Kevin de Bruyne ya kammala komawa Napoli bayan da dan wasan tsakiyar Belgium din ya bar Manchester City inda ya buga wasanni 422 ya kuma zura kwallaye 108 a karshen kakar wasar bana. De Bruyne zai hadu da tsohon kocin Chelsea da Tottenham Antonio Conte, wanda shi ne kocin zakarun na kasar Italiya a halin yanzu.
Napoli ta sanar da sanya hannun dan wasan mai shekaru 33 a shafukanta na sada zumunta inda ta yi wani rubutu a sama dake nuna ” Sarki Kev” ya zo, Kevin ya bar Manchester City bayan ya shafe shekaru 10 a kulob din, inda ya lashe manyan kofuna 19 bayan da ya zo daga Wolfsburg a shekara ta 2015.
- An Bude Baje Kolin Tattalin Arziki Da Cinikayya Na Sin Da Afirka A Changsha
- Ba Zan Bar Nijeriya Ta Zama Kasa Mai Jam’iyya Daya Ba – Tinubu
De Bruyne ya taimaka wa City ta lashe kofunan Firimiya shida, Kofin League biyar da Kofin FA guda biyu, sai kofin gasar zakarun Turai na farko da kungiyar ta taba lashewa a shekarar 2023, sai kuma kofunan Firimiya uku a jere yayin da kungiyar Pep Guardiola ta zama kungiya ta biyu daga kasar Ingila da ta taba samun wannan nasarar.
An sanar da tashin shi daga City kafin karshen kakar wasa ta bana, kuma De Bruyne ya yi bankwana da magoya baya a filin wasa na Etihad bayan wasansa na karshe a gida da suka buga da Bournemouth a watan Mayu, City ta yi kokarin cike gibin da De Bruyne ya bari, yayinda ta dauki yan wasan tsakiya Tijjani Reijnders daga AC Milan da Rayan Cherki daga Lyon.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp