• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

by Idris Aliyu Daudawa
2 hours ago
in Manyan Labarai
0
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A garin Nyanya, da yake ƙarƙashin Babban Birnin Tarayya Abuja, matar aure, Hauwa Moji, ita ma ta bada labarin irin yadda suke fuskantar lamarin. Ta bayyana cewa ‘ya’yanta b za su ci gaba da karatu ba a wannan zangon ba, domin komai ba sai saboda an ƙara kuɗin haya da kuma na makaranta, tace irin wannan lamarin da zai laƙume kuɗaɗe masu yawa mijinta ba zai iya ɗaukar nauyin abubuwan ba a lokaci ɗaya.

Ta ce, “Matsalar ta fara ne bayan da minjinta ya rasa aikin koyarwa da yake yi ya fara neman wani. Cikin ikon Allah sai ya samu wani amma kafin a daga hutu. Wani abin takaici dole ne ya fita daga gidan da aka ba shi makarantar da ya ajiye aiki, hakan ya nuna dole ne ya nemi wani wurin zama.

“Ta ci gaba da bayanin mijina daga ƙarshe ya samu wuri a Nyanya. Maigidan yace zai biya Naira 400, 000, amma saboda baya kusa, sai mai bada hayar ya ce, bayan ya amshi wasu ƙarin kuɗi, sai ya tsaya kai da fata cewa dole ne sai ya biya Naira 700, 000 a shekara ta farko saboda akwai kuɗin da ake ba mai bada haya, kuɗin Lauya, da kuma sauran wasu kuɗaɗe daban, daga nan kuma shekara mai zuwa sai ya biya, Naira 400,000 .

  • Hukumar SUBEB Ta Yi Kira Ga Al’umma Da Su Sa ‘Ya’yansu Makaranta
  • ‘Yan Makaranta Sun Kera Mota Mai Amfani Da Lantarki A Sakkwato

“Bai da zaɓi dole ya haɗa ya biya da kuɗaɗen da yara ya kamata a biya ma su kuɗin makaranta, maimakon haka sai ya biya kuɗinhaya suka shiga cikin gidan. Ta ci gaba da ƙarin bayani.Bamu da abinda ya dace mu yi wanda fi wanda muka yi, amma ba maganar fara karatun yara ba a wannan zangon, sai kuma lokacin da abubuwa suka fara gyaruwa su ci gaba da karatu.

Ita kuma Gloria Oche, da take da ‘ya’ya uku ya bayyanawa LEADERSHIP cewa ‘yar’uwarta tana tunanin ko za ta ɗauki mataki da ta san zai fishshe ta.

Labarai Masu Nasaba

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

Kamar yadda Oche, wadda ‘ya’yan ‘yar’uwarta suke zuwa makarantar Reno ta Oluwami da Firmare , da take Abuja inda shekarun baya suke biyan wajen Naira 600,000 ko wane zangon karatu, saboda wasu haraje- harajen da aka haɗa da su ciki.

“Maganar gaskiya kowace shekara idan za’a shiga sabon zangon karatu, makarantu su kan ƙara kuɗin makaranta, su ƙara wasu sabbin abubuwa, kamar su kuɗin ICT, wasanni tsaro. Sai dai ƙarin da akwai matuƙar matsala.”

A makarantar( Prime School ) da ke, Karu,inda aka ƙiyasta ana biyan kusan Naira 300, 000, kowane zangon karatu,wani Malamin da baya son a ambaci sunansa ya ce, akwai ƙarin kuɗin makaranta waɗanda suna da alaƙa ne da lamarin daya shafi kayn zuwa makaranta, bunƙasar makaranta, da kuma sauran abubuwa.

“Idan aka dukkan ƙarurrukan da aka yi abin zai zama da akwai ɗaure kai. Kuɗin haya ya ƙaru a wannan unguwa idan kuma mutum ya yi bincike kuma za a gane irin mutanen da suke zama a wurin, waɗanda abinda suke samu ba kasafai yake biya masu buƙata ba. Don haka idan har ka sa ɗanka wannan makaranta,duk da yake dai z aka, iya biya,amma idan wani babban abu ya taso kamar kiuɗin haya abin sai dai ayi shiru kamar yadda ya ce,”.

Wani mahaifi, Joseph Hange wanda ‘yarsa take zuwa makarantar Bright Child Academy, Lugbe, cewa ya yi sabuwar shekarar karatun ta zo da abubuwa masu sosai zuciya.

