ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Daukakar Nasaba Da Girman Garinsa (SAW)

by Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
2 years ago
Nasaba

Suna daga cikin abin da ba a bukatar a kafa dalili a kansu, in dai kai musulmi ne ba ka bukatar sai an gaya maka daukakar danginsa da girman garinsa da girman inda ya taso, ko ka ce akwai wani bayani mai rikitarwa da sai an maka bayaninsu, ko akwai wani abu boyayye a ciki, shi Annabi (SAW) zababben Bani Hashim ne, ta bangaren kyau, iya magana, Ilimi da dukkan alheri, haka aka san ‘ya’yan Hashimu da wadannan kyawawan halitta.

Ya ishe mu alfahari cewa duk kyawun Abdulmuddalibi, shi ne shugaban Bani Hashim amma gashi yana wa Annabi waka yana cewa “Wa Ab’yadu yustaskal gamamu bi wajhihi, simalul yatama ismatun lil aramili – fari ne wanda da albarkar fuskarsa ake shayar da girgije, Uban marasa Uba kuma mijin mata gwagware.

  • Hikimomin Kalaman Manzon Allah (SAW)
  • Fasaha Da Balagar Harshen Manzon Allah (SAW) II

“Takdi bihin nakatul ajma’u mu’utajiran bil burdikal badri jalla lailataz zulami – rakumi yanayin taku daidai da shi, ya lulluba da bargo kai ka ce wata ne da ya bayyana a cikin dare mai duhu.

ADVERTISEMENT

“Yaluzu bihil hullaku min ali Hashimin, wahum indahum fi ni’imatin wa fawadili – Halakakkun Bani Hashim da shi suke fakewa, kuma shi (Annabi SAW) mai ni’ima ne da babbar daraja a wajensu”

Shi ne zababben Bani Hashim, haifaffen Bani Hashim, shi ne mafi daukakan Larabawa kuma mafi buwayarsu ta dukkan bangare na Mahaifinsa da bangaren mahaifiyarsa duk babu kamarsa sannan kuma dan garin Makkah ne wacce ita ce mafi girman garuruwan Allah da wajen bayin Allah.

LABARAI MASU NASABA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

Alkalin Alkalai ya yi mana Hadisi, Hussaini bin Muhammadus Sadafiyyu (Allah Ya rahamshe shi) ya ruwaito Hadisi inda ya daga Salsalar hadisin har zuwa Abu Hurairata daga Annabi (SAW) ya ce: “Bu’istu min kairi kuruni bani Adama, karnan fa karnan, hatta kuntu minal karnillazi kuntu fihi – An tashe ni daga fiyayyen zamaninnikan ‘yan Adam, tsara bayan tsara, tun daga zamanin Annabi Adam har na zo cikin wannan zamanin da nake ciki”

An karba daga Abbas bin Abdulmuddalibi ya ce, Annabi (SAW) ya ce “ Innallaha Ta’ala khalakal khalka waja’alani min kairim, min kairi karnihim, summa takhayyaral kaba’ila, faja’alani min khairi kabilihim, summa takhayyaral buyuta, faja’alani min khairi buyutihim, wa’ana khairihim nafsan wa khairuhum baitan – Lallai Allah Ubanagiji Ya halicci halitta sai ya sanya ni mafificinsu, a cikin mafificin tsaransu, sannan ya zabi kabilu, sai ya sanya ni cikin fiyayyar kabila, Sannan Allah Ya zabi Gida, sai ya sanya ni mafi girman gidansu, ni ne mafi girman ‘yan Adam a kan kaina kuma ni ne mafi girmansu gida.“

An karbo daga Wasila dan Asda’i ya ce, Annabi (SAW) Ya ce “ innallahasdafa min waladi Ibrahim Isma’ila, wasdafa min waladi Isma’ila Bani Kinana, wasdafa min Bani Kinanata Kuraishan, wasdafa min Kuraishan Bani Hashim, wasdafani min Bani Hashim – Allah Ya zabi Annabi Ismail daga cikin ‘ya’yan Annabi Ibrahim (AS), Allah Ya zabi Bani Kinana daga cikin ‘ya’yan Annabi Isma’il, Allah ya zabi Kuraishawa daga cikin Bani Kinana, Allah ya zabi Bani Hashimu daga cikin Kuraishawa, sai Allah Ya zabe ni daga cikin Bani Hashim.”

An karbo daga Abdullahi dan Umar (RA) ya ce, Annabi (SAW) ya ce “Allah Ubangiji madaukaki, ya yi zabe a cikin halittunsa, sai ya zabi ‘ya’yan Adam, a cikin ‘yan Adam sai ya zabi Larabawa, a cikin Larabawa, sai ya zabi Kuraishawa, a cikin Kuraishawa sai Ya zabi Bani Hashimu, a cikin Bani Hashim sai ya zabe ni, ban gushe ba ina abin zabi daga cikin zababbu. Kowa ya sani! duk wanda ya so Larabawa, don yana so na ne yaso su, duk wanda ya ki Larabawa, don yana ki na ne ya ki su.

An karba daga Abdullahi dan Abbas yana cewa ”Ruhin Annabi ta kasance haske ce tana gaban Allah tun kafin ya halicci Annabi Adam da Shekaru 2000 (na kirgen Ubangiji), wannan hasken bai gushe ba yana Tasbihi, Mala’iku ma suna Tasbihi da Tasbihinsa, yayin da Allah Ya Halicci Annabi Adam, sai Allah ya sanya wannan Hasken a tsatson Adamu, sai Allah ya saukar da ni kasa a tsatson Adamu (AS), ya sanya ni a tsatson Annabi Nuhu (AS), ya jefa ni a tsatson Annabi Ibrahim (AS), sannan Allah bai gusheba yana ciro ni daga tsatson masu girma (Maza) da mahaifa (Mata) har ya fitar da ni daga Uwata da Ubana, babu wani ko wata da na biyo ta tsatsonta da suka taba zubar da ruwan banza (lalata ko kuma a ce ain masha’a).

‘Yan uwa masu karatu, hakika girman Annabi (SAW) a wurin Allah ba zai misaltu ba, kamar dai yadda muka rika kawowa cikin darussan da muka gabatar a wannan shafi.

Nasaba
Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
+ postsBio
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci
  • Shehu Ismaila Umar Mai Diwani
    https://hausa.leadership.ng/author/shehu-ismaila-umar-mai-diwani/
    Albishir Ga Iyayen Da Suka Karantar Da ‘Ya’yansu Alkur’ani (2)

MASU ALAKA

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW
Dausayin Musulunci

Buƙatar Yawaita Salati Ga Annabi Muhammad SAW

May 29, 2026
Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari
Dausayin Musulunci

Buƙatar Komawa Ga Allah Ta Hanyar Yawaita Istigfari

May 22, 2026
Nasaba
Dausayin Musulunci

Bukatar Kula Da Tarihi A Musulunci

May 15, 2026
Next Post
Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 

Minista Ya Buƙaci Masu Amfani Da Manhajojin Sada Zumunta Su Riƙa Ƙimanta Nijeriya 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.