• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daukakar Nasaba Da Girman Garinsa (SAW)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
7 months ago
in Dausayin Musulunci
0
Daukakar Nasaba Da Girman Garinsa (SAW)
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Suna daga cikin abin da ba a bukatar a kafa dalili a kansu, in dai kai musulmi ne ba ka bukatar sai an gaya maka daukakar danginsa da girman garinsa da girman inda ya taso, ko ka ce akwai wani bayani mai rikitarwa da sai an maka bayaninsu, ko akwai wani abu boyayye a ciki, shi Annabi (SAW) zababben Bani Hashim ne, ta bangaren kyau, iya magana, Ilimi da dukkan alheri, haka aka san ‘ya’yan Hashimu da wadannan kyawawan halitta.

Ya ishe mu alfahari cewa duk kyawun Abdulmuddalibi, shi ne shugaban Bani Hashim amma gashi yana wa Annabi waka yana cewa “Wa Ab’yadu yustaskal gamamu bi wajhihi, simalul yatama ismatun lil aramili – fari ne wanda da albarkar fuskarsa ake shayar da girgije, Uban marasa Uba kuma mijin mata gwagware.

  • Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)
  • Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW) II

“Takdi bihin nakatul ajma’u mu’utajiran bil burdikal badri jalla lailataz zulami – rakumi yanayin taku daidai da shi, ya lulluba da bargo kai ka ce wata ne da ya bayyana a cikin dare mai duhu.

“Yaluzu bihil hullaku min ali Hashimin, wahum indahum fi ni’imatin wa fawadili – Halakakkun Bani Hashim da shi suke fakewa, kuma shi (Annabi SAW) mai ni’ima ne da babbar daraja a wajensu”

Shi ne zababben Bani Hashim, haifaffen Bani Hashim, shi ne mafi daukakan Larabawa kuma mafi buwayarsu ta dukkan bangare na Mahaifinsa da bangaren mahaifiyarsa duk babu kamarsa sannan kuma dan garin Makkah ne wacce ita ce mafi girman garuruwan Allah da wajen bayin Allah.

Labarai Masu Nasaba

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

Alkalin Alkalai ya yi mana Hadisi, Hussaini bin Muhammadus Sadafiyyu (Allah Ya rahamshe shi) ya ruwaito Hadisi inda ya daga Salsalar hadisin har zuwa Abu Hurairata daga Annabi (SAW) ya ce: “Bu’istu min kairi kuruni bani Adama, karnan fa karnan, hatta kuntu minal karnillazi kuntu fihi – An tashe ni daga fiyayyen zamaninnikan ‘yan Adam, tsara bayan tsara, tun daga zamanin Annabi Adam har na zo cikin wannan zamanin da nake ciki”

An karba daga Abbas bin Abdulmuddalibi ya ce, Annabi (SAW) ya ce “ Innallaha Ta’ala khalakal khalka waja’alani min kairim, min kairi karnihim, summa takhayyaral kaba’ila, faja’alani min khairi kabilihim, summa takhayyaral buyuta, faja’alani min khairi buyutihim, wa’ana khairihim nafsan wa khairuhum baitan – Lallai Allah Ubanagiji Ya halicci halitta sai ya sanya ni mafificinsu, a cikin mafificin tsaransu, sannan ya zabi kabilu, sai ya sanya ni cikin fiyayyar kabila, Sannan Allah Ya zabi Gida, sai ya sanya ni mafi girman gidansu, ni ne mafi girman ‘yan Adam a kan kaina kuma ni ne mafi girmansu gida.“

An karbo daga Wasila dan Asda’i ya ce, Annabi (SAW) Ya ce “ innallahasdafa min waladi Ibrahim Isma’ila, wasdafa min waladi Isma’ila Bani Kinana, wasdafa min Bani Kinanata Kuraishan, wasdafa min Kuraishan Bani Hashim, wasdafani min Bani Hashim – Allah Ya zabi Annabi Ismail daga cikin ‘ya’yan Annabi Ibrahim (AS), Allah Ya zabi Bani Kinana daga cikin ‘ya’yan Annabi Isma’il, Allah ya zabi Kuraishawa daga cikin Bani Kinana, Allah ya zabi Bani Hashimu daga cikin Kuraishawa, sai Allah Ya zabe ni daga cikin Bani Hashim.”