“Abin bai tsaya kan maganar ƙare-ƙaren kuɗaɗen bane kawai na kuɗin makaranta, abinci, Littattafai, suturar zuwa makaranta, ziyarar buɗe ido, duk a haɗa su wuri ɗaya. Kamar su da suke harkar kasuwanci, lamarin tattalin arzikin ba shi da daɗi.Cewa ya yi sun tattauna a gida ko daga ƙarshe irin wannan tafiyar za ta ɗore”.

Yayin da Iyaye lamarin ya hana su kwanciyar hankali,su ma Malaman makarantar kamar duk jirgi ɗaya ya ɗauko su.Domin kuwa yawancin makarantu yawan ƙarin kuɗin makaranta bai kai wag a ƙarin albashi ga su Malaman makarantar.

Wani Malami mai suna Moses Sachi a Abuja shi ma abin ya dame shi, saboda kuwa cewa yayi “Muna dai jin Iyaye suna kokawa, amma mu ma a matsayinmu na Malamai, matsalar da take damun Iyayen yaran muma ita ce ke damun mu .Lamarin kuɗin haya, abinci, da zirga- zirga abin yana ci mana tuwo a ƙwarya.

Wasu daga cikinmu akwai ayyukan da muke yi domin a samu tsira da mutunci kamar, zuwa koyar da darussa a gida, ƙananan sana’oi, kawai saboda dai mu samu kulawa da Iyali . Wasu makarantu sun ɗan yi ƙarin albashi wanda bai maganin matsin tattalin arzikin da kowa yake fuskanta ba, bama kamar talaka kamar yadda ya jaddada” .

Binciken da LEADERSHIP ta yi rahoton ya nuna matslar ba kawai ta ƙare bane kan ƙarin kuɗin makaranta ba.Kuɗaɗen haya sun ƙaru a sassa daban daban kamar su Abuja, Legas, da kuma wasu manyan wurare kamar Karu, Lugbe, da Gwarimpa da sauarn sassan Babban Birnin Tarayya Abuja, masu gidaje sun ƙara kuɗin haya da kashi 30 kamar yadda binciken ya nuna

Shi yasa Iyayen da suke biyan kuɗin makaranta dubban Nairori yanzu dole ne su san irin hanyar da za su bi, domin su nemi ƙarin kuɗin da za su cika domin biyan haya.

Wani mahaifi a Nyanya, mai suna Isaac Terseer, ya yi lamarin kallon abinda zai yi wuyar jurewa:

Inda ya ce “Wannan tamkar mutum ya riƙa bin inuwa ne da ƙoƙarin kamata.An ƙara kuɗin makaranta, kuɗin haya sun ƙaru.

Wannan halin ƙuncin rayuwa tana sa mutane ko iyalai su cikin halin ni’yasu kan yadda za su yanke shawarar daga cikin abubuwan da suka kamata su yi su ɗauki ɗaya da suke ma kallpon ya fi muhimmanci. Wasu na canza wa ‘ya’yansu makaranta zuwa wadda kuɗin da za su iya biya.Wasu suna tunanin yanke shawarar a riƙa koya masu a gida, ko kuma maida su makarantun gwamnati duk kuwa da yake akwai matsalar kayan aiki da, da rashin nagartar koyarwar.

An samu bayanan da suke nuna Iyaye na biyan tsakanin Naira milyan 3 zuwa 5 kowane zangon karatu.

Ta ɓangaren tsaka- tsaki ana biyan Naiar 800,000 zuwa milyan 2.5 kowane zangon karatu.

Waɗanda ake ma kallon masu sassauci ne a Abuja ana biyan Naira 120,000 zuwa 200, 000 a kowane zangon karatu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: HutuKudiMakaranta
ShareTweetSendShare
Previous Post

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

Next Post

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

Related

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

25 minutes ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

3 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

7 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

15 hours ago
An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta
Manyan Labarai

An Tsinci Gawar Ɗalibar Jami’ar Taraba A Ɗakin Saurayinta

20 hours ago
Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Ƙasurgumin Ɗan Ta’adda A Kogi

24 hours ago
Next Post
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

'Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

LABARAI MASU NASABA

Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

September 14, 2025
Likitoci

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

September 14, 2025
APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

APC Na Ƙoƙarin Tarwatsa Mu Ne Saboda Kar Mu Ƙwaci Mulki A 2027 – ADC

September 14, 2025
An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

An Cafke Bature Ɗan Shekara 37 Kan Mutuwar Ɗan Nijeriya Mazaunin Birtaniya

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

September 14, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

DAPPMAN Ta Soki Matatar Dangote Kan Rage Farashin Man Fetur

September 13, 2025
Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

Yadda Wani Ya Kashe Ƙaninsa, Ya Ɓoye Gawar A Duro

September 13, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.