ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, June 13, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daraktocin Da APC Ta Kora Sun Yi Zargin An Handame Biliyoyi A Jam’iyyar

by Yusuf Shuaibu
4 years ago
APC

Rikici ya kara kamari a cikin jam’iyya mai mulki ta APC bayan korar daraktoci a sakateriyar jam’iyyar da ke Abuja, inda suka zargi shugaban jam’iyyar, Sanata Abdullahi Adamu da handame biliyoyi wanda suka tura masa a asusun sirri ba tare da sanin kwamitin gudanarwa ba.

Daraktocin da aka kora sun zargi shugaban jam’iyyarda handame naira biliyan uku daga asusun banki na sirri.

A ranar 22 ga watan Afriluce, Adamu ya dakatar dadukkan rassan daraktoci da keshalkwatan jam’iyyar a Abuja bisa zarginsu da cin hanci da rashawa.

ADVERTISEMENT
  • Ba Mu Taba Ganin Ambaliyar Ruwa Mafi Muni A Nijeriya Kamar Ta Bana Ba – Gwamnati
  • Sin Tana Maraba Da Kiran Taron Sulhu Tsakanin Al’ummomin Libya

Daraktocin sun hada da Elder Anietie Offong (Direktan walwala); Bartholomew I. Ugwoke (Daraktan bincike); Abubakar Suleiman (Daraktan kudade); Dakta Suleiman Abubakar (Daraktan gudanarwa); Salisu Na’inna Dambatta (Daraktan tallace-tallace) da kuma Dare Oketade (Daraktan lauyoyi).

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa Adamu ya saura daraktocin. Tun lokacin da Adamu ya hau kan shugabancin jam’iyyar a ranar 1 ga watan Afrilu ya kafa kwamitin sauyi wanda tsohon gwamnan Jihar Jigawa, Ali Saad Birnin Kudu ya ke jagoranta domin yin nazari kan shugabancin riko na Gwamnan Jihar Yobe, Mai Mala Buni da sauran matsalolin da suke addabar jam’iyya.

LABARAI MASU NASABA

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

An dai bayyana cewa an kori daraktocin bias shawarar da kwamitin ya bayar.

Wakilin Jaridar Daily Trust ya bayyana cewa duk irin kokarin da ya yi na jin ta bakin kwamitin gudanarwa amma lamarin ya ci tura. Sai dai a makon da ya gabata lokacin da yake fira da manema labarai, Adamu ya zargi daraktocin da cin hanci da rashawa.

Ya ce shugabancinsa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga wurin kwamitin riko da Mai Mala Buni ya jagoranta.

Amma an musanta cewa bayanan da aka gabatar wajen korar daraktocin ciki har da shugaban sashin shari’a kwamitin bai bayar da shawara a sallame su ba tunda har yanzu ma’aikata ne na jam’iyya kuma dole a biya su hakkinsu.

Sun ce ikirarin da Adamu yake yi na cewa ya gaji bashin naira biliyan 7.5 daga jagoranci Buni karya ya shirga, wanda hasalima suka zargi shi da bude asusun banki na sirri ba tare da amincewar kwamitin gudanarwa ba, sannan ya bukaci su saka masa naira biliyan uku a ciki.

Lokacin da aka tuntubi Adamu a wayar salula ya musanta ikirarin daraktocin, inda ya bayyana cewa an adana kudaden ne ba wai don a kasha ba.

“An dai adana wadannan kudade ne ba wai domin a kashe su ba wanda su kuma suke kallon akasin haka. Ni ba ni da abokin fada, domin ni ina fada ne da hujja. Duk wadanda suke zargin an kasha wadannan kudade su fito karara su bayyana hujjojinsu.

“Duk abin da nake yi a matsayina na Abdullahi Adamu na kan shawarci kwamitin gudanarwa domin amincewa da dukkan wani mataki da aka bijiro da shi,” in ji shi.

APC
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Hukuncin Kotu Na Barazana Ga Zaben 2027 —INEC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Matsalar Tsaro Da Tsadar Kayan Noma Na Barazana Ga Samar Da Abinci A Daminar Bana

MASU ALAKA

ADC Ta Fara Sayar Da Fom Din Takara Kafin Babban Taron Jam’iyya
Siyasa

2027: ADC Ta Fara Sulhunta Mambobinta Da Ba Su Gamsu Da Zaɓen Fidda Gwani Ba A Kaduna

June 9, 2026
A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara
Siyasa

A Ƙarshe Jamilu Gwamna Ya Samu Babbar Dama Ta Yin Takara

June 8, 2026
Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere
Siyasa

Shugabannin NDC Na Arewa Maso Yamma Sun Zargi Kwankwaso Da Ƙoƙarin Babakere

June 8, 2026
Next Post
Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

Mutane 197 Sun Kamu Da Cutar Kwalara A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

Wannan Hakki Na Tushe Yana Da Matukar Muhimmanci

June 13, 2026
An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

An Cafke Mutum Uku Kan Kisan Mawaki Dan Asalin Nijeriya Da Birtaniya

June 13, 2026
Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

Allah Kaɗai Zai Iya Kawo Ƙarshen Matsalar Tsaro A Nijeriya – Matawalle

June 13, 2026
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutun Biyu Da Ake Zargi Da Fashi Da Makami A Adamawa

June 13, 2026
Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

Kamfanin Simintin Dangote Ya Kaddamar Da Tsarin Fasahar Zamani (AI) Domin Inganta Tsaro Da Harkar Sufuri

June 13, 2026
Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

Tsohon Kakakin Ma’aikatar Tsaro Rabe Abubakar Ya Rasu A Hannun ‘Ƴan Bindiga

June 13, 2026
Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

Yadda Matata Ta Daina Girki, Ta Ke Lakaɗamin Duka — Miji Ya Koka

June 13, 2026
Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

Ranar Dimokuraɗiyya: Gwamna Uba Sani Ya ‘Yanta Fursunoni 97

June 13, 2026
Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

Bukatar Rike Sirri A Tsakanin Ma’aurata

June 13, 2026
Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

Hukumar FAO Ta Samar Da Shirin Kiwon Tarwada A Jihar Gombe

June 13, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.