• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Darussan Kiyayewa Daga Hadurran Tankar Mai

by Leadership Hausa
10 months ago
in Manyan Labarai
0
Darussan Kiyayewa Daga Hadurran Tankar Mai
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A cikin watan Oktoba 2024 ne wata tankar Man fetur ta yi hatsarin inda bayan dan lokaci ta kama da wuta a kauyen Majiya da ke karamar hukumar Taura ta Jihar Jigawa.

Hatsarin wanda ya zuwa yanzu, adadin wadanda suka rasu bayan bindigar da tankar ta yi, sun kai 181, tare kuma mutane fiye da 90 da aka kwantar a asibitoci, domin a duba lafiyarsu.

  • Ba Zan Goyi Bayan Ƙudirin Ƙarin Haraji Ga Talakawa Ba – Sanata Ndume
  • Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya NaÉ—a Manjo Janar Olufemi MuÆ™addashin Babban Hafsan Sojin Ƙasa

Abin nazari a nan shi ne, ba wai kawai aukuwar hatsarin ne abin dubawa ba, amma a zahiri, abin bakin ciki dangane da hatsarin shi ne,yadda yanayin tsarin kasar nan yake, musamman ma na kasa yin wani hobbasan kare rayukan ‘yan Nijeriya marasa karfi a duk lokacin da wani abu irin wannan bala’in ya auku.

Gwamnan Jihar Malam Umar Namadi, a cikin jimamin sanar da yawan adadin wadanda suka rasa rayukansu a hatsarin, ya ce, wani dan bangare na hatsarin kawai ya bayyana wasu al’umma saboda munin lamarin.

Sai dai, kuma a bayan aukuwar wannan hatsarin, akwai wasu sauran iyalai da wasu al’ummomi da ke a yankin da hatsarin ya auku ya janyo tarwatsa rayuwarsu.

Labarai Masu Nasaba

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Har zuwa yanzu dai, tambayar da ake ta famar yi ita ce, shin ta yaya ne, hatsarin ya auku?

Koda yake dai, a martanin da Shugaba kasa Bola Tinubu yayi bayan aukuwar lamarin, ya ba ‘yan Nijeriya tabbacin cewa, gwamnatinsa ta hanyar yin hadaka da gwamnatocin jihohi, za su yi gaggawar daukar matakai a kan aukuwar irin wannan lamarin da kuma yin nazari a kan tsarin yadda ake jigilar man fetur a tankokin man a daukacin kowane sako da lungu na Nijeriya

Kazalika, Tinubu ya umarci hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC), da ta kara karfafa matakan yin tafiye-tafiye wadanda suka hada da kara yawan yin sintiri a kan hanyoyin kasar nan, tsaurara bin dokokin yin tuki da saura matakai a kan manyan hanyoyin kasar nan.

Tinubu ya kara da cewa, duk kuma direban da aka samu ya karya su dokokin tukin, duk abinda ya faru da shi, shi ya ja wa kansahi,ya kuma bayar da tabbacin cewar, gwamnatinsa za ta tabbatar da an kiyaye aukuwar irin wadannan hadurran a kasa a nan baki daya.

Sai dai, tambayar mu a nan ita ce, shin wane mataki ne ya dace a dauka akan karuwar asarar yawan rayukan ake za a rika yi kafin Nijeriya ta lalubo da mafita a kan makasudin aukuwar irin wannan annobar ta hatsarin?

Tankar man dai, ta juya ne a babbar hanyar wadda hanyar da ba ta samun kulawar da ta kamata ba.

Wani karin abin takaici anan shi ne, yadda daruruwan mutane a yankin suka fake da kangin talaucin da suke fuskanta, su kai ta yin fitar Farin dango domin zuwa kwasar ganimar man a cikin bokitansu, wanda ba su riga sun farga ba, tartsatsin wuta ya tashi, tankar ta yi bindiga, ta jefa kasar nan a cikin zaman makoki. Aukuwar lamarin dai, bai da wata sarkakiya a cikinsa.

Bugu da kari, bisa rahotannin Hukumar kiyaye haddura ta kasa (FRSC) na 2020 ya nuna cewa, akwai sama da hatsari tankar mai guda 1,500 da suka auku a Nijeriya, wanda hakan ya yi sanadiyar mutuwar mutane fiye 535.

A kwana- kwanan nan irin wannan hatsarin ya auku a Jihar Neja, inda mutane 48 suka rasa rayukansa.

Har-ila-yau, har yanzu ana ci gaba da jimamin tashin wutar da ta auku ta kuma lakume ababen hawa a kan babbar hanyar Ibadan zuwa Ife. Aukuwar wadannan hadduran kawai, sun isa a ce, ba a gamsu da matakan da ake dauka na magance aukuwar lamuran ba a kasa.

Na daya, dogaron da aka yi gaba daya wajen yin jigilar man a hanya domin rabar da man, abu ne da ke da hadarin gaske kuma wanda bai wadatar ba.

