ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, July 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daraktocin Da APC Ta Kora Sun Yi Zargin An Handame Biliyoyi A Jam’iyyar

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
APC

Rikici ya kara kamari a cikin jam’iyya mai mulki ta APC bayan korar daraktoci a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, inda suka zargi shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu da handame biliyoyi wanda suka tura masa a asusun sirri ba tare da sanin kwamitin gudanarwa ba.

Daraktocin da aka kora sun zargi shugaban jam’iyyarda handame naira biliyan uku daga asusun banki na sirri.

A ranar 22 ga watan Afriluce, Adamu ya dakatar dadukkan rassan daraktoci da keshalkwatan jam’iyyar a Abuja bisa zarginsu da cin hanci da rashawa.

ADVERTISEMENT
  • Ba Mu Taba Ganin Ambaliyar Ruwa Mafi Muni A Nijeriya Kamar Ta Bana Ba – Gwamnati
  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Daraktocin sun hada da Elder Anietie Offong (Direktan walwala); Bartholomew I. Ugwoke (Daraktan bincike); Abubakar Suleiman (Daraktan kudade); Dakta Suleiman Abubakar (Daraktan gudanarwa); Salisu Na’inna Dambatta (Daraktan tallace-tallace) da kuma Dare Oketade (Daraktan lauyoyi).

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Adamu ya saura daraktocin. Tun lokacin da Adamu ya hau kan shugabancin jam’iyyar a ranar 1 ga watan Afrilu ya kafa kwamitin sauyi wanda tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Ali Saad Birnin Kudu ya ke jagoranta domin yin nazari kan shugabancin riko na Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni da sauran matsalolin da suke addabar jam’iyya.

LABARAI MASU NASABA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

An dai bayyana cewa an kori daraktocin bias shawarar da kwamitin ya bayar.

Wakilin Jaridar Daily Trust ya bayyana cewa duk irin kokarin da ya yi na jin ta bakin kwamitin gudanarwa amma lamarin ya ci tura. Sai dai a makon da ya gabata lokacin da yake fira da manema labarai, Adamu ya zargi daraktocin da cin hanci da rashawa.

Ya ce shugabancinsa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga wurin kwamitin riko da Mai Mala Buni ya jagoranta.

Amma an musanta cewa bayanan da aka gabatar wajen korar daraktocin ciki har da shugaban sashin shari’a kwamitin bai bayar da shawara a sallame su ba tunda har yanzu ma’aikata ne na jam’iyya kuma dole a biya su hakkinsu.

Sun ce ikirarin da Adamu yake yi na cewa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga jagoranci Buni karya ya shirga, wanda hasalima suka zargi shi da bude asusun banki na sirri ba tare da amincewar kwamitin gudanarwa ba, sannan ya bukaci su saka masa naira biliyan uku a ciki.

Lokacin da aka tuntubi Adamu a wayar salula ya musanta ikirarin daraktocin, inda ya bayyana cewa an adana kudaden ne ba wai don a kasha ba.

“An dai adana wadannan kudade ne ba wai domin a kashe su ba wanda su kuma suke kallon akasin haka. Ni ba ni da abokin fada, domin ni ina fada ne da hujja. Duk wadanda suke zargin an kasha wadannan kudade su fito karara su bayyana hujjojinsu.

“Duk abin da nake yi a matsayina na Abdullahi Adamu na kan shawarci kwamitin gudanarwa domin amincewa da dukkan wani mataki da aka bijiro da shi,” in ji shi.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku

MASU ALAKA

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci
Siyasa

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo
Manyan Labarai

ADC Ta Rushe Shugabannin Jam’iyyar A Kano, Ta Naɗa Kwamitin Riƙo

July 6, 2026
Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija
Siyasa

Jam’iyyar PDP Ce Za Ta Dawo Da Kwanciyar Hankali A Nijeriya – Hajiya Khadija

July 5, 2026
Next Post
Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga A Wani Ƙauyen Katsina

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Ibrahim Aliyu Na Ci Gaba Da Rasa Tasiri A Harkar Fili Da Gidaje A Yankin Abuja

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Fafutukar Neman Sabon Sakataren Majalisar Ɗinkin Duniya

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Yadda Jana’izar Ruhullah Khomeini Ta Shiga Kundin Tarihi Na Guinness

July 10, 2026
NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

NIMC Ta Yi Haɗin Gwuiwa Da Ma’aikatun Gwamnati Don Faɗaɗa Rajistar NIN

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

“Mutunta Ƴancin Addinai Ita Ce Hanyar Wanzar Da Zaman Lafiya A Kaduna”

July 10, 2026
Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Falalar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

July 10, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya

July 10, 2026
Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

Shugaban Miyetti Allah, Bodejo Ya Karyata Zargin Halatta Kudin Haram A Zaman Kotu

July 10, 2026
Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

Tinubu Ya Nemi Amincewar Majalisar Kan Gyaran Kudirin Dokar Shari’ar Manyan Laifuka

July 10, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.