• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daraktocin Da APC Ta Kora Sun Yi Zargin An Handame Biliyoyi A Jam’iyyar

by Yusuf Shuaibu
3 years ago
APC

Rikici ya kara kamari a cikin jam’iyya mai mulki ta APC bayan korar daraktoci a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, inda suka zargi shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu da handame biliyoyi wanda suka tura masa a asusun sirri ba tare da sanin kwamitin gudanarwa ba.

Daraktocin da aka kora sun zargi shugaban jam’iyyarda handame naira biliyan uku daga asusun banki na sirri.

A ranar 22 ga watan Afriluce, Adamu ya dakatar dadukkan rassan daraktoci da keshalkwatan jam’iyyar a Abuja bisa zarginsu da cin hanci da rashawa.

  • Ba Mu Taba Ganin Ambaliyar Ruwa Mafi Muni A Nijeriya Kamar Ta Bana Ba – Gwamnati
  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Daraktocin sun hada da Elder Anietie Offong (Direktan walwala); Bartholomew I. Ugwoke (Daraktan bincike); Abubakar Suleiman (Daraktan kudade); Dakta Suleiman Abubakar (Daraktan gudanarwa); Salisu Na’inna Dambatta (Daraktan tallace-tallace) da kuma Dare Oketade (Daraktan lauyoyi).

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Adamu ya saura daraktocin. Tun lokacin da Adamu ya hau kan shugabancin jam’iyyar a ranar 1 ga watan Afrilu ya kafa kwamitin sauyi wanda tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Ali Saad Birnin Kudu ya ke jagoranta domin yin nazari kan shugabancin riko na Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni da sauran matsalolin da suke addabar jam’iyya.

LABARAI MASU NASABA

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

An dai bayyana cewa an kori daraktocin bias shawarar da kwamitin ya bayar.

Wakilin Jaridar Daily Trust ya bayyana cewa duk irin kokarin da ya yi na jin ta bakin kwamitin gudanarwa amma lamarin ya ci tura. Sai dai a makon da ya gabata lokacin da yake fira da manema labarai, Adamu ya zargi daraktocin da cin hanci da rashawa.

Ya ce shugabancinsa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga wurin kwamitin riko da Mai Mala Buni ya jagoranta.

Amma an musanta cewa bayanan da aka gabatar wajen korar daraktocin ciki har da shugaban sashin shari’a kwamitin bai bayar da shawara a sallame su ba tunda har yanzu ma’aikata ne na jam’iyya kuma dole a biya su hakkinsu.

Sun ce ikirarin da Adamu yake yi na cewa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga jagoranci Buni karya ya shirga, wanda hasalima suka zargi shi da bude asusun banki na sirri ba tare da amincewar kwamitin gudanarwa ba, sannan ya bukaci su saka masa naira biliyan uku a ciki.

Lokacin da aka tuntubi Adamu a wayar salula ya musanta ikirarin daraktocin, inda ya bayyana cewa an adana kudaden ne ba wai don a kasha ba.

“An dai adana wadannan kudade ne ba wai domin a kashe su ba wanda su kuma suke kallon akasin haka. Ni ba ni da abokin fada, domin ni ina fada ne da hujja. Duk wadanda suke zargin an kasha wadannan kudade su fito karara su bayyana hujjojinsu.

“Duk abin da nake yi a matsayina na Abdullahi Adamu na kan shawarci kwamitin gudanarwa domin amincewa da dukkan wani mataki da aka bijiro da shi,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

APC
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta
Siyasa

Jam’iyyar NNPP A Kaduna Ta Ƙaryata Batun Tsige Shugabanta

October 24, 2025
ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa
Siyasa

ADC Ta Gargaɗi Gwamnatin Tarayya Kan Amfani da Zargin Juyin Mulki Wajen Yaƙar ‘Yan Adawa

October 22, 2025
Next Post
Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

APC

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Da Burgediya Janar Yake a Matsayin Sarkin Ƙabilar Sayawa

October 27, 2025
Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

Yawan Jigilar Kayayyakin Dake Bukatar Kankara a Kasar Sin Ya Zarce Tan Miliyan 117 a Watannin Yuni Da Yuli Da Agusta

October 27, 2025
Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

Sin Za Ta Yi Tsayin Daka Wajen Kare Tsarin Cinikayya Tsakanin Mabanbantan Sassa

October 27, 2025
Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

Xi Ya Halarci Nune-Nune A Babban Gidan Adana Kayan Tarihi Na Karni

October 27, 2025
Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

Shugaba Tinubu Ya Gana Da Sabbin Hafsoshin Tsaro

October 27, 2025
Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

Mutanen Katsina Sun Koka Kan Dakatar da Aikin Gyaran Hanyar Mararrabar Kankara–Dutsinma–Katsina

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.