Har ila yau, rashin samar da ingancen tsarin safarar kaya a cikin Jirgin kasa a kasar nan, na daga cikin abinda ke janyo ci gaba da asarar rayukan matafiya, bayan alhali, kasashen da suka ci gaba, tuni sun dade suna yin amfani da tsari na zamani, wajen yin jigilar kaya.

Irin wannan annobar da ke faruwa, na da nasaba ne da matsin tattalin arziki da kasar nan ke fama da shi.

Idan aka yi la’akari da yadda wasu talakawan kasar suka sayar da rayuwarsu domn fita kwasar ganimar man, bayan tankokin mai sun fadi, hakan yana nunawa a karara, cewa, talauci ya yiwa wasu al’umomin kasar daurin dema minti.

Bugu da kari, iftibila’in da ya auku na fashewar bututun mai a yankin Jesse a 1998, lamarin ya lakume rayuka sama da 1,000, wanda har yanzu, ana ci gaba da jimamin aukuwar lamarin a kasar.

Kazalika, bayan shekaru sha biyu, sai kuma ace ga irin makamancin i wannnan iftibila’in ya kara aukuwa.

A bisa ra’ayin wannan jaridar, duba da cewa, ra’ayoyin za su iya ban-banta, amma wadannan matsalolin da aka zayyana a sama, har yanzu lamurran ba su sauya ba, musamman kangin talauci, damuwa da kuma karancin kayan aiki.

Har yanzu, ana ci gaba da samun yin bindigar tankokin dakon man wanda kuma sai asarar rayuka, ake kara samu.

Da farko, dole ne mu sauya zuwa yin amfani da tsari na zamani wajen safarar kaya, musamman ma ta hanyar samar da kyakyawan tsarin yin amfani da hanyar Jirgin kasa.

Na biyu kuma, ya zama wajibi a karfafa kiyaye dokokin yin tuki, musamman a lokacin da tankokin mai suka yo dakon man, don kai shi wurin da ya dace su je.

Ya dakyau direbobi a Nijeriya su tabbatar da suna duba lafiyar motocin su dakayu, kafin su fara tunanin fara yin aiki da su.

Sai abu na uku, ya zama wajibi ne mu magance kalubalen da talauci ke jefa ‘yan Nijeriya, wajen daukar irin wadancan matakan.

Bama kamar yadda wasu mutanen suka gwammace su sadaukar da kansu domin zuwa kwasar ‘yar ganimar litocin man, wannan ya nuna yadda mahukunta a kasar, suka kasa samarwa ‘yan kasar kayan biyan bukatunsu yau da kullum.

Iftibla’in da ya auku a Jigawa, abu ne da ya kamata ya zama izina, dangane da jigilar mai ta hanyar yin amfani da hanya, inda kuma a gefe, daya ya nuna cewa, ana fuskantar talauci a kasar Nijeriya.

Wadannan hadurran da suka auku, dama an yi hasashen aukuwarsu, wadanda kuma za a iya dakile aukuwar ta su, wanda hakan ya nuna gazawar mahukunta, wajen kare rayukan ‘yan Nijeria

Idan har ba mu sanya niyyar yin gyara akan lamarin ba, musamman ma ta hanyar samar da sauye-sauye, to tabbas, za a ci gaba da samun asarar rayuka.

Ya kamata ace an inganta rayuwar al’umma, mai makon sai idan wata tankar mai ta fadi ne, za su je kwasar ganima domin biyan bukatun su na yau da kullum ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BindigaHatsariJigawaTankar Mai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mene Ne Ainihin Abun Da Philippines Ta Samu Daga Wajen Amurka?

Next Post

Dauke Lantarkin Arewa

Related

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP
Manyan Labarai

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

7 hours ago
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

19 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

1 day ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

1 day ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu ÆŠaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Next Post
Dauke Lantarkin Arewa

Dauke Lantarkin Arewa

LABARAI MASU NASABA

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

Tanko Yakasai Ya Nuna Takaici Kan Rashin Samar Da Kamfanin Sarrafa Fata A Kano Kamar Na Legas

August 24, 2025
An Harbe Fitaccen Dan Bindigan Da Ya Addabi Mazauna Abuja A Sansaninsa

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3, Sun Kwato AK-47 A Kebbi

August 24, 2025
Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

Wike Bai Isa Ya Hana Mu Babban Taron Jam’iyyarmu Ba – Gwamnonin PDP

August 24, 2025
Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

Trump Ya Ce Zai Yi Duk Mai Yiwuwa Don Ganawa Da Putin Da Zelensky Lokaci Guda

August 24, 2025
Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

Fabio Na Brazil Ya Kafa Sabon Tarihi A Kwallon Kafa

August 24, 2025
Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

Babban Burina A Harkar Fim Shi Ne Ganin Habakar Harshe Da Al’adun Hausa—Murtala Abdullah

August 24, 2025
NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.