• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dattawan Arewa Za Su Gabatar Wa Tinubu Shawarwari Kan Tattalin Arziki Da Tsaro

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
Dalilin Kotu Na Dakatar Da Yanke Hukunci Kan Karar Zaben Tinubu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dattawan arewa a karkashin kungiyar ‘Arewa New Agenda’ (ANA) sun kimtsa tunkarar gwamnatin tarayya tare da shawarorin kan matakan da za a bi wajen magance matsalolin tsaro da matsin rayuwa, musamman a yankin arewa da ma Nijeriya baki daya.

A cewar dattawan, shawarrarin muddin aka amsa kuma aka yi amfani da su, la-shakka za su kawo karshen matsalolin da suka addabi kasar nan.

  • Gwamnatin Jigawa Ta Amince Da Kashe Naira Biliyan Ɗaya Don Aikin Kiwon Lafiya Kyauta Ga Marasa Ƙarfi A Jihar
  • Za Mu Daidaita Farashin Abinci Kafin Watan Ramadan – ‘Yan Kasuwar Kano

Tsohon sakataren gwamnatin tarayya, Yayale Ahmed, shi ne ya sanar da hakan a lokacin bude taron tattauna hanyoyin yadda za a bi wajen dakile matsalar yunwa a arewacin Nijeriya wanda ya gudana a Abuja a karshen mako.

A Ado Ekiti ta Jihar Ekiti, dattijo kuma babban lauya (SAN), Afe Babalola, ya nemi Shugaban Kasa, Bola Tinubu da ya aiwatar da matakan da za su kai ga kawo karshen matsalar tattalin arziki da tsaro da ‘yan Nijeriya ke fama da su, yana mai cewa matsalolin na matukar ruguza kasar nan.

Shugaban ANA, Ahmad MoAllahyidi, shi ne ya gabatar da shawarorin ga dattawan da suka hada da tsoffin gwamnoni, Isa Yuguda, Sani Yerima, Jonathan Zwingina,  Babangida Ngoruje, tsohon shugaban ma’aikata na tarayya, Danladi Kifasi, Fatima Adams da shugaban hukumar alhazai, Jalal Arabi.

Labarai Masu Nasaba

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ahmed ya ce, “A matsayinmu na dattawa, mun cimma matsayar gabatar da kanmu domin hidimta wa Nijeriya da kuma ganin mun ciyar da arewacin kasar nan gaba ba wai don mun karaya ba, saboda don mun kasance masu gaskiya.

“Muna son mu canza tsarinmu da dabarunmu wajen magance matsalolin da suka addabi arewacin Nijeriya.

“Nauyin da ke kanmu ba wai kawai mu ce gwamnati ba ta gudanar da aikin da ke kanta ba ne, dole ne gwamnati ta yi aiki tukuru tare da gudunmawa, dole ne gwamnati ta kasance mai daukan dawainiya ta hanyar jajircewarmu.

“Mu kungiyar ‘yan Nijeriya ne masu kishi, sakamakon wannan yunkurin namu za a sanar da jama’an da ke da karfin ikon inganta rayuwar al’umma baki daya.”

Kungiyar ANA ta ce akwai bukatar gwamnatin tarayya ta tallafa wa arewa ta hanyar aiwatar da dokar fara kasuwanci na 2022. A cewarta, wannan kai tsaye zai taimaka wa kamfanonin da suke yankin wajen gudanar da bincike, samar da horaswa da kuma fitar da kayayyaki daidai da yadda ake yinsu a duniyance.

Shugaban ANA ya ce shawarorin za su ba da damar bunkasa harkokin da suka shafi na noma da kuma taimaka wa kowace jiha da ke arewacin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Har Yanzu Tinubu Na Biyan Tallafin Mai Ta Bayan Fage – IMF

Next Post

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

Related

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi
Labarai

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

1 hour ago
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi
Labarai

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

4 hours ago
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza
Labarai

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

13 hours ago
Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 
Labarai

Bashir Ojulari: Me Ya Sa Ake Tsoron Gaskiya Ta Yi Aiki A NNPC? 

15 hours ago
Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa
Labarai

Gwamnatin Kaduna Ta Amince Da Hutun Wata 6 Ga Mata Masu Shayarwa

15 hours ago
’Yansanda Sun Kama ’Yan Bindiga 17 Tare Da Kashe 3 A Abuja
Labarai

An Hallaka Manomi, An Kashe Shanu Da Tumakai A Wani Sabon Rikici A Bogoro

15 hours ago
Next Post
Amurka

Martanin Gwamnatin Tinubu Ga PDP: Matsalar Nijeriya Ba Ta Kai Ta Kasar Venezuela Ba

LABARAI MASU NASABA

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

Ina Fatan Taka Inda Yayana Ya Taka A Fagen Ƙwallon Ƙafa A Duniya -Jobe Bellingham

August 9, 2025
Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

Sai An Magance Matsalar Asusun Haɗin Gwiwa, Za A Tabbatar Da Cin Gashin Kan Ƙananan Hukumomi

August 9, 2025
Tinubu Ya Gwangwaje Ƴan Wasan Ƙwallon Kwando Ta Mata Da Dala $100,000 Kowace

Jerin Ƴan Wasa Mata Da Suka Samu Kyautar Dala 100,000 Daga Gwamnatin Nijeriya

August 9, 2025
Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

Afrika Ba Ta Cikin Jerin Fannonin Da Muke Ba Fifiko – Amurka

August 9, 2025
Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

Ƴan Bindiga Sun Sace Fasinjoji 9 A Kogi

August 9, 2025
ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

ADA/ADC, APC Da PDP: Jam ’iyyun Siyasa Da Ke Shan Jinin ’Yan Nijeriya

August 9, 2025
Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

Xi Jinping Ya Zanta Da Putin Ta Wayar Tarho

August 8, 2025
Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

Gwamnatin Tarayya da Ofishin Jakadancin Amurka Sun Haɗa Gwiwa Don Wayar Da Kan ‘Yan Nijeriya Kan Sababbin Ƙa’idojin Samun Biza

August 8, 2025
Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

Shin Amurka Ta Manta Da Azabar “Babban Koma-Baya” Tare Da Haraji Mafi Yawa a Lokacin Na Tsawon Kusan Karni?

August 8, 2025
Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

Nijeriya Ta Horar Da Likitoci 360 Don Magance Mutuwar Mata Masu Juna Biyu

August 8, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.