An karbo daga Abdullahi dan Umar (RA) ya ce, Annabi (SAW) ya ce “Allah Ubangiji madaukaki, ya yi zabe a cikin halittunsa, sai ya zabi ‘ya’yan Adam, a cikin ‘yan Adam sai ya zabi Larabawa, a cikin Larabawa, sai ya zabi Kuraishawa, a cikin Kuraishawa sai Ya zabi Bani Hashimu, a cikin Bani Hashim sai ya zabe ni, ban gushe ba ina abin zabi daga cikin zababbu. Kowa ya sani! duk wanda ya so Larabawa, don yana so na ne yaso su, duk wanda ya ki Larabawa, don yana ki na ne ya ki su.

An karba daga Abdullahi dan Abbas yana cewa ”Ruhin Annabi ta kasance haske ce tana gaban Allah tun kafin ya halicci Annabi Adam da Shekaru 2000 (na kirgen Ubangiji), wannan hasken bai gushe ba yana Tasbihi, Mala’iku ma suna Tasbihi da Tasbihinsa, yayin da Allah Ya Halicci Annabi Adam, sai Allah ya sanya wannan Hasken a tsatson Adamu, sai Allah ya saukar da ni kasa a tsatson Adamu (AS), ya sanya ni a tsatson Annabi Nuhu (AS), ya jefa ni a tsatson Annabi Ibrahim (AS), sannan Allah bai gusheba yana ciro ni daga tsatson masu girma (Maza) da mahaifa (Mata) har ya fitar da ni daga Uwata da Ubana, babu wani ko wata da na biyo ta tsatsonta da suka taba zubar da ruwan banza (lalata ko kuma a ce ain masha’a).

‘Yan uwa masu karatu, hakika girman Annabi (SAW) a wurin Allah ba zai misaltu ba, kamar dai yadda muka rika kawowa cikin darussan da muka gabatar a wannan shafi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: DaukakaManzon Allah Sallallahu alaihi WasallamaNasaba
ShareTweetSendShare
Previous Post

NSCDC Ta Cafke Hatsabibin Ɗan Bindiga A Kano

Next Post

Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 

Related

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (3)

16 hours ago
Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)
Dausayin Musulunci

Yadda Manzon Allah (SAW) Ya Yi Aikin Hajji (1)

2 weeks ago
Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci
Dausayin Musulunci

Abubuwan Da Aka Haramta Wa Mahajjaci

3 weeks ago
Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa
Dausayin Musulunci

Shimfida A Kan Aikin Hajji Da Bayani A Kan Mikatin Da Manzon Allah (SAW) Ya Sa

1 month ago
Ramadan
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (4)

1 month ago
Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni
Dausayin Musulunci

Darussa Daga Tafsirin Ramadan Daga Masu Bibiya (3): Shari’ar Manzon Allah (SAW) Ta Zo Da Wayewa A Kowane Fanni

2 months ago
Next Post
Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 

Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

June 6, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Halarci Taron Ministocin Kula Da Matakan Taron FOCAC Da Bikin Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayyar Sin Da Afirka Karo Na 4

June 6, 2025
An Kama Wadanda Ake Zargi Da Kai Wa Shugaban Kwadago Hari Ribadu

Ribadu Ya Kara Jaddada Gargadinsa Kan Biyan Kudin Fansa Ga Masu Garkuwa Da Mutane

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

Kasar Sin Ta Harba Sabon Rukunin Taurarin Dan Adam Mai Samar Da Sadarwar Intanet

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.