• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani

by Sulaiman
3 years ago
in Labarai
0
Dattawan Arewa Sun Yi Tir Da Kalaman Gwamna Ortom Kan Ƙyamar Fulani
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Kungiyar Dattawan Arewa (NEF) ta bayyana kalaman da gwamnan jihar Binuwai, Samuel Ortom ya yi a matsayin ‘masu tsauri’, wanda a lokacin da yake yin Allah wadai da kisan mutane 18 da aka yi a yankin karamar hukumarsa a ranar Juma’ar da ta gabata ya ce ba zai taba goyon bayan wani Bafulatani ya sake zama shugaban kasar Najeriya.

 

Ortom ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar bakuncin takwarorinsa na jihohin Rivers, Oyo, Abia da Enugu a wani liyafar cin abinci a Makurdi, ya ce: “Kuna so in zama bawa ga Bafulatani. Gara in mutu. Ana kashe mutanena kuna so in yi shiru. Ba zan taba goyon bayan Bafulatani ya zama shugaban kasa ba. Idan kuma akwai wani wanda yake shirye ya yi aiki tare da ni don tabbatar da tsaron jama’ata, zan yi aiki da shi.”

  • Abin Da Ya Sa Muka Gamsu Da Manufofin Kwankwaso – Matasan Arewa A Legas

Sai dai kungiyar dattawan Arewa a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Laraba mai dauke da sa hannun Daraktan yada labarai da fa’ida, Dakta Hakeem Baba-Ahmed, ta ce kalaman Gwamnan kwata-kwata bai dace da shugaba ba, musamman a daidai lokacin da ake siyasantar da matsalar rashin tsaro a kasar nan.

 

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Kungiyar ta ce, “mu ma kamar sauran ‘yan Najeriya, mun kalli bidiyon da Gwamnan Jihar Binuwai, Samuel Ortom ke magana a cikin yanayi da kuma yare da bai dace da shugaba ba.

 

“Kungiyar Dattawan Arewa ta ci gaba da yin Allah-wadai da yanayin kawanya da rashin tsaro da ‘yan Nijeriya suka yi rayuwa a ƙarƙashinsu a cikin ‘yan shekarun nan. Musamman a Arewa ‘yan damfara fulani sun yi fice a matsayin masu kisa da ‘yan fashi da masu garkuwa da mutane.

 

“Ya kamata gwamna Ortom ya cika rantsuwar da ya yi da kuma alkawarin da ya yi na yin rayuwa a matsayinsa na shugaban al’ummarsa.

 

“Ya kamata ya guje wa sha’awar buga wasan kwaikwayo wanda, kamar sauran ‘yan Najeriya, ke da burin samun sauki da kuma kawo karshen kashe-kashen da ke tayar da juna da kuma kai su ga rikice-rikice marasa iyaka.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

IBB Na Kokarin Kawo Karshen Sabanin Da Ke Tsakanin Atiku Da Gwamnonin PDP ‘Yan 5 

Next Post

Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

3 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

5 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

6 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

10 hours ago
Ortom
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

11 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

12 hours ago
Next Post
Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

Shirin Nijeriya Na Yaki Da Talauci A Duniya

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.