsofaffin Shugabannin Nijeriya Suka Fuskanta Bayan Barin Mulki

June 27, 2025
Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

Lai Cing-te Ba Zai Cimma Nasarar Kalubalantar Dokar Kasa Da Kasa Ba

June 27, 2025
JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

JAMB Ta Ayyana 28 Ga Yuni Don Ɗaliban Da Za Su Sake Rubuta Jarabawa

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

Abin Da Ya Sa Muke Ci Gaba Da Tuntubar Kasar Sin A Kai A Kai

June 27, 2025
Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

Abin Da Ya Sa Ilimi Yake Da Muhimmanci Ga Rayuwar Al’umma (7)

June 